Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana
Published: 22nd, October 2025 GMT
Ma’aikatar al’adu da yawon bude ido ta kasar Sin ta fitar da alkaluman kasuwar yawon shakatawa ta kasar tsakanin watan Janairu zuwa na Satumban bana. Kuma sakamakon binciken kididdigar da aka yi ya nuna cewa, daga watan Janairu zuwa na Satumban bana, adadin yawon shakatawa da mutanen kasar Sin suka yi a cikin gida, ya zarce biliyan 4.
Haka kuma, jimillar kudaden da mutanen kasar Sin suka kashe a harkokin yawon shakatawa ya kai kudin kasar Yuan tiriliyan 4.85, adadin da ya karu da tiriliyan 0.5 bisa na makamancin lokacin a bara, wanda ya kai kaso 11.5 bisa dari. Daga cikinsu, akwai tiriliyan 4.05 da mazauna birane da garuruwa suka kashe, adadin da ya karu da kaso 9.3 bisa dari. Sai kuma tiriliyan 0.8 da mazauna yankunan karkara suka kashe, adadin da ya karu da kaso 24 bisa dari. (Murtala Zhang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: adadin da ya karu da kaso
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi
Tsohon Shugaban Hukumar Kaɓar Koke-koke da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama shi.
Ya ce an kama shi ne saboda jagorantar shari’ar almundahanar biliyoyin Naira na Dala Inland Dry Port, wadda ta shafi tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da iyalinsa.
Jirgin sojin sama ya yi hatsari a Neja Nakiya ta hallaka yara 4 a BornoMuhuyi, ya shaida wa DCL Hausa cewa an tafi da shi Abuja cikin dare.
“Da aka kama ni, suka sanya jami’ai biyu ɗauke da bindiga a gefena, sai wasu uku a gaba. Haka muka tafi daga Kano zuwa Abuja cikin dare,” in ji shi.
Ya ce ’yan sandan sun ƙi nuna masa takardar izinin kama shi har sai da suka isa Abuja.
“Da muka isa, suka gabatar min da sabbi tuhume-tuhume na ɓatanci da kutse.
“A ina ne wanda ake zargi zai ki kare kansa ya kuma umarci ’yan sanda su kama babban lauya mai shigar da ƙara?” ya tambaya.
An bayar da belinsa, amma an umarce shi da ya koma Abuja a ranar Laraba tare da miƙa fasfo d5insa.
Ganduje da ’ya’yansa na fuskantar shari’a kan zargin canja mallakar kaso 20 a aikin Dala Inland Dry Port ba bisa ƙa’ida ba.