Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20
Published: 20th, October 2025 GMT
Morocco ta ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20 a karon farko a tarihin gasar, bayan ta doke Argentina da ci 2 da nema, tawagar da ta fi kowace ƙasa a duniya lashewa a tarihi
Wannan gagarumar nasara ya sa ta zama ƙasar Afirka ta biyu da ta ɗaga wannan kofi bayan Ghana, wadda ta yi nasara a shekarar 2009.
Gwamnonin Kano, Katsina da Jigawa sun ƙulla yarjejeniyar bunƙasa wutar lantarki Kano Pillars ta dakatar da KocintaA yammacin jiya Lahadi ce aka gudanar da wasan ƙarshe a filin wasa na Estadio Nacional Julio Martínez Prádanos da ke birnin Santiago na Chile, gidan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Universidad de Chile da kuma babbar tawagar ƙwallon ƙafar ƙasar.
‘Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafar Morocco ta ‘yan ƙasa da shekaru 20 sun buga wasan ƙarshe cikin natsuwa da ƙarsashi, cike da ƙwarin gwiwa, lamarin da ya ba da gudunmuwa haƙarsu ta cimma ruwa.
Ɗan wasan gaban Morocco, Yassir Zabiri, shi ne gwarzon wannan karo, inda a cikin minti na 12 da fara wasa ya ci ƙwallon farko ta hanyar bugun tazara, sannan daga bisani ya sake jefa ƙwallo ta biyu bayan hutun rabin lokaci.
Tawagar Argentina, wadda ke neman kofi na bakwai a tarihin wannan gasa, sun yi duk mai yiwuwa wajen riƙe ƙwallo a yayin wasan, amma suka gaza fasa bayan Morocco da ke ƙarƙashin jagorancin Youssef Benchaa.
Morocco dai ta taka rawar gani sosai a wannan gasa, inda ta fara doke Spain, Brazil, Koriya ta Kudu da Amurka, sannan a wasan kusa da ƙarshe ta doke Faransa a bugun daga kai sai mai tsaron raga.
Tawagar Morocco ta yi rashin nasara ne kawai a hannun Mexico a matakin rukuni, amma daga nan ta ƙara ƙaimi suka ci gaba da taka rawar gani har suka ɗaga kofin.
Messi ya jajanta wa ‘yan wasan ArgentinaTauraron ƙwallon ƙafa, Lionel Messi, ya jajanta wa tawagar Argentina ta ‘yan ƙasa da shekaru 20, bayan rashin nasarar da ta yi a gasar da aka kammala ranar Lahadi a ƙasar Chile.
Messi ya wallafa a Instagram cewa, “Ku saurara, yara!!! Kun taka rawar gani a gasar, kuma duk da cewa mun so ganin kun ɗaga kofin, mun yi murna da abin da kuka ba mu, da kuma alfaharin yadda kuka kare tutar ƙasarmu da zuciyarku.”
Wannan rashin nasara ta ja hankalin tauraron ɗan wasan, wanda ya taɓa lashe gasar ta ‘yan ƙasa da shekaru 20 tare da Argentina a shekarar 2005.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Argentina Kofin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta kama matashin nan da ake zargi da kashe makwabciyarsa a unguwar Shuwari II, a garin Maiduguri babban birnin jihar, ta hanyar daba mata wuka.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na dare a ranar Talata.
Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwaYa ce ana zargin matashin ne mai shekaru 17 da aka fi sani da Amir, wanda makanike ne da kashe matar ta hanyar daba mata wuka.
Wani makwabcin wajen ya shaida cewa ana zargin matashin ne da shiga gidan ta hanyar tsallake katanga bayan ya jira ragowar mutanen gidan sun shiga ciki.
A cewar majiyar, matashin ya ɗauki wuƙa ya daba wa matar gidan, wadda ba a bayyana sunanta ba, a ƙirji da wuya, sannan ya tafi da wayarta da na’urar cajin hannu (power bank).
Majiyar ta ƙara da cewa bayan aikata laifin, wanda ake zargin ya koma gidansu ya wanke tufafinsa da kayan da ya yi amfani da su domin kauce wa bin sahunsa.
Rahotanni sun ce ƙanwar mijin wadda aka kashe ce ta fara sanar da jama’a bayan ta ji ihun matar tana neman taimako.
Lokacin da ta fito ta duba, sai ta ga wanda ake zargin yana gudu ya koma gidansu.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa jami’an ’yan sanda sun kama matashin da misalin ƙarfe 2:30 na rana.
Sai dai kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, bai samu damar yin ƙarin bayani ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.