Aminiya:
2025-10-24@13:45:54 GMT

An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai

Published: 24th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan jihar Yobe ta ce ta cafke wani shugaban mazaba na jam’iyyar APC a karamar hukumar Karasuwa bisa zarginsa da hannu a kisan wata mata.

Rundunar ta ce ta samu nasarar ce a binciken da take yi kan wata gawar da aka gano a kusa da Jami’ar Tarayya da ke Gashuwa a makon da ya gabata.

Gwamnan Neja ya ba dukkan iyalan wadanda suka kone a gobarar tankar mai N1m Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027

A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ’yan sanda daga sashin karamar hukumar Bade sun kama wani mutum mai suna Abdulmumini Garba, mai shekaru 60, dangane da mutuwar matar mai suna Falmata Abubakar, ‘yar shekara 45 da haihuwa.

Rahoton ya nuna cewa wanda ake zargin mazaunin Gasma ne a karamar hukumar Karasuwa, kuma yana rike da mukamai biyu: Sakataren APC na Mazava a Karasuwa da Sakataren Kasuwar Gwari a Gashuwa.

‘Yan sanda sun ce an kama Garba ne bayan gudanar da bincike mai zurfi da kuma kokarin leƙen asiri da suka yi a ranar 17 ga watan Oktoba, 2025.

Lokacin da ake masa tambayoyi, Garba ya amsa cewa shi ne ya kashe Falmata Abubakar a cikin motarsa, bayan samun sabani tsakaninsu.

An bayyana cewa rikicin ya samo asali ne daga bukatar marigayiyar na neman taimakon kuɗi don tallafa wa sana’arta, wanda ya rikide zuwa tashin hankali da ya haifar da mutuwarta.

Bayan mutuwar, wanda ake zargin ya ce ya jefar da gawar a daji da ke kusa da wajen da misalin ƙarfe 10 na dare, inda daga bisani aka gano gawar.

Rundunar ’yan sanda ta bayyana wannan ci gaba a matsayin shaida ta ƙwazo da dabarun tattara bayanai da suka taimaka wajen gano wanda ake zargi cikin gaggawa.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya jinjina wa jami’an sashin Bade bisa ƙwarewa da jajircewarsu, tare da jaddada aniyar rundunar na ganin an samu adalci.

CP Ado ya tabbatar wa da jama’a cewa za a kammala bincike cikin tsanaki, sannan a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala binciken.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sayyed al-Houthi: Mun shirya dawowa fagen daga idan Isra’ila ta ci gaba da kisan kiyashi a Gaza

A cikin jawabin da ya gabatar a wannan Talata da aka nuna kai tsaye a taron jana’izar  babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Yemen  Laftanar Janar Mohammed al-Ghamari, Sayyed Abdulmalik al-Houthi ya jaddada cewa, kasar Yemen za ta ci gaba da kasancewa cikin shirin komowa ga ayyukan soji idan Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta koma kisan kare dangi, da kuma ci gaba da killace yankin zirin Gaza.

Sayyed al-Houthi ya yi ishara da irin babban gangami na dubban daruruwan mutane da suka taru a wurin jana’izar shahid al-Ghamari a matsayin abin da ke nuni da tsayin daka na al’ummar Yemen a kan manufofinsu.

Sayyed al-Houthi ya kuma yi nuni da cewa al’ummar Yemen sun gamsu da matsayi mai Daraja da suke a kansa, na yin sadaukarwa domin taimakon ‘yan uwansu musulmi da ake zalunta a Gaza, inda ya bayyana arangamar da  Yemen ta yi da yahudawan sahyuniya a cikin shekaru biyu da cewa sadaukarwa saboda Allah da kuma ‘yan adamtaka, da kuma kin mika wuya ga zaluncin masu grman kai na duniya.

Ya ce wadanda suka mika wuya ga mnufofin yahudawa a yankin, ba su daukar komai face kaskanci da kunya a idon duniya, sabanin matsayar al’ummar Yemen da sauran bangarori masu gwagwarmaya domin taimakon al’ummar Falastinu a yankin, wadanda suka Fifita rayuwa a cikin karama da ‘yanci, ko da kuwa hakan zai kaisu ga matsayi na shahada a kan tafarkin gaskiya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Nigeria: “Yan Sanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Neman Sakin Jagoran ‘Yan Awaren Biafara October 21, 2025 HKI Tana Ci Gaba Da Hana Wa Falasdinawa Abinci October 21, 2025 An Yi Fashi Da Makami A Gidan Adana Kayan Tarihin  ” Louvre” Na Kasar Faransa October 21, 2025 Yemen : An yi jana’izar babban hafsan sojin kasar Shahid al-Ghamari a Sana’a October 21, 2025 Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza October 21, 2025 Equatorial Guinea ta zargi Faransa da karan-tsaye wa zaman lafiya a kasar October 21, 2025 Faransa : Sarkozy, ya fara zaman gidan yari na shekara 5 October 21, 2025 Gaza : Falasdinawa 97 sojin Isra’ila suka kashe tun bayan cimma yarjejeniya October 21, 2025 Iran Da Faransa Zasu Yi Musayar Fursinoni, Esfandiari Tana Daga Cikin Wacce Za’a Sallama October 21, 2025 Gaza: Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa 57 A Cikin Sa’o’i 24 Da Suka Gabata October 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha ta miƙa wa Ukraine sojoji 1,000 da suka mutu a fagen daga
  • Gwamantin Nijar ta ƙara albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikata
  • DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a Kaduna
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Jihar Zamfara Ta Gargadi Direbobi Game Da Rufe Lambar Mota
  • Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci
  • Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi
  • Sayyed al-Houthi: Mun shirya dawowa fagen daga idan Isra’ila ta ci gaba da kisan kiyashi a Gaza
  • Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi
  • Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi