Ma’aikatar al’adu da yawon bude ido ta kasar Sin ta fitar da alkaluman kasuwar yawon shakatawa ta kasar tsakanin watan Janairu zuwa na Satumban bana. Kuma sakamakon binciken kididdigar da aka yi ya nuna cewa, daga watan Janairu zuwa na Satumban bana, adadin yawon shakatawa da mutanen kasar Sin suka yi a cikin gida, ya zarce biliyan 4.

998, adadin da ya karu da miliyan 761 bisa na makamancin lokacin a bara, karuwar ma ta kai kaso 18 bisa dari. Daga ciki, adadin yawon shakatawa da mazauna birane da garuruwa suka yi ya kai biliyan 3.789, adadin da ya karu da kaso 15.9 bisa dari. Sai kuma adadin yawon shakatawa da mazauna yankunan karkara suka yi ya kai biliyan 1.209, adadin da ya karu da kaso 25 bisa dari.

 

Haka kuma, jimillar kudaden da mutanen kasar Sin suka kashe a harkokin yawon shakatawa ya kai kudin kasar Yuan tiriliyan 4.85, adadin da ya karu da tiriliyan 0.5 bisa na makamancin lokacin a bara, wanda ya kai kaso 11.5 bisa dari. Daga cikinsu, akwai tiriliyan 4.05 da mazauna birane da garuruwa suka kashe, adadin da ya karu da kaso 9.3 bisa dari. Sai kuma tiriliyan 0.8 da mazauna yankunan karkara suka kashe, adadin da ya karu da kaso 24 bisa dari. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli October 22, 2025 Daga Birnin Sin Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar October 22, 2025 Daga Birnin Sin Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya  October 21, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: adadin da ya karu da kaso

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi

Tsohon Shugaban Hukumar Kaɓar Koke-koke da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama shi.

Ya ce an kama shi ne saboda jagorantar shari’ar almundahanar biliyoyin Naira na Dala Inland Dry Port, wadda ta shafi tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da iyalinsa.

Jirgin sojin sama ya yi hatsari a Neja Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno

Muhuyi, ya shaida wa DCL Hausa cewa an tafi da shi Abuja cikin dare.

“Da aka kama ni, suka sanya jami’ai biyu ɗauke da bindiga a gefena, sai wasu uku a gaba. Haka muka tafi daga Kano zuwa Abuja cikin dare,” in ji shi.

Ya ce ’yan sandan sun ƙi nuna masa takardar izinin kama shi har sai da suka isa Abuja.

“Da muka isa, suka gabatar min da sabbi  tuhume-tuhume na ɓatanci da kutse.

“A ina ne wanda ake zargi zai ki kare kansa ya kuma umarci ’yan sanda su kama babban lauya mai shigar da ƙara?” ya tambaya.

An bayar da belinsa, amma an umarce shi da ya koma Abuja a ranar Laraba tare da miƙa fasfo d5insa.

Ganduje da ’ya’yansa na fuskantar shari’a kan zargin canja mallakar kaso 20 a aikin Dala Inland Dry Port ba bisa ƙa’ida ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi
  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15