Aminiya:
2025-12-09@18:57:41 GMT

Gwamnan Neja ya ba dukkan iyalan wadanda suka kone a gobarar tankar mai N1m

Published: 24th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya sanar da bayar da tallafin naira miliyan ɗaya ga duk iyalin da ya rasa ɗan uwa a gobarar tankar man da ta faru a garin Essa, Karamar Hukumar Katcha.

Haka kuma, ya ba da tallafin naira dubu ɗari biyar ga kowanne daga cikin waɗanda suka jikkata a lamarin.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai yankin da abin ya shafa, inda ya tantance tare da ganawa da shugabannin al’umma da mazauna yankin.

Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027 NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas?

Wannan sanarwa ta fito ne daga Sakataren Yada Labarai na Gwamnan, Bologi Ibrahim, a daren Alhamis.

Mummunan hatsarin gobarar tankar man ya faru ne da misalin ƙarfe 3:45 na ranar Talata, lokacin da wuta ta tashi a cikin tankar man fetur din da mutane ke diba daga tankar da ta kife a kan hanyar Bida–Badegi–Agaie.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar, Abdullahi Arah, ya tabbatar da cewa adadin waɗanda suka mutu ya kai 42, yayin da waɗanda suka jikkata suka kai 52.

Arah, wanda ya bayyana hakan a hirarsa da gidan talabijin na Arise, ya danganta faruwar lamarin da lalacewar hanya da kuma zafin rana a yankin, wanda ya taimaka wajen haifar da gobarar.

“Ina jin baƙin ciki matuƙa da faruwar wannan lamari,” in ji Gwamna Bago, yayin da yake addu’ar samun sauƙi ga waɗanda ke jinya a asibitocin Bida da Abuja.

Sai dai ya soki dabi’ar dibar man fetur daga tankar da ta kife, yana mai cewa hakan na da matukar hatsari kuma babban laifi ne.

“Mun zo ne don yin ta’aziyya da su kan asarar rayuka, da kuma tunatar da su muhimmancin kiyaye rayuka.

“Abin takaici ne a ce tankar man ta faɗi, sai mutane su fito da jarakuna suna dibar man. Wannan sata ce, kuma dole ne a dakatar da ita. Ba za mu goyi bayan hakan ba,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma ce fitaccen ɗan kasuwa, Aliko Dangote, ya yi alkawarin gyara hanyar Mokwa–Lambata, kuma aikin zai fara nan ba da jimawa ba.

A ƙarshe, gwamnatin jihar ta bayyana cewa za ta gina cibiyar kula da lafiya ta farko a garin Essa domin biyan buƙatun lafiyar al’ummar yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobarar tankar mai

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166

166-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma, ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtada Muttari, ko kuma cikin littafin Mathnawa na Maulana Jalaluddeen Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin wannan Shirin.

/////….Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan al-Mujtaba da muke kawo maku, mun yi maganar yadda Imam Al-Assan (a) ya jarrabi sojojinsa, don ya san gaskiyar halin da suke ciki. Inda                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                yayi khuduba, sannan a cikin khudubar ya fada masu cewa Mu’awiya dan Abu Sufyan ya bijiro masa wani al-amari wanda babu izza a cikinsa, idan suna sun rayuwa basa son mutuwa zai amince da bukatar amma idan sun shiryawa mutuwa kuma to zai kai kararsa ga Allah ya bude yaki da shi har zuwa abinda Allah ya hukunta. Amma sai suka ce masa suna son rayuwa.

Daga nan Imam (a) ya kara tabbatar da cewa bai da sojojin da zai yaki Mu’awiya da su, kuma idan har jinkirta sulhu da shi ma zai kara fadawa cikin hatsari ne, da shi da iyalan gidansa da kuma raguwar muminai masu Ikhlasi.

Kafin haka kwamandojinsa da dama sun karbi kudade daga wajen Mu’awiya sun kuma sulale  sun koma bangarensa.

Sannan mun bayyana dalilan da suka sa rundunar Imam Alhassan (a) ta kasa yakar Mu’awiya dan Abusufyan, ko kuma rundunar sham. Daga cikin mun kawo, banbance-bambancen akidu da rundunar take da su, akwai Khawarijawa, akwai shi’ar babansa da kuma wadanda suka san matsayin iyalan gidan manzon Allah (s) a cikin al-ummar Musulmi. Kuma su suna biyayya a gareshi ba tare da sun tambayi dalili ba, amma su kadan ne a cikin Rundunar. Wannan kuma, saboda mafi yawansu sun yi shahada a yake-yaken siffin da Jamal da kuma wasu wurare.

Sannan akwai wadanda kabilanrsu tafi damunsu a kan addininsu. Basa ganin shugaban addini ya fi shugaban kabilarsu, don haka ne sun fi biyayya ga shuwagabaninsu na kabila a kan shugabansu na addini wato Imam  Al-Hassan (a) kuma su suka fi yawa a cikin rundunar tasa.

Sannan mun yi maganar Rashawan da Mu’awiya yake bawa kwamandojin rundunar Imam Al-Hassan(a), da kuma shuwagabannin kabilun larabawan iraki a lokacin. Cin hancin da Mu’awiya ya rabawa kwamandojin rundunar Imam Al-Hassan(a) yana daga cikin manya-manyan al-amuran da suka rusa rundunar Imam (a).

Wannan kuma saboda mafi yawansu masoya duniya ne, kuma basu san Allah kuma basa tsoronsa. Su karbi kudade daga wajen Mu’awiya su rusa addinin musulunci karkashin jagorancin hujjan Allah a bayan kasa.

Sun saida gaskiya sun goyi bayan karya don dan dirhamomi da mu’awiya ya basu. Basa tsoron haduwarsa da Allah. Basa jin kunyarsa hatta, basa jin kungiyar abinda al-ummun da zasu zo nan gaba zasu fada masu.

Abinda ya tabbata dangane da rundunar Imam Al-Hassan (s) shi ne, mafi yawansu basa da manufa mai kyau a fitowarsu tare da shi. Wasu daga cikinsu sun bayyana manufofinsu a wasu yake-yake a baya suna cewa (Wanda ya bamu dirhami zamu yi yaki tare da shi).

Sannan wani yana aibata wani da aka kashe a wani yaki daga cikin yake-yake a baya yana fadawa ‘ya’yansa

(Ba a tafarkin Allah ne babanku ya hadu da mutuwa ba, said ai don, sai sai saboda dirhamomi). Wannan kamar yadda ya zo a cikin littafin Tarikhin Al-Umamu wal-Muluk JZ 5 SH 10.

Don haka idan runduna tana yaki ne da wasu manufofi na duniya, wannan hatsari ne ga daular ga kuma shugaban daular daga cikin gida. Kuma mai irin wannan tunanin yana iya juyawa shugabansa a duk lokacinda yaga dama. Kuma idan makiya sun hadu da shi suna iya cutar da daular ko shugaban da shi.

Lalacewar Irakawa a lokacin ya kai ga a lokacinda Imam Al-Hassan (a) ya sauka gidan gidan Sa’ad dan Mas’ud Athaqafi, wanda ya kasance walin Imam Amirulmumina (a) a Mada’in sai Imam Al-Hassan ta tabbatar da shi. Imam ya sauka gidansa yana jinyar raunin da aka ji masa a cinyarsa. Sai dan dan’uwansa Mukhtar ya shigo wajensa, ance a lokacin yaro ne, sai ya fadawa amminsa Sa’adu dan Mas’ud, shin kana son wadata da daukaka ne?

Sai y ace, ina jinka.

Sai ya ce ka kama Hassan ka sami amici da shi daga Mu’awiya. Sai Amminsa ya zabura saboda maganarsa yana cewa: Tsinuwar Allah ya tabba a kanka. In kama dan diyar manzon Allah (s) don neman amincin ? amma al-amarinka ya munan.

Wannan ba ra’ayin dan Mukhtar ne kawai ba, da dama daga cikin sojojin Imam Al-Hassan (a) suna rigengento wajen neman abin duniya ta duk inda ya zo masu. Kuma ba cikin sojojin Imam Al-Hassan kadai ba, tun zamanin Amirulmuminina Aliyu dan Abitalib haka suke. Kamar yadda Imam Aliyu zainul Abidina yake fada. Lalle Mu’awiya yana yakar Aliyu da zinarinsa). Yana nufin sojojinsa).

Mu’awiya ya gane inda raunin sojojin Imam Al-Hassan yake, sai yayi ta tunkuda masu rashawa su ka amsa masa, suka sulale suka koma wajensa suka bar zurriyar manzon Allah (s) wadanda ya barwa al-umma a bayansa su kadai.

Sai kuma yada karya a cikin rundunar Imam Al-Hassan (a). Yada labaran karya a cikin rundunar Imam Al-Hassan ya taka rawa mai yawa, a cikin rusa rundunar. Karyayyakin da ma’aikatan mu’awiya suka yada a cikin mayakan Imam Al-Hassan suna da yawa. Daga cikin sun yada cewa Kais dan Sa’ad dan Ubada ya sulhunta da mu’awiya ko kuma an kashe shi. Sannan sun yada labarin cewa mu’awiya yana musayar wasiku da Imam Al-Hassan (a) dangane da sulhuntawa.

Sannan sojojin Imam Al-Hassan (a) sun amince sun yarda da wadan nan labaran karya ba tare da tabbatar da gaskiyansu ba, sannan labaran sun samar da baraka a rarraban kai a tsakaninsu. Labaran sun Sanya tsoro da damuwa a cikin zukatansu. Da haka kuma suka tarwatse suka yi Rauni, har shaitan ya sami damar shiga cikin zukatansu yayi masu waswasi.

Karya mafi girma wanda mu’awiya da mutanensa suka yi itace, wacce tawagar da Mu’awiya ya aika zuwa wajen Imam Al-Hassan (a) da sunan sulhuntawa da shi, bayan fitowarta daga wajensa, na cewa wai Imam ya Amice da sulhuntawa da Muawiya.

A lokacinda suka ji wannan karyar ba tare da sunji daga wajensa ba. Sai suka yo kansa suka yi wawason kayakinsa, wasu suna kafirta shi.

Sannan abin mamakin da ya faru a lokacin, shi ne shuwagabannin kabilun larabawan Iraki a lokacin suna kallon wadan nan mutanensu suna wulakanta Imam Al-Hassan(a) amma basu tashi sun hanasu ba. Sun ci gaba da zama a cikin masaukansu ana kawo masu labarin abinda yake faruwa.

Wannan halin ya ci gaba har zuwa lokacinda Imam Al-Hassan (a) ya ga cewa baya cikin amince a cikin wadannan mutanen, sai ya ce a kira masa wadanda ya amince da su don su kare shi da sauran iyalan gidansa.

Wadan nan sune dalilan da suka sa rundunar Imam Al-Hassan (a) ta rushe. Kuma ta rushe da daularsa saboda sojoji sune karfin ko wace daula, idan har shugaban baida sojojin da zasu kareshi su kuma yi masa biyayya to ta yaya zai yaki makiyansa?

Sai kuma abu na biyu, daga cikin dalilan da suka tilastawa Imam Al-Hassan Sulhuntawa. Kuma shine karfin soje na abokin gabansa Mu’awiya dan Abusufyan. Karfin sojojin Mu’awiya ne yasa ya sami damar yakar Amirulmuminina Aliyu dan Abitalib (a) a siffin, duk da cewa an sami nasara a kansa in ba don yaudarar da suka yin a daga mushafi ba. Har’ila yau tare da sojojin nasa ne ya tilastawa Imam Al-Hassan sulhuntawa da shi daga baya.

Da farko mu’awiya ya fahinci abinda mutanensa suke so ya kuma basu, don haka sai suka so shi, shi ma ya so su, don haka ne suke masa biyayya kan dukkan abinda ya umurcesu, kuma suke yarda da duk abinda ya fada masu.

Tare da hakan ne cusa masu a cikin kwakwalensu kan cewa, Banu umayya sune Magadan manzon Allah (s), bayan khalifofi uku na farko.

Don haka ne malaman tarihi suka kawo kan cewa, a lokacinda aka yiwa sarki Abul Abbas Assaffah, sarki na farko daga cikin sarakunan Abbasiyawa, a lokacinda ya kwace iko da kasar Sham aka kuma kawo karshen daular Banu Umayyah, sai shuwagabannin kabilu da kungoyi a sham sun zo wajensa, suna rantse masa da Allah kan cewa su basu taba sanin cewa manzon Allah (s) yana da zurria ko kuma makusanta wadanda zasu gajeshi ba in banda banu umayyah. Don haka aka fada masu, don haka basu san haka ba, sai da Abbasiyawa suka kwace iko. 

Hakan kuma ya faru ne saboda hadisan karya da aka kirkirosu aka kuma yada kan cewa banu umayya sune Magadan manzon Allah (s) sune mafi kusa da shi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri December 7, 2025 Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Ya Yi Wani  Hatsari a Neja