Uwargidan Shugaban Ƙasa ta Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta kaddamar da Dijital E-Learning Library a Gusau, Jihar Zamfara — ɗaya daga cikin jihohi goma da aka zaɓa a faɗin ƙasar domin aiwatar da wannan muhimmin aiki ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) tare da haɗin gwiwar Hukumar bunkasa ayukkan fasaha ta kasa (NITDA).

A yayin bikin kaddamarwar, Sanata Tinubu ta bayyana cewa wannan aiki ba wai game da fasaha da kwamfuta kawai ba ne, amma yana nufin ƙarfafa matasa, rage gibin fasaha (digital divide), da kuma buɗe sabbin ƙofofin ilimi da ƙirƙira ga al’ummar Zamfara da ma Najeriya baki ɗaya.

Uwargidan Shugaban Ƙasa, wacce Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta wakilta, ta bayyana cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaba a kowace al’umma.

Ta ce, a wannan zamani na dijital, samun kayan koyon zamani ba wata alfarma ba ce, amma wajibi ne domin ci gaban ilimi.

A cewarta, ta hanyar wannan dijital library, dalibai, malamai, masu bincike da ma jama’a gaba ɗaya za su sami damar shiga manyan bayanai, albarkatu da dama na ilmantarwa a sauƙaƙe.

Sanata Tinubu ta bayyana cewa Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) yana da burin tallafa wa ilimi, ƙirƙira da ci gaban zamantakewa, kuma wannan E-Learning Library na ɗaya daga cikin manyan alamu na hangen nesa na shirin.

Ta kuma yaba wa Ma’aikatar Sadarwa, Ƙirƙira da Tattalin Arzikin Dijital da kuma NITDA bisa ƙwarewar su wajen aiwatar da aikin.

A nata jawabin, Uwargidan Gwamnan Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta nuna godiya mai zurfi ga mijinta, Gwamna Dauda Lawal, bisa jajircewarsa wajen inganta harkar ilimi a jihar.

Ta shawarci dalibai, malamai da masu bincike da su amfani da wannan cibiyar ta dijital yadda ya kamata, domin bunƙasa ilimi da gina kyakkyawar makoma ga matasa da ƙarni masu zuwa.

Tun da fari, Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Zamfara, Malam Wadatau Madawaki, wanda Maryam Yahaya, Babban Sakataren Ma’aikatar, ta wakilta, ya yaba wa Sanata Oluremi Tinubu bisa ƙoƙarinta wajen bunƙasa ilimin dijital ta hanyar kafa wannan E-Learning Library ƙarƙashin shirin Renewed Hope Initiative.

Kwamishinan ya bayyana aikin a matsayin babbar nasara wajen bunƙasa ƙirƙira, haɗa kai ta hanyar fasaha da kuma tabbatar da ingantaccen ilimi ga ’yan Zamfara.

Haka kuma, ya yaba wa Uwargidan Gwamna Hajiya Huriyya Dauda Lawal bisa wakiltar Uwargidan Shugaban Ƙasa da kuma irin goyon bayanta da jajircewa wajen cigaban ilimi a jihar.

Madawaki ya ƙara da cewa wannan E-Learning Library na tafiya da hangen nesa na Gwamna Dauda Lawal, wanda tun bayan hawa mulki ya ayyana dokar ta-baci kan ilimi, matakin da ya haifar da gagarumin ci gaba a fannin ilimi a jihar.

Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Uwargidan Shugaban Ƙasa Dauda Lawal

এছাড়াও পড়ুন:

Minista Matawalle ya Karɓi Manyan Jiga-Jigan PDP Da Suka Koma Jam’iyyar APC

Aƙalla shugabanni 15 na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a Jihar Zamfara sun sauya sheka zuwa All Progressives Congress (APC).

 

An gabatar da waɗannan waɗanda suka sauya shekar ne a gaban Ministan Harkokin Tsaro na Ƙasa, Dr. Bello Mohammed Matawalle, a Abuja ranar Laraba, ta hannun Shugaban APC na Jihar Zamfara, Alhaji Tukur Umar Danfulani, tare da Sanata Tijjani Yahaya Kaura da Alhaji Lawal M. Liman.

 

A cewar wata sanarwa da Mai Magana da yawun jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, Yusuf Idris Gusau, ya fitar, Minista Matawalle ya tarbi sabbin ’yan jam’iyyar da farin ciki, inda ya tabbatar musu da daidaito da damar ci gaba da aiki a cikin jam’iyyar.

 

Dr. Matawalle ya bayyana matakin da suka ɗauka na komawa APC a matsayin abin jarumtaka kuma daidai da lokaci, tare da nuna farin ciki kan yadda jam’iyyar ke ƙara samun karɓuwa a Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya.

 

Ya yaba wa shugabannin jam’iyyar a matakin jiha bisa jajircewar su wajen tuntuba da wayar da kan jama’a, wanda ya ce hakan ya ƙarfafa martabar APC a sassan jihar.

 

Da yake gabatar da waɗanda suka sauya sheka, Shugaban APC na Jihar Zamfara, Tukur Umar Danfulani, ya bayyana cewa sabbin ’yan jam’iyyar sun haɗa da manyan shugabanni 15 na PDP a matakin jiha da yankuna, waɗanda suka shiga APC domin shirye-shiryen zaɓen 2027.

 

Ya ce an karɓe su tun da farko ta hannun Sanata Tijjani Yahaya Kaura, a madadin tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Sanata mai wakiltar Zamfara ta Yamma, Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar.

 

 

Daga cikin fitattun waɗanda suka sauya sheka akwai: Isiyaka M. Dabo, Shugaban Matasa na PDP; Nasiru Mohammed Anka, Ma’ajin Yankin Zamfara ta Yamma; Junaidu Magaji Kiyawa, Sakataren Shirye-shirye na PDP na Zamfara ta Arewa; Musa Halilu Faru, Mataimakin Sakataren Shirye-shirye na Zamfara ta Yamma; Alhaji Lawali Aliyu Shinkafi, Sakataren Yanki na Zamfara ta Arewa; da kuma Hajiya Rabi Bakura da Hajiya Amina Duniya, waɗanda duka Ex-Officio ne na PDP a matakin jiha.

 

Sauran sun haɗa da Bashar Mohammed Dogon Kade, tsohon ɗan takarar majalisar jiha ta Kaura Namoda South, da Rilwanu Bello, tsohon ɗan takarar kansila.

 

Shi ma Sanata Tijjani Kaura, ya bayyana wannan sauya sheka a matsayin babban abin farin ciki ga APC, yana mai cewa sabbin mambobin za su ƙara ƙarfafa ginin jam’iyyar da kyautata damar ta a gaban zaɓen 2027.

 

Ita kuwa Hajiya Amina Duniya, wacce ta ce ta shafe shekaru 25 a jam’iyyar PDP, ta yi alkawarin jawo ƙarin magoya baya zuwa APC tare da kira da a tabbatar da adalci da daidaito ga kowa.

 

Taron ya samu halartar manyan jiga-jigan APC da suka haɗa da: Hon. Lawal M. Gabdon Kaura, tsohon shugaban APC; Alhaji Kabiru Balarabe, tsohon Sakataren Gwamnati; Hon. Yazid Shehu Danfulani, Manajan Darakta na NIAC; Barr. Aminu Junaidu, tsohon Kwamishinan Shari’a; Alhaji Sha’ayau Yusuf Talata-Mafara; Hon. Ibrahim Maigandi Danmalikin Gidan Goga, mai ba Minista shawara kan harkokin siyasa; da Malam Yusuf Idris Gusau, Mai Magana da yawun jam’iyyar, da sauransu.

 

Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasa Dubu Ɗaya Za Su Samu Horon Fasahar Zamani A Nasarawa — Remi Tinubu
  • Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudurin Gwamnatinsa Na Ƙara Zuba Jari A Ilimi
  • Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu
  • Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
  • Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
  • Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027
  • Minista Matawalle ya Karɓi Manyan Jiga-Jigan PDP Da Suka Koma Jam’iyyar APC
  • Idan Tinubu ya gaza zai yi wuya a samu shugaban da zai yi nasara — Shehu Sani
  • Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal