2025-10-22@11:34:06 GMT
إجمالي نتائج البحث: 3922

«tashar jiragen»:

    Dr Majid Ghayour Mubarhan kwararre kuma farfesa a jami’ar kiwon lafiya ta birnin mashahada ya samu kyautar hukumar WHO na gabashin meditareniya saboda namijin kokarin da yayi na kirkiro abin da zai kula da kuma kare kamuwa da cututtuka da basa yaduwa, kamar cutar kansa ciwon zuciya da kuma ciwon Sugar. Wannan kyautar tana nuna irin ci gaban da Iran ta samu ne a bangaren kimiyyaa yankin duk da takunkumi da kuma takurawar da take fuskanta daga bangaren kasashen turai dake takaita halartar masana kimiyyar kasar  hallara a matakin kasa da kasa. A duk shekata hukumar lafiya ta duniya tana bada kyauta ga duk wani masanin kimiya da yayi kwazo wajen kirkiro wata fasaha a bangaren lafiyar gama gari,  da...
    Babban jam’in hukumar tsaro ta kasar iran ya bayyana jin dadin kasar iran ga kasar Rasha saboda goyon bayan da ta bata a kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya kan hakkin iran a gaban kasashen turai dake kokarin kakkaba mata sabon takunkumin karya tattalin Arziki, Babban sakataren tsaro na kasar Iran Dr Ali Larijani ya fadi hakan ne a jiya talata A wata ganawa da yayi da jakadan shugaban kasar Rasha Alexander Lavrentiev da ya kawo ziyara nan kasar iran , larijani a matsayinsa na mai bawa jagora shawara ya jinjinawa kasar rasha game da goyon bayan da take bawa kwamitin. LarIjani da sauran jami’an gwamnatin kasar Rasha sun yi bitar matakin hadin guiwa dake tsakanin Tehran da mosko a...
    Piwuna, ya ce gwamnati ta gaza cika alƙawurran da ta ɗauka duk da sanarwar kwanaki 14 da ASUU ta bayar tun a ranar 28 ga Satumba, 2025. Ya ce babu wani abin da aka cimma wanda zai hana ƙungiyar aiwatar da shawarar majalisar zartarwarta na fara yajin aikin. “Dukkanin rassan ASUU a faɗin ƙasar nan an umarce su da su janye ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na dare ranar Litinin,” in ji Piwuna Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin wannan lokaci, za ta ɗauki mataki mafi tsanani bayan kammala yajin aikin gargaɗin. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe...
    Piwuna, ya ce gwamnati ta gaza cika alƙawurran da ta ɗauka duk da sanarwar kwanaki 14 da ASUU ta bayar tun a ranar 28 ga Satumba, 2025. Ya ce babu wani abin da aka cimma wanda zai hana ƙungiyar aiwatar da shawarar majalisar zartarwarta na fara yajin aikin. “Dukkanin rassan ASUU a faɗin ƙasar nan an umarce su da su janye ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na dare ranar Litinin,” in ji Piwuna Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin wannan lokaci, za ta ɗauki mataki mafi tsanani bayan kammala yajin aikin gargaɗi. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe...
    Labaran da suke fitowa daga birnin Khartum babban birnin kasar Sudan sun bayyana cewa jirgin yaki na kunan bakin wake ya fada kan wani yanki kusa da tashar jiragen sama na birnin kwana guda kafin gwamnatin kasar ta sake bude ta fiye da shekaru biyu da sufe ta. Shafin yanar gizo na labarai ‘ArabNews’ na kasar Saudiya ya bayyana cewa an rufe tashar jiragen sama na Khurtum ne, jim kadan bayan fara yaki da a cikin watan Afrilun shekara ta 2023.  Yaki tsakanin sojojin Sudan da kuma dakarun  ‘ Rapid Support Forces (RSF), dakarun daukin gaggawa wanda ya lalata muhimman kayakin aiki a tashar, hakan ya sa aka rufe ta.   Wakilin kanfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya...
    Shugaban kungiyar Hizbullah Ta Kasar Lebanon Sheikh Na’em Qasim ya bayyana cewa, ya bayyana cewa Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu ya zubar da jinin mutanen yankin yammacin Asia da dama, amma wannan bai bashi lamunin cewa haramtacciyar kasar Isra’ila (HKI) zata zauna lafiya a yankin nan gaba ba. Tashar tal;abijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban kungiyar yana fadar haka a jiya Talata a wani bikin kaddamar da littafi wanda yake bayyana ra’yin Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaie dangane da wakoki da kidekide. Yace: Duk tare da zubar da jinin mutanen yankin a duk a lokacinda ya ga dama, Netanyahu ba zai ce yana da lamuni na zaman lafiya ga HKI a nan...
    A cikin jawabin da ya gabatar a wannan Talata da aka nuna kai tsaye a taron jana’izar  babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Yemen  Laftanar Janar Mohammed al-Ghamari, Sayyed Abdulmalik al-Houthi ya jaddada cewa, kasar Yemen za ta ci gaba da kasancewa cikin shirin komowa ga ayyukan soji idan Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta koma kisan kare dangi, da kuma ci gaba da killace yankin zirin Gaza. Sayyed al-Houthi ya yi ishara da irin babban gangami na dubban daruruwan mutane da suka taru a wurin jana’izar shahid al-Ghamari a matsayin abin da ke nuni da tsayin daka na al’ummar Yemen a kan manufofinsu. Sayyed al-Houthi ya kuma yi nuni da cewa al’ummar Yemen sun gamsu da matsayi mai Daraja da suke a...
    Wasu da ake zargin masu kwacen waya ne sun kashe ma’aikaciyar jinya a Asibitin Gambo Sawaba da ke Zariya a jihar Kaduna mai suna Hadiza Musa. Bayanai sun ce marigayiyar it ace mataimakiyar shugabar sashen haihuwa a asibitin. Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi Mijinta, Hamza Ibrahim Idris, wanda ke aiki a Abuja, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kashe matarsa ne a ranar Asabar yayin da take dawowa daga aiki. “A ranar Asabar, ta kira ni ta ce za ta je wajen gyaran gashi sannan ta ziyarci wani shagon masu magani a Filin Mallawa, Tudun Wada Zariya, kuma na amince.”...
    Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira biliyan ɗaya domin gyaran ajujuwan karatu a wasu makarantu na gwamnati. Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse. A cewarsa, majalisar zartarwar jihar ta amince da kashe fiye da Naira miliyan 528 domin gyaran ginin ajujuwa a wasu zababbun makarantu na gwamnati a fadin jihar. Ya bayyana cewa, manufar aikin ita ce inganta yanayin karatu, tabbatar da tsaro, da kuma samar da iingantaccen ilimi karkashin shirin gwamnatin jihar na farfado da ilimin asali. Sagir Musa ya kuma ce, majalisar ta amince da kashe sama da Naira miliyan 512 domin  samar...
      “Wadanda aka nada sun bayyana a gaban kwamitin don tantancewa a ranar Talata, 14 ga Oktoba, 2025,” in ji shi. “Kwamitin bai samu koke ko korafe-korafe ba a kansu, sun nuna shiri da cancanta akan ayyukan da aka zabo su”.   Ya bayyana sunayen wadanda aka tantance a matsayin: “Aminu Yusuf (Jihar Neja) – Shugaba, Joseph Haruna Kigbu (Jihar Nasarawa) – Kwamishina, Tonga Betara Bularafa (jihar Yobe) – Kwamishina. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi October 21, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja October 21, 2025 Manyan...
    ‘Yan sanda a birnin Abuja sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa Zanga-zangar masu neman a saki jagoran ‘yan awaren Biafar Nnamdi Kanu wanda ake yi wa shari’a bisa tuhumarsa da ayyukan ta’addanci. Shi dai Kanu yana jagorantar kungiyar ‘yan asalin Biarafa ( Ipob) a takaice wacce a hukumance an haramta, saboda kiran da take yin a balle yankin kudu masu gabashin kasar da ‘yan kabilar Igbo suke da rinjaye domin kafa musu kasa mai cin gashin kanta. Jami’an tsaro sun rika yin sintiri a tsakiyar birnin Abuja, da motoci masu silke da kuma masu watsa ruwan zafi. Haka nan kuma sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye akan masu goyon bayan kungiyar da su ka...
    Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanar da shirinsa na ɗaga darajar Kwalejin Jinya ta Nafisatu da ke Kwankwaso zuwa cikakkiyar Jami’ar Kiwon Lafiya albarkacin bikin zagayowar ranar haihuwarsa. Taron na wannan Talatar, 21 ga watan Oktoban 2025, ya gudana ne a garinsa na Kwankwaso da ke Karamar Hukumar Madobi, inda aka yaba da ci gaban da makarantar ta samu tun daga kafuwarta a 2019 zuwa yanzu. Tinubu ya naɗa sabon Minista Alƙaluman wucin-gadi na nuna Paul Biya ya lashe zaɓen Kamaru Kwankwaso ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin ƙara buɗe damammaki ga mata matasa su sami ilimin kiwon lafiya mai zurfi. Ya jaddada cewa makarantar ita ce ta farko a Najeriya da ke karɓar dalibai...
    A Yemen Dubban daruruwan mutane ne suka fito titunan birnin Sana’a domin jana’izar babban hafsan hafsan sojin kasar, Laftanar Janar Mohammad Abd al-Karim al-Ghamari, wanda aka ayyana shahadarsa a hare-haren da Isra’ila ta kai a watan Agusta… Taron dai ya nuna matukar hadin kan al’ummar kasar, da suka fito daga sassan babban birnin kasar da larduna daban-daban, tare da manyan jami’an soji da wakilan gwamnati. Jama’a na dauke da hotunan marigayi Janar din, tutocin kasar Yemen, da tutoci masu nuna goyon baya ga gwagwarmayar Falasdinu da kuma yin Allah wadai da harin Amurka da Isra’ila. Tashar Al Mayadeen ta bayar da rahoton cewa, dubun dubatar ‘yan kasar ne suka halarci jana’izar, yana mai nuni da irin yadda jama’a ke girmama...
    Kasashen Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a Gaza Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da mai baiwa kasar Iraki shawara kan harkokin tsaro Qasim al-Araji sun bukaci kasashen duniya da su dakatar da kisan gillar da gwamnatin Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a zirin Gaza. Al-Araji, wanda ke jagorantar wata tawagar jami’an tsaro a kasar Iran, ya gana da Araghchi a yammacin jiya Litinin, inda suka yi musayar ra’ayi da su kan hanyoyin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, da kuma tattauna halin da ake ciki a Gaza da Lebanon. Dukkan jami’an biyu sun bayyana damuwarsu kan yadda Isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude...
    Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanyar Babban Sara zuwa Malam Bako zuwa Shabaru zuwa Kirgi zuwa Albasu, mai tsawon kilomita 28.2, a Karamar Hukumar Sule Tankarkar,wanda kudinsa ya kakaNaira Biliyan 4.47, a ci gaba da shirin Gwamnati da Jama’a. Aikin hanyar zai hada fiye da kauyuka 60 tare da karfafa harkokin kasuwanci da zamantakewa a yankin. Haka kuma, gwamnan ya bude sabuwar cibiyar kula da lafiya ta farko, da makarantar Tsangaya ta zamani, da kuma rukunin samar da ruwa a yankin. Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin Gwamnati da Jama’a hanya ce ta karfafa gaskiya, bayyana ayyuka da kuma baiwa jama’a damar fadin  ra’ayoyinsu. “Mun zo ne mu nuna abin da muka...
    Kakakin fadar Kremlin Dmitry Peskov ya sanar a wannan  Litinin cewa, kasar Rasha a shirye take ta fadada hadin gwiwa da Iran a dukkan bangarori, yana mai cewa, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu tana ci gaba da kara habaka, da kuma  amincewa da juna. Peskov ya yi nuni da cewa, Moscow na goyon bayan ci gaba da shawarwari kan yarjejeniyar shirin nukiliyar Iran, yana mai jaddada cewa, “Matsayar da kasashen turai suka dauka game da batun Shirin ba ta da amfani, kuma hakan  yana kara  dagula lamurra, da kuma kawo cikas ga  duk wani ci gaba na hakika kan wannan batu.” In ji shi. Wannan matsayi na Rasha, na zuwa ne a daidai lokacin da lamurra suke kara rincabewa a...
    Wata kotun majistare da ke Kano ta umarci Hukumar Hisbah ta jihar da ta shirya ɗaura aure tsakanin wasu fitattun ’yan TikTok guda biyu — Idris Mai Wushirya da Basira Yar Guda — cikin kwanaki 60. Kotun ta bayar da wannan umarnin ne bayan yaɗuwar bidiyon Mai Wushirwa da ’Yar Guda a kafafen sada zumunta, da Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta bayyana a matsayin “na batsa da rahsin tarbiyya.” Bidiyoyin sun nuna waɗannan ’yan TikTok ɗin suna nuna soyayya a bainar jama’a, abin da hukumomi suka ce ya saɓa da ɗabi’u da koyarwar addini da al’adun mutanen Jihar Kano. A yayin zaman kotun ranar Litinin, Mai Shari’a Halima Wali ta yi gargaɗi cewa idan ba a ɗaura auren...
    Mahdieh Esfandiari, malamar jami’a ba’iraniya tana daga cikin Iraniyawar da za’a yi musayarta a shirin musayar fursinonin tsakanin JMI da Farans a cikin yan kwanaki masu zawa. Tashar talabijib ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin wajen  kasar Iran Vahid Jalalzadeh yana fadar haka ya kumakara da cewa JMI ta yi amfani da hanyoyin diblomasiyya wandanda sukakai ga musayar fursinonin tsakanin ta da kasar Faransa kuma daga cikin wadanda Faransa zata yi musayar da su har da ita Mahdieh  Esfandiari wacce gwamnatin kasar Faransa ta tsare ta tun watan Maris na wannan shekara saboda ta nuna goyon bayanta a Falasdinawa a shafinta na yanar gizo. Jalalzadeh ya kara da cewa , duk tare da cewa gwamnatin kasar Faransa...
    Ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta bada sanarwan cewa a cikin sa’o’ii 24 da suka gabata sojojin HKI sun kai falasdinawa 57 ga shahada, wanda kuma ya kawo adadin wadanda ya kawo yawan wadanda ta kashe tun fara yakin tufanul Aksa zuwa 68,216. Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto majiyar na cewa sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa 45 kai tsaye da makamansu daga sama kasa da kuma ruwa a yankuna daban daban na zirin gaza a yayinda gawaki 12 kuma yana daga cikin wadanda aka zakulo daga burbushin gine-gine. Har’ila yau sun jikata wasu Falasdinawa 158 a cikin wannan lokacin. Ma’aikatar ta kara da cewa har yanzun akwai dubban gawakin Falasdinawa a karkashin gine-ginen da aka rusa...
    A jiya litinin ce masu goyon bayan Nnamdi Kanu shugaban kungiyar neman kafa kasar Biafara (IPOP) daga tarayyar Najeriya, wanda ake tsare da shugaban kungiyar tare da tuhumar ayyukan ta’addan sun fito zanga-zanga suka kuma tushe wata babban titi a Abuja. ‘Yansanda sun jefa masu hayakin teargas don tarwatse su a jiya litinin. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayyana cewa Kanu wanda yake da Passport na kasar Burtania ya yi kokarin wanke kansa daga tuhumar da ake masa tun 2021 amma ya kasa. Kanu yana jagorantar kungiyar IPOP tun da dadewa, da nufin samar da kasar Biafara a yankin kudu maso gabacin Najeriya. Kafin haka dai yan kabilar Ibo sun yi kokarin bellewa daga tarayyar Najeriya a...
    Wakilin Amurka a kasar Syria Tom Barak ya bayyana a wannan Litinin cewa, shirin shugaban Amurka Donald Trump mai dauke da abubuwa 20 na dakatar da yakin zirin Gaza ya haifar da wani sabon yanayi na siyasa, wanda hakan ya sa batun kulla alaka tsakanin kasashen larabawa da Isra’ila ya kara samun karbuwa fiye da kowane lokaci. Barak ya bayyana a wani sakon da ya wallafa a shafukan sada zumunta cewa, “hanyar samun zaman lafiya a yankin ta bayyana karara duk kuwa da kalubalen da ake fuskanta, musamman dangane da warware matsalar Hamas.” In ji shi. Ya kara da cewa: “Saudiyya na gab da shiga yarjejeniyar kulla alaka da Isra’ila a hukumance, yayin da ta yi hakan, sauran kasashe za...
    Kakakin fadar Kremlin Dmitry Peskov ya sanar a wannan  Litinin cewa, kasar Rasha a shirye take ta fadada hadin gwiwa da Iran a dukkan fannoni, yana mai cewa, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu tana ci gaba da kara habaka, da kuma  amincewa da juna. Peskov ya yi nuni da cewa, Moscow na goyon bayan ci gaba da shawarwari kan yarjejeniyar nukiliyar Iran, yana mai jaddada cewa, “Matsayar da kasashen turai suka dauka game da batun Shirin Iran na nukiliya ba ta da amfani, kuma hakan  yana kara  dagula lamurra, da kuma kawo cikas ga  duk wani ci gaba na hakika kan wannan batu.” In ji shi. Wannan matsayi na Rasha na zuwa ne a daidai lokacin da lamurra suke kara...
    Jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga shugaban Amurka Trump cewa: su ci gaba da mafarkinsu! Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei a yayin da yake tsokaci kan kalaman shugaban Amurka a yayin ziyarar da ya kai yankunan da aka mamaye, ya ce Trump cikin alfahari ya ce kasarsa ta yi luguden bama-bamai tare da lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, yana mai mayar msa da martani cewa: “To, su ci gaba da yin mafarkinsu!” A yayin ganawarsa da safiyar yau da zakaran wasanni kuma wadanda suka lashe gasar Olympics ta kasa da kasa, Jagoran ya kara da cewa: Duk abin da kuke yi ana danganta shi da Iran da kuma al’ummar kasar  ne, kuma...
    Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta samu nasarar tara dukiyar da ta haura naira biliyan 500 a tsawon shekaru biyu na gwamnatinsu. Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya bayyana haka ne a yayin wani taron bita da ƙara wa juna sani na alƙalai da Hukumar EFCC tare da haɗin gwiwar Hukumar Shari’a ta Najeriya (NJC) suka shirya a birnin Abuja. Red Cross ta kafa cibiyoyin rage haɗurran bala’o’i a makarantun Gombe NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU Shettima ya buƙaci alƙalai da sauran ma’aikatan ɓangaren shari’a da su ƙara ƙaimi tare da yin aiki bisa gaskiya da adalci, yana mai...
    Ƙungiyar Agaji ta Red Cross ta Najeriya (NRCS), tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Italiya, ta kafa cibiyoyin Rage Haɗurran Bala’o’i (Disaster Risk Reduction – DRR) a makarantun sakandare guda biyu a Jihar Gombe, domin inganta shirye-shiryen kare kai daga bala’o’i da kuma ƙarfafa juriya a tsakanin matasa. Makarantun da suka amfana da wannan shiri su ne Ƙaramar Sakandaren Gwamnati ta Pilot da kuma Sakandaren Gwamnati ta Comprehensive, Deba. NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a Kano A yayin bikin ƙaddamar da cibiyoyin, ƙungiyar Red Cross ta raba kayan karatu da suka haɗa da jakunkuna masu ɗauke da bayanai kan DRR, littattafan rubutu, alƙalumma da kayan lissafi...
    Fitaccen jarumin barkwancin finafinan Indiyan nan Asrani ra rasu. Asrani, wanda  asalin sunansa shi ne Govardhan Asrani, ya rasu yana mai shekaru 84, kuma ya shafe sama da shekara 50 yana fitowa a finafinan Indiya, inda ya fito a finafinai sama da 350. Dan wasan finafinan, ya shahara wajen taka rawar barkwanci da kuma ƙaramin jarumi wanda ake kira da mai taimaka wa jarumi wato supporting actor. Daga cikin fina-finansa da suka yi fice akwai Sholay, inda ya fito a matsayin ɗansand da Bawarchi da Chupke-Chupke da Hera Pheri da Muqabla da Dhamaal da Yamla Pagla Deewana da Dillagi da Welcome da Bhool Bhulaiya da Garam Masala da Baghban da The Burning Train da Ajnabee da Seeta aur Geeta da...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing October 20, 2025 Daga Birnin Sin Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana October 20, 2025 Daga Birnin Sin Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20 October 19, 2025
    Jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga shugaban Amurka Trump cewa: su ci gaba da mafarkinsu! Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei a yayin da yake tsokaci kan kalaman shugaban Amurka a yayin ziyarar da ya kai yankunan da aka mamaye, ya ce Trump cikin alfahari ya ce kasarsa ta yi luguden bama-bamai tare da lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, yana mai mayar msa da martani cewa: “To, su ci gaba da yin mafarkinsu!” A yayin ganawarsa da safiyar yau da zakaran wasanni kuma wadanda suka lashe gasar Olympics ta kasa da kasa, Jagoran ya kara da cewa: Duk abin da kuke yi ana danganta shi da Iran da kuma al’ummar kasar  ne, kuma...
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Tana tabbatar da yin riko da hakkokin kasarta na kare hakkin mallakar makamashin nukiliya na zaman lafiya Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa, a yayin shawarwarin da aka yi a birnin New York da kuma fahimtar da mahukuntan birnin Alkahira suka yi da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa, jami’an yammacin duniya da ke bin Amurka, sun bukaci a maido da kudurorin takunkumin da kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya ya kakaba kan Iran a shekarar 2006 zuwa 2010, to amma kasashen China da Rasha sun fito fili suna adawa da wannan gurguwar tunani tare da jaddada rashin amince da shi. A farkon taron manema labarai...
    Babban sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran ya karbi bakwancin takwaransa na kasar Iraki a birnin Tehran Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani, ya karbi bakwancin mai baiwa kasar Iraqi shawara kan harkokin tsaro, Qasim al-Araji. A yau litinin ne mai baiwa kasar Iraqi shawara kan harkokin tsaro, Qasim al-Araji, ya iso birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran, inda yake jagorantar wata babbar tawaga ta tsaro. Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya gana da mai baiwa kasar Iraqi shawara kan harkokin tsaro Qasim al-Araji, inda suka tattauna batutuwa da dama musamman kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu da muhimman mu’amalar da ke tsakaninsu. Share 0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify...
    Wakilin Amurka na Musamman a kasar Siriya ya matsa kaimi domin ganin kasashen Saudiyya da Lebanon da kuma Siriya sun kulla alakar jakadanci da haramtacciyar kasar Isra’ila Wakilin Amurka na musamman a Siriya Tom Barrack, ya gabatar da manufofinsa na sake fasalin yankin Gabas taTsakiya a siyasance bayan kawo karshen yakin Gaza. A cikin dogon hangen nesa, wanda ya wallafa a shafinsa na Twitter, Barrack ya yi ikirarin cewa abu mafi muhimmanci shi ne samar da zaman lafiya a yankin, da kwance damarar Hizbullah, da shigar da kasashen Labanon da Siriya cikin yarjejeniyoyin kyautata alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila. Ya kara da cewa Saudiyya ma tana dab da kyautata alakarta da haramtacciyar kasar Isra’ila. Barrak ya bayyana cewa: Taron Sharm...
    Jam’iyyar APC reshen Jihar Borno ta rage wa mata kashi 50 cikin 100 na farashin fom ɗin tsayawa takara, makonni gabanin zaɓen kananan hukumomi da za a gudanar a ranar 13 ga Disamba, 2025. Da yake sanar da hakan a Maiduguri, shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bello Ayuba, ya ce an ɗauki matakin ne domin magance matsalar ƙarancin kuɗi da ke hana mata shiga siyasa da tsayawa takara. Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20 Dembele ya dawo PSG bayan jinyar makonni “Wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da muke yi na samar da daidaito ga mata a fagen siyasa. “Muna son ganin mata da yawa suna jagoranci a matakin ƙasa, suna ba da gudummawa...
    Hukumar gudanarwar Kungiyar Kwallon kafa ta Kano Pillars ta dakatar da Babban Kocinta Ahmed Garba Yaro Yaro da bai ba da shawara ga  Kocin, Ogenyi Evans, nan take. Ta kuma nada tsohon kyaftin kuma Mataimakin Koci, Gambo Muhammad nan take, ya jagoranci lamuran fasaha na ƙungiyar. Mai horar da masu tsaron raga, Suleiman Shuaibu, zai taimaka masa, yayin da Koci Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai ba da ƙarin goyon baya har sai an fitar da sabbin umarni. Kungiyar ta dauki wannan mataki ne bayan abin da ta kira “rashin tagomashinta” a Gasar Firimiyar Najeriya (NPFL) ta 2025/2026 da ake ci gaba da yi. Sanarwa da kulob ɗin ta fitar, hukumar gudanarwar ta ce an ɗauki matakin ne bayan...
    Don haka, an nada “tsohon kaftin din kungiyar kuma mataimakin koci, Gambo Muhammad, tare da mai horar da masu tsaron gida, Suleiman Shuaibu, su maye gurbin wadanda aka sallama na dan wucin gadi. Bugu da kari, Koci Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai taimakawa wadanda aka nada na dan wucin gadin”.   LEADERSHIP ta ruwaito cewa, kungiyar mai taken ‘Sai Masu Gida’ tana fama a ‘yan makonnin nan. Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ta kuma ci tarar kungiyar tarar kudi sama da Naira miliyan 9 biyo bayan rikicin da ya ɓarke a yayin da suke karawa da wata kungiya a filin wasa na Sani Abacha. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A...
    Dakarun kare juyin musulunc na kasar iran ta bayyana cewa tana da cikakken shiri na kafa fadada dabarun yin hadin guiwa da dakarun karejuyin musulunci na kasar yamen wajen kalubalnatar kasashe ma’abota girman ai da kuma yan sahyuniya. A cikin sakon da kwamandan dakarun kare juyin musulunci na iran ya fitar a jiya lahadi mojor ganar mohammad pakpur ya aike da sakon ta’aziya ga babban hafsan hafsoshin sojin kasar Yamen  brigadier janar Yousef hassan al’madani na shahadar major ganar mohammad abdular karin al’gamari wanda yayi fama da rashin lafiya sakamakon rauni da ya ji a harin da isra’ila ta kai masa a watan Augusta  tare da wasu abokan aiki  har da dan sa mai shakara 13. Har ila yau ya...
    Rahotanni da gwamnatin Gaza ta fitar ya nuna cewa sojojin Isra’ila sun keta yarjejeniyar da aka cimma tsakani, har sau 80 wanda  haka ya jawo mutuwar falasdinawa 97 da kuma jikkata wasu guda 230 na daban kuma tana ci gaba da cin zarafin wasu a yankunan da ta mamaye. Duk da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimma tsakanin Hamas da Isra’ila a Gaza a  kasar Masar, amma isra’ila ta dawo da ci gaba da kai hare harenta , lamari da ya jawo suke daga bangaren jami’an gwamnatin faladinu. Tun bayan da aka sanar da dakatar da bude wuta a gaza sau 80 ke nan isra’ila tana keta yarjeejniyar da sandiyar haka mutane 97 suka mutu wasu guda 230...
    Darakta Janar na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) Rafael Grossi ya bayyana kwarin gwiwar cewa, za a iya warware takkadama kan shirin Iran na makamashin nukiliya ne ta hanyar diflomasiyya kadai. Grossi ya bayyana hakan ne a wata hira da jaridar Neue Zeitung ta kasar Switzerland a jiya Lahadi. Shugaban hukumar ta IAEA ya ce, masu binciken ba su sami wata shaida da ke nuna cewa Iran ta boye wani adadi na sinadarin uranium da aka inganta ba. Ya kara da cewa, “Yawancin abubuwan da aka samu na Iran an adana su ne a wuraren da aka sani a Isfahan da Fordow, da kuma wani lokaci a Natanz.” in ji shi. Grossi ya bayyana kwarin gwiwa cewa “za a...
    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce shugabannin Hamas ba su da hannu a harin da aka kaiwa sojojin Isra’ila a kudancin Gaza. Da yake magana da jami’an sojin sama na Amurka wato Air Force One a jiya Lahadi 19 ga Oktoba, Trump ya danganta harin da wasu da ya kira wadanda suka yi tawaye a cikin kungiyar Hamas. Trump ya bayyana a fili cewa: Ko ta yaya dai, za a kula da lamarin yadda ya kamata. Za a dauki matakai masu tsauri, amma yadda ya kamata a cewarsa. Trump ya kuma kara da cewa, yana fatan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza za ta ci gaba da tabbatar da manufofin Washington na wanzar da zaman lafiya a Gaza. An kashe...
    Sojojin ruwa na kasar  Iran da kuma Azerbaijan sun fara atisayen hadin giwa dangane da ceto da kuma kai dauki a kusa da tsibirin Boyuk kusa da babban birnin kasar Azerbaijan Baku a cikin tekun Caspian. Kamfanin dillancin labaran tasnim na kasar Iran ya nakalto majiyar atisayin na cewa, sojojin ruwa na JMI  da kuma na dakarun kare njuyin juya halin musulunci IRGC har iyla yau da sojojin ruwa na kasar Azerbaijan ne suke cikin atisayen na kwanaki 4 wanda kuma sukabawa suna  AZIREX 2025. Jiragen yakin da suke aiki a wannan atisayen sun hada da Paypan, da makamai masu linzamina sepah da jirgin ruwa yaki na Shaahid Labarin ya kara da cewa manufar wannan Atisayen sun hada da karfafa...
    An saki ɗan jarida, Ibrahim Ɗan’uwa Rano, bayan da ƴansanda suka tsare shi a shalƙwatar Rundunar Ƴansanda ta Zone 1 Kano bisa zargin batanci ga wani mutum. Sakin nasa ya biyo bayan suka da matsin lamba daga ƙungiyoyin fararen hula irinsu Cibiyar Fasahar Bayanai da Ci Gaban Jama’a (CITAD), da Amnesty International, da sauran ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam, waɗanda suka bayyana tsarewar tasa a matsayin mataki na keta haƙƙin ɗan Adam da kuma yunƙurin danne ƴancin ƴan jaridu. Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya  Ƙungiyoyin sun buƙaci a sake shi ba tare da wani sharaɗi ba, suna mai cewa tsarewar ta saɓawa...
    Ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci ya bayyana cewa, mafi yawancin kasashen duniya sun yi Imani da ka’idoji na cin gashin kai da ‘yanci. Abbas Arakci wanda ya gabatar da jawabi a wurin zaman majalisar zartarwa a yau Lahadi ya ce ya bayyana cewa a fagen diplomasiyya Iran ta dauki makamin dakile kokarin kasashen turai na sake dawu da takunkumi a kanta, ta hanyar aiki tare da kasashen Rasha da kuma China. Haka nan kuma ya yi jinjina ga matakin bayan nan da kungiyar ‘yan-ba-ruwanmu ta dauka na nuna cikakken goyon bayanta ga Iran, yana mai cewa; Ana samun kafuwar sabon kawance a duniya, yayin da kasashen turai da wasu tsiraru suke a gefe daya, ita kuwa Iran da mafi...
    Ƴansandan sun kuma yi kira ga ƴan jarida da su tabbatar da daidaito a rahotanninsu, tare da tuntuɓar sashin hulɗa da jama’a na yankin kafin yaɗa labaran da ke da sarƙakiya. AIG Garba ya gargaɗi ƴan jarida da su guji tsoma baki a cikin binciken da ke gudana, yana mai cewa “a bar doka ta yi aikinta.” Sai dai sanarwar ba ta fayyace halaccin tsarewar farko da aka yi wa ɗan jaridar ba, ko kuma ko an kama shi ne ba tare da takardar izinin kame ba. A halin yanzu, ƙungiyoyin kare ƴancin ƴan jarida da ƙungiyoyin farar hula da dama suna ci gaba da kira ga ƴansanda da su saki Ishaq tare da dakatar da duk wani yunƙuri na...
    ’Yan Sanda sun saki ɗan jaridar Kano, Ibrahim Ɗan Uwa Rano, bayan tsare shi da suka yi kan zargin ɓata sunan hadimin Gwamnan Jihar, Abdullahi Ibrahim Rogo. An tsare Rano a Shiyyar ’Yan Sanda ta Ɗaya da ke Kano, bisa zargin ɓatanci. Talauci ne babban maƙiyin ɗan Adam — Atiku ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun bayyana tsare shi a matsayin saɓa doka da kuma ƙoƙarin danne ’yancin ’yan jarida.
    Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana talauci a matsayin babban abokin gabar ɗan Adam. Ya ce ƙaruwar talauci a Najeriya na ci gaba da jawo rashin lafiya, jahilci, rashin tsaro, da rashin fata a tsakanin jama’a. ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook domin bikin Ranar Yaƙi da Talauci ta Duniya, Atiku, ya ce wannan rana tana tunatar da gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki muhimmancin ƙara ƙoƙari wajen yaƙar talauci “Talauci ne babban abokin gabar ɗan Adam. Yana haifar da matsaloli kamar rashin lafiya, jahilci, rashin tsaro da sauransu,” in...
    Hukumar samar da abinci ta MDD ta bukaci a bude duk wasu hanyoyi domin shigar da abinci a Zirin Gaza, saboda yadda magance matsalar yunwa a Zirin zai dauki lokaci. Kakakin WFP Abeer Etefa ta shaidawa manema labarai a Geneva cewa, za a dauki lokaci kafin a rage yunwa. “Yanayi a Gaza yana da matukar wahala kuma har yanzu muna da nisa daga cimma wannan burin,” in ji ta. A cewar WFP, bukatar gaggawa ta ta’allaka ne ga “bude mashigar kan iyaka guda biyar” zuwa cikin yankin “domin a wadata Gaza da abinci da kuma samar da wuraren rarrabawa cikin gaggawa,”. Shirin WFP, “shi ne kara yawan taimakon da za a kai ga mutane miliyan 1.6 a cikin Gaza cikin...
    Yanzu kuma za a ci gaba da tattaunawa kan yadda za a aiwatar da sauran sharuddan da ke ke kunshe a yarjejeniyar.   Masu sanya ido na ganin cewa aikin sake ginan yankin Gaza wanda aka rushe kusan daukacinsa a yakin da aka yi na shekara biyu, zai zama babban kalubale.   Wannan ce ranar da kowa ke jira -Trump A lokacin da Donald Trump ya yi jawabi, ya bayyana yau a matsayin “ranar da kowa ya yi ta hankoro da addu’ar ganin zuwan ta.” Shugaban na Amurka ya ce “Wannan yarjejeniya mai matukar tarihi” wadda gungun shugabannin duniya suka sanya wa hannu, na nuna cewa “addu’ar miliyoyin al’umma ta karbu”. Daga nan sai ya ce shugabannin sun samu nasarar...
    Bayanai daga rundunar sojin Najeriya na cewa an kafa wani kwamiti da ke binciken wasu jami’ai 20 da aka tsare bisa zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Jaridar Premium Times ta ruwaito wata majiyar soji da ke da masaniya kan lamarin tana cewa al’amarin ya faru ne a ƙarshen watan Satumba. An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano An tsinci gawar wata mata da aka yi wa kisan gilla a Yobe Majiyar ta ce ana zargin jami’an da shirya zubar da jini a juyin mulkin, kasancewar akwai sunayen wasu manyan jami’an gwamnati da aka shirya yi wa kisan gilla. A cewar majiyar kamar yadda Premium Times ta ruwaito, daga cikin manyan jami’an gwamnatin waɗanda masu kitsa...
    Ofishin Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sanar  a ranar Asabar cewa “Mashigar Rafah a Gaza za ta kasance a rufe har sai abin da hali ya yi a nan gaba.” Ofishin Netanyahu ya kara da cewa, bude mashigar ya dogara ne bisa ga  yadda Hamas ta aiwatar da tsarin yarjjeniyar da aka cimmawa wajen mika gawawwakin Isra’ilawa da ke hannunta. Wannan bayanin ya zo ne jim kadan bayan da ofishin jakadancin Falasdinu a Masar ya sanar da cewa za a sake bude mashigar Rafah da ke kudancin zirin Gaza a ranar Litinin mai zuwa. A nata bangaren, kungiyar Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, matakin da Netanyahu ya dauka yana a matsayin keta sharuddan yarjejeniyar tsagaita bude...
    A wani jawabin da aka yada ta kafar sadarwar zamani ta shafin Facebook jiya, ma’aikatar ta kara da cewa tun lokacin da shi Gwamnan ya dare kan Kujerar mulkin Jihar, mulkin gwamna Inuwa ya kafa dokar ta baci kan lamarin daya shafi ilimi, inda ya bullo da tsare tsare da zuba jari da zummar bunkasa bangaren ilimiin.   Wadanda za su amfana da karin tallafin kudin karatun sun hada dalibai masu karatun da suka hada da PhD, MSc, PGD, BSc, HND, NCE, ND, da kuma Satifiket.   Da yake na shi jawabin wajen sa albarkacin baki kan ci gaban da aka samu, Shugaban kungiyar dalibai ‘yan asalin Jihar da suke Jami’ar Jihar Gombe, Abubakar Muhammad Yamanga, ya bayyanawa LEADERSHIP cewa...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Kuduri mai lamba 2231 ya ƙare aiki a yau A cikin wata wasika da ya aike wa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ministan harkokin wajen kasar Iran ya tabbatar da cewa a karshe kuduri mai lamba 2231 ya kare a yau, kuma duk wani kira na farfado da shi ko dawo da wa’adin kudirorin da ya kare, ba shi da wani tushe na shari’a, kuma ba zai iya haifar da wani tasiri na tilasta aiki da shi ba. Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Sayyid Abbas Araqchi ya aike da wasika zuwa ga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da kuma shugaban kwamitin sulhu...
    Wasikar Iran, Rasha da China ga Majalisar Dinkin Duniya dangane da kawo karshen kuduri mai lamba 2231 Mataimakin ministan harkokin wajen kasar mai kula da harkokin shari’a da kasa da kasa ya sanar da cewa, kasashen Iran, Rasha, da China sun aike da wata wasika ta hadin gwiwa zuwa ga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya dangane da kawo karshen kudurin kwamitin sulhu mai lamba 2231. Mataimakin ministan harkokin wajen kasar kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya bayyana irin gagarumin yunkurin diplomasiyya da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke yi na kawo karshen kudurin kwamitin sulhu mai lamba 2231 a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin...
    Makami mai linzami na Iran kirar “Ghadr-H” ya aika da sako mai muni ga gwamnatin mamayar Isra’ila Wani masani kan harkokin tsaro da tsare-tsare Kanar Abdul Karim Khalaf ya bayyana cikakkun bayanai masu inganci da siffofi na musamman na makami mai linzamin na Iran “Ghadr H”, yana mai jaddada cewa; Makamin ya aike da sako mai karfi ga gwamnatin mamayar Isra’ila saboda karfin da take da shi na kutsawa cikin mafi tsauri na tsaron iska da kuma gujewa radar. Khalaf ya bayyana a cikin bayanansa cewa: “Ghadr” ya bambanta da sauran hasken wadda da ba a taba ganin irinsa ba a cikin yaki da kuma karfin da yake da shi na barna saboda fasahar da ke dauke da shin a...
    Mataimakin firaministan kasar Sin, kana jagoran tawagar kasar mai tattauna batutuwan tattalin arziki da cinikayya da tsagin Amurka He Lifeng, ya zanta ta kafar bidiyo da sakataren baitul-malin Amurka Scott Bessent, da wakilin cinikayyar kasar Jamieson Greer a jiya Asabar. Yayin zantawar tasu, jami’an sassan biyu sun amince da gudanar da sabon zagayen tattaunawa game da batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya nan ba da jimawa ba. Kazalika, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi bisa sahihanci, da zurfafa tattaunawa, da musaya mai ma’ana dangane da yadda za a aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma, yayin tattaunawarsu ta wayar tarho a farkon shekarar nan, da ma muhimman batutuwa masu nasaba da dangantakar tattalin arziki da cinikayya...
    Shi ma a nasa jawabin yayin gudanar da taron, shugaban kwamitin Alhaji Abdullahi Abdulmalik Digi, ya ce, a shekaru hudu da ya yi yana jagorancin kwamitin sun yi abin da yakamata su yi, inda ya ce, a Azumin bara an dauki yara marayu 2000 da aka raba musu abinci da suka hada da buhunan shinkafa da kuma kayan Sallah da za su dinka, mata aka raba musu shadda mata kuma atamfofi inda jimillar kudin da aka kashe ya zama Naira miliyan 64.2.   Bayan wannan an kashe Naira milin 26 wajen biya wa yara 520 kudin makaranta, inda kowane yaro ake biya masa Naira dubu 50 a kananan hukumomi shida na FCT Abuja.   Sannan an kashe Naira miliyan 3...
    Dan wasan gaba na Barcelona Robert Lewandowski ba zai buga wasan hamayya tsakanin FC Barcelona da Real Madrid wanda ake yi wa take da El Classico ba bayan da zakarun na Sifaniya suka gano cewa yana fama da rauni a kafarsa ta hagu, dan wasan mai shekaru 37 ya samu rauni ne a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da Poland ta buga da kasar Lithuania ranar Lahadi. Lewandowski yana da tsagewar tsoka a cikin femoris na cinyarsa ta hagu,” in ji Barcelona a cikin wata sanarwa, yayin da kafofin yana labarai na Sifaniya suka ruwaito cewa zai iya yin jinyar makonni hudu zuwa shida, Barcelona za ta kara da Real Madrid wadda ke jagorantar gasar La Liga...
    Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa a Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya yi iƙirari cewa ministoci da manyan hafsoshin sojin ƙasar sun taya shi murnar bayan bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka kammala. Issa Tchiroma Bakary ya bayyana cewa ministoci da manyan jami’an tsaron da ministocin sun kira shi a waya suna jaddada goyon bayansu da niyyar biyayya ga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma abin da al’umma suka zaɓa. Ya bayyana haka ne wani a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, yana mai nuna godiya ga waɗanda suka goyi bayansa, tare da jaddada cewa wannan lokaci yana da muhimmanci matuka ga kasa. Ya ce, “Ina godiya daga zuciyata ga ministoci...
    Hukumomi a Gaza sun zargi sojojin Isra’ila da satar sassan jikin gawarwakin Falasdinawa tare da kira a binciki wannan “mummunan laifi.” Darektan ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza Ismail Thawabta, ya fada a ranar Jumma’a cewa sojojin “mamaya na Isra’ila sun mika musu gawarwaki 120 ta hannun kungiyar agaji ta Red Cross a cikin kwanaki ukun da suka gabata, amma mafi yawan sun zo cikin mummunan yanayi, suna nuna alamun kisa da kuma azabtarwa. Thawabta ya ce akwai alamun shakewa da alamar igiya a wuyansu, lamarin da ke nuni da kisa da gangan.” “Sassan gawarwakin mutane da yawa sun bace, ciki har da idanu, da sauran gabobin,” in ji Thawabta, wanda ya ce ya tabbatar da cewa sojojin Isra’ila “sun...
    A wani bayani da kungiyar Hamas din ta fitar tayi tir da Israila kan yanayin da gawarwarakin da ta bata na palasdinawa dake hannunta, inda aka ga alamomi na Azabtarwar ajikinsu da kuma cire wasu sassan jikinsu don haka ta yi kara da a kafa kwamitin bincike na kasa da kasa kan halin rashin dan adamta da isra’ilan  ta nuna kan gawarwakin. Ta ce yin amfani da hanyoyi daban daban wajen Azabtarwa yana haifar da damuwa sosai kuma ya taka dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar Janeva, kuma wadannan ayyukan daidai suke da kisan kiyashi kan alummar falasdinu,  Wasu kungiyoyin sun mika batun ga kwamitin kula da hakokin dan adam na majalisar dinkin duniya domin yin matsin lamba kan...
    A Madagaska jiya Juma’a ne kotun tsarin mulkin kasar ta rantsar da Kanar Michael Randrianirina a matsayin shugaban kasa. Hakan na zuwa ne bayan majalisar dokokin kasar ta tsige shugaban kasar Andry Rajoelina bayan ya tsere daga kasar sanadiyyar zanga zangar data rikide zuwa bore wa gwamnatinsa saboda matsalar wutar lantarki da ruwan sha. Tunda farko dai kanar Randrianirina ya kiyasta zai rike mulki na wa’adin watanni 18 zuwa 24 lokacin da za’a kai ga gudanar da zaben raba gardama na kundin tsarin mulkin kasar. A ranar Talata da ta gabata ne, Randrianirina ya sanar da juyin mulkin kwace Mulki a kasar yana mai danganta hakan da rashin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasar, da keta hakkokin bil’adama.  A kuma...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar iran Isma’il baqae yayi tir da harin da HKI ta kai a kudancin labanon kuma ta bayyana hakan a matsayin keta hurumin kasar , yace kasashen Amurka da faransa a matsayinsu na garanto wajen dakatar da bude wuta suke da alhakin taka mata burki kan hare-haren da take kaiwa. Wannan harin da Isra’iala ta kai a kudancin labanon rahotanni sun nuna cewa shi ne kusan karo na 5000 da ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma  tsakaninsu. Kuma wanann ba shi ne karon farko da Isra’ila ke keta yarjejeniyar da aka cimma ba, saboda  akwai dalilai masu yawa da suka tabbatar da haka saboda ta saba yi a yankin gaza da ma labanon din...
    Aƙalla makarantun gwamnati 188 ne aka rufe sakamakon mtsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya. Binciken da wakilanmu suka gudanar ya nuna cewa, an rufe makarantu da dama a yankin saboda hare-haren da ’yan bindiga suke kai wa ƙauyukan da kuma yadda wasu makarantun ke zama a matsugunin mutanen da rashin tsaro ya raba da muhallansu. Wakilanmu sun gano aƙalla an rufe makarantu 55 a Jihar Binuwai, 52 a Jihar Katsina, 39 a Jihar Zamfara, 30 a Jihar Neja, 6 a Jihar Sakkwato da kuma 6 a Kaduna, baya ga makaratu 52 da 55 da aka rufe a jihohin Katsina da Benuwai. Wannan adadi na iya zama sama da haka, saboda ba za a iya isa ga wasu wuraren ba....
    Hukumomi a Gaza sun zargi sojojin Isra’ila da satar sassan jikin gawarwakin Falasdinawa tare da kira a binciki wannan “mummunan laifi.” Darektan ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza Ismail Thawabta, ya fada a ranar Jumma’a cewa sojojin “mamaya na Isra’ila sun mika musu gawarwaki 120 ta hannun kungiyar agaji ta Red Cross a cikin kwanaki ukun da suka gabata, amma mafi yawan sun zo cikin mummunan yanayi, suna nuna alamun kisa da kuma azabtarwa. Thawabta ya ce akwai alamun shakewa da alamar igiya a wuyansu, lamarin da ke nuni da kisa da gangan.” “Sassan gawarwakin mutane da yawa sun bace, ciki har da idanu, da sauran gabobin,” in ji Thawabta, wanda ya ce ya tabbatar da cewa sojojin Isra’ila “sun...
    A Madagaska jiya Juma’a ne kotun tsarin mulkin kasar ta rantsar da Kanar Michael Randrianirina a matsayin shugaban kasa. Hakan na zuwa ne bayan majalisar dokokin kasar ta tsige shugaban kasar Andry Rajoelina bayan ya tsere daga kasar sanadiyyar zanga zangar data rikide zuwa bore wa gwamnatinsa saboda matsalar wutar lantarki da ruwan sha. Tunda farko dai kanar Randrianirina ya kiyasta zai rike mulki na wa’adin watanni 18 zuwa 24 lokacin da za’a kai ga gudanar da zaben raba gardama na kundin tsarin mulkin kasar. A ranar Talata da ta gabata ne, Randrianirina ya sanar da juyin mulkin kwace Mulki a kasar yana mai danganta hakan da rashin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasar, da keta hakkokin bil’adama.  A kuma...
    A yayin da Najeriya ke karkata zuwa amfani da kayan tsaro na zamani na cikin gida domin ƙarfafa gwiwar jami’an tsaronta a fagen fama, wani ɗan Jihar Katsina ya fara ƙera motar yaƙi nau’in Track Armored Personnel Carrier (TAPC). Jihar Katsina na daga cikin jihohin Arewa da suka fi fama da hare-haren ’yan bindiga, inda suka kashe dubban mutane tare da raba wasu da muhallansu gami da rusa harkokin tattalin arziki da na zamantakewa. Ana cikin haka ne wani ɗan asalin yankin Kaita a jihar mai suna Injiniya Ibrahim Lawal Ɗankaba, ya fara yunƙurin ƙera motar yaƙi, wadda ya sanya wa suna Beguwa, a ƙoƙarinsa na tallafa wa yunƙurin gwamnati na daƙile ayyukan ’yan ta’addanci da suka daɗe suna...
    Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yaman Sayyid Abdul-Malik Badreddin al-Houthi ya yi jawabi a yammacin yau alhamis kan batutuwa daban-daban da suka shafi duniyar musulmi, musamman abubuwan da suka faru a Gaza da Yemen. Ya ci gaba da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ba tare da la’akari da duk wani matsin lamba ba, ta yi sadaukarwa ta karshe a kan turbar goyon bayan Falasdinu, kuma ta bayar da dama ga kwamandojin gwagwarmayar ‘yanci, daga cikinsu akwai babban kwamandan shahidi Qassem Soleimani. Yayin da yake magana kan zagayowar shahadar babban kwamanda Yahya al-Sinwar, Sayyid Abdul-Malik Badreddin ya ce: “Babban darussan da ya bari na tsararraki, da kuma matsayinsa na sadaukar da kai da jihadi, suna wakiltar muhimman dabi’u da kuma babban...
    An gudanar da bikin bayar da lambar yabo ta wasan kwallon kafa na Asiya da Futsal na shekarar 2025 a birnin Riyadh na kasar Saudiyya. A bangaren mata kuwa, Marzieh Jafari, shugabar kungiyar kwallon kafa ta mata ta kasar Iran, ita ce babbar mai horar da mata, yayin da Salar Aghapour ta lashe kyautar ‘yar wasa mafi nuna kwazo a wasan Futsal a wannan  shekara. Share 0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran: Kudurin Kwamitin Tsaro Kan Yarjeniyar JCPOA Ya Kawo Karshe A Yau...
    Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fidda bayani kan cewa daga yau Asabar 18 ga watan Octoban shekara ta 2025, kudurin kwamitin tsaro na MDD wanda aka samar don goyon bayan aiwatar da yarjeniyar Nukliyar kasar Iran wacce aka fi sani da JCPOA ya kawo karshe. Don haka daga yau shirin Nukliyar kasar Iran ta koma karkashen yarjeniyar NPT, kuma za’a yi mu’amala da shirin kamar sauran kasashen karkashin kula na hukumar IAEA. Tsahar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ma’aikatar na bada wannan sanarwan a safiyar Asabar ta kara da cewa dama kudurin na tsawon shekaru goma ne daga yau ta gama aiki. Daga yau shirin Nukliyar JMI zai ci gab aba tare da wani karin ka’idojin...
    Kauyukan kasar Iran guda uku,  Soheili a kan tsibirin  Qeshm, da Kandelous a lardin Mazandaran, da kuma  Shafiabad a lardin Kerman na kasar Iran sun shiga cikin zababbun  kauyuka a duniya na yawon shekatawa saboda kyauwunsu da kuma samar da dukkan abin kyautata rayuwa a cikinsu. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto mataimakin ministan al-adu na kasar Iran yana bada wannan sanarwan a jiya Jumma’a. Anoushirvan Mohseni-Bandpei, ya kara da cewa zabar wadan nan kauyuka na kasar Iran cikin kyauyuka wadanda suka cancanci shiga wuraren yawon shakatawa a duniya wanda hukumar  ‘ The United Nations World Tourism Organization (UNWTO), ta yi zai bunkasa yawon shakatawa a kasar Iran , kuma ma’aikatarsa tana aiki dare da rana don...
    Mataimakin shugaban kasa na farko a nan kasar Iran Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa JMI, kofarta a bude ga tattaunawa da dukkan kasashen duniya in banda HKI. Ya ce mun tattauna hatta da Amurka amma sai suka farmana da yaki a tsakiyar tattaunawar. Don haka Iran tana tattaunawa da dukkan kasashen duniya, sai dai ba zata amince da bukatun da ba zai yu amince da su ba. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar  Iran ya nakalto mataimakin shugaban kasar yana fadar haka a jiya Jumma’a a lokacinda yake ganawa da masu masana’antu a kasar a nan Tehran, ya kara da cewa gwamnatin Amurka ta bukaci tattaunawa da Iran amma tare da sharadin ta amince da bukatarta kafin a fara...
    Tashar talabijin ta CNN ta bayar da rahoton cewa, Janar Alvin Holsey, kwamandan rundunar sojin Amurka ta Kudu, ya yanke shawarar yin murabus nan da watan Disamba, saboda takun-saka tsakaninsa da sakataren tsaron Pete Hegseth, kan rashin jituwar da aka samu game da batun ayyukan sojojin Amurka a yankin Caribbean. Rahoton ya bayyana cewa, a makwannin da suka gabata ne Janar Holsey ya bayyana damuwarsa kan sahihancin wadannan ayyuka, yayin da Hegseth ya nuna takaicinsa kan yadda ayyukan ke tafiyar hawainiya, lamarin da ya janyo cece-kuce tsakanin bangarorin biyu. A cewar rahoton, manyan jami’an biyu sun tayar da jijiyoyin wuya ne a  yayin wani taro a ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon a makon da ya gabata, inda suka yi musayar...
    Tawagar sun gabatar da kansu ga babban sakataren hukumar gudanarwar ci gaban Jihar Katsina, Dakta Mustapha Shehu. Tawagar sun ce ziyarar wani bangare ne na shirye-shiryen gudanar da aikace-aikace domin inganta zaman lafiya da kuma sanar da tallafin jin kai ga ‘yan gudun hijira.   Gwamnan Katsina ya yaba wa Bankin Duniya da ya yi hadin gwiwa da Jihar Katsina don fuskantar matsalolin tsaro da kuma tallafa wa ‘yan gudun hijira. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja October 17, 2025 Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu...
    Shugaban ya kara da cewa, aana sa ran aikin za a fara gudanar da shi ne, a zangon farko na shekarar 2026.   Ya ci gaba da cewa, aikin na yiwa wadannan Tashoshin garanbawul, na daga cikin kudurorin Gwamnatin Tarayya na zamantar da Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa, musamman ta hanyar samar da kayan aiki na zamia da kuma ci gaba da janyo hankalin masu son zuba hannun jari zuwa ga fannin, wanda hakan zai kuma kara sanya gasa a cikin wadanda suke a cikin fannin.   Ya bayyana cewa, masu son zuba hannun jari a fannin suna ci gaba da nuna shawarsau, musamman saboda sauye-sauyen da Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinbu ta kirkiro da su, a fannin kara...
    An rantsar da Kanal Michael Randrianirina a matsayin sabon shugaban gwamnatin sojin Madagascar, bayan ya jagoranci hamɓarar da shugaba Andry Rajoelina. Sabon shugaban Madagascar kuma ya jaddada cewa hawan sa, ba juyin mulki ba ne, domin ya samu goyon bayan kotun tsarin mulkin ƙasar. Gwamnonin APC sun yi taro a Jihar Kebbi ’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe Bayan ya sha rantsuwar kama aiki Kanal Randrianirina ya ce abubuwan da zai fi bai wa fifiko sun haɗa da ruwan sha da abinci da kuma kafa gwamnati. Tsohon shugaban Ƙasar Rajoelina wanda ’yan majalisar ƙasar suka tsige bayan tserewarsa waje a ƙarshen makon jiya, ya yi Allah wadai da juyin mulki kuma yaƙi amincewa da murabus duk da baya cikin...
    Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar da tarwatsa wasu muhimman wurare 21 na ‘yan sahayoniyya a lokacin yakin 12 Kwamandan Dakarun sa-kai na Basij Birgediya Janar Gholamridha Sulaimani ya bayyana cewa: Tunanin kawar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran a cikin yakin kwanaki 12 da aka yi, wauta ce ta makiya yahudawan sahayoniyya, wadanda suka gaza a yunkurin da suka yi. Ya jaddada cewa: Iran ta lalata muhimman wurare 21 na ‘yan sahayoniyya da makamanta masu linzami a yakin karshe. Birgediya Janar Gholamreza Soleimani ya bayyana a wurin taron tunawa da shahidai a Isfahan cewa: Makiya sun yi tunanin cewa za su iya kawar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran nan da kwanaki 10, kuma sun yi niyyar haifar da hargitsi da...
    Abokan Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya sun bayyana cewa: Sake dawo da takunkumi bayan karewarsa baya da wani tushe na doka ko tsari Kungiyar aminan Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wata sanarwa game da cikar kudiri mai lamba 2231 kan yarjejeniyar makamashin nukiliyar Iran a ranar 18 ga watan Oktoba, inda ta bayyana cewa matakin da Amurka da Turai suka dauka na sake daukar matakin kakaba takunkumin da ya kare kan wata kasa tsari ne da baya ya kan wani tushe na doka ko yarjejeniyar kasa da kasa. Kungiyar aminan Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wata sanarwa a ranar Alhamis da ke nuna cikar kuduri mai lamba 2231 na kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya...
    Kasar Iran ta yi Allah wadai da harin wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka kai kan yankin kudancin kasar Lebanon Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya yi Allah wadai da hare-haren da yahudawan sahayoniyya suka kai a wurare da dama a kudancin kasar Lebanon. Ya jaddada cewa, sun biyo bayan yadda aka ci gaba da yin sassauci da rashin daukar nauyin masu daukar nauyin yarjejeniyar tsagaita bude wuta – Faransa da Amurka – yana mai nuni da alhakin kai tsaye da ke kan kasashen biyu a wannan fanni. A cikin wata sanarwa da ya fitar, Baqa’i ya dauki hare-haren da yahudawan sahayoniyya suka kai a jiya da rana da kuma dare kan wasu wurare a kudancin...
    Kungiyar Hamas ta yi kira ga masu shiga tsakani da su matsa wa haramtacciyar kasar Isra’ila lamba kan aiwatar da sharuddan yarjejeniyar Gaza Kungiyar Hamas ta yi kira ga masu shiga tsakani da su ci gaba da taka rawa wajen bin diddigin aiwatar da sauran tanade-tanaden yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, musamman ma wadanda suka shafi shigar da adadin taimakon da ake bukata. A cikin wata sanarwa da ta fitar, kungiyar ta jaddada bukatar gaggauta fara kafa kwamitin tallafawa al’umma domin fara gudanar da ayyukansa na gudanar da harkokin yankin zirin Gaza. Kungiyar Hamas ta bayyana jin dadin ta ga kokarin da masu shiga tsakani a Masar, Qatar, da Turkiyya suka yi na cimma yarjejeniyar dakatar da yakin wuce...
    Majalisar Zartarwar Jihar Jigawa ta amince da wasu manyan kwangiloli da kudinsu ya haura Naira Biliyan 6, domin karfafa bangarorin noma, ilimi da ci gaban tattalin arziki a fadin jihar. A cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai bayan zaman majalisar da aka gudanar a fadar gwamnatin Dutse, kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna kudirin gwamnatin jihar wajen inganta muhimman bangarori da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar al’umma. A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2 domin sayen babura nau’in Hunter guda 1,180 ga malaman gona a fadin jihar. Ya ce wannan mataki ya yi daidai da kokarin Gwamna...
    A taron majalsar zartarwar, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa zabinsa na Amupitan ya yi ta’allaka ne a kan rashin nuna son kai na siyasa, gaskiya da kyakkyawan tarihinsa.   Mambobin majalisar, ciki har da shugabanni na yanzu da na baya, sun amince da nadin, suna bayyana Farfesa Amupitan a matsayin mutum mai gaskiya. Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya ce tarihin Amupitan na ciki da kwazo da adalci da kwarewa da hidimar kasa.   Bayan amincewar majalisar, ana sa ran shugaba zai mika sunan Amupitan zuwa majalisar dattawa don tantancewa da tabbatarwa bisa ga tsarin kundin mulkin Nijeriya.   Farfesa Amupitan, mai shekaru 58, dan asalin kauyen Ayetoro Gbede a cikin karamar hukumar Ijumu ta Jihar Kogi. Ya...
    Dantsoho ya sanar da haka ne, bayan kaddamar dashi a matsayin Mataimakin Shugaban Kungiyar a kwanan baya a wani taro kan harkokin Tashoshin Jiragen Ruwa na duniya da aka gudanar.   Kazalika, Dantsoho ya ci gaba da cewa, zai mayar da hankali ne, kan wanzar da tsarin da NPA, ta sanya a gaba da kara karfafa hadaka, musaman domin a habaka samar da sauki a fannin gudanar da hada-hadar Tashohin Jiragen Ruwa da ke a Afrika ta Yamma.   Idan za a iya tunawa, harkar gudanar da Tashoshin Jiragen Ruwa na Afrika ta Yamma na fuskantar kalubale da suka hada da, yin aiki da kayan da suka dade da rashin samar da dawamammen tsari da kuma rashin rungumar yin aiki...
    Rahotanni sun bayyana cewa shakih Naim Qassim babban sakatare janar din hizbullah na kasar labanon ya bayyana a jiya Alhamis a gaban mambobin kungiyar Kashafat Al-Mahadi cewa Amerika da Isra’ila ba za su iya yin galaba akan hizbullah ba, Babban hadafin kafa wannan kungiyar shi ne kokarin wayar da kan yara matasa yan shekara 6 zuwa 18 muhimman alamuran addini, adaidai lokacin da gwamntin sahyuniya take ta kokari wajen yada akidar sahyuniyanci tsakanin yara matasa, kungiyar tana taka muhimmiyar rawa wajen yada akidar gwagwarmaya ga matasa masu tasowa inda yanzu haka tana da mambobin fiye da 100,000. Shaikh Naim Qaseem ya bayyana muhimmancin wannan kungiyar kuma ya bayyana cewa samuwar wadannan matasa zai kara taimakawa wajen tunkarar dukkan kalubalen dake...
      Manyan malamai, shugabanni na addini, gargajiya da siyasa daga sassan Arewacin Najeriya sun hallara a Kaduna domin Taron Musamman na Malaman Arewa (Special Northern Ulamah Summit), wanda ya mayar da hankali kan nemo mafita ta dindindin ga matsalolin tsaro da ƙalubalen tattalin arziki da ke addabar yankin.   Taron ya tattauna kan ƙarfafa haɗin kai tsakanin malamai, amfani da kafafen sada zumunta ta hanyar da ta dace, da kuma ƙarfafa hulɗa tsakanin shugabannin addini, gargajiya da na siyasa domin dawo da zaman lafiya da daidaito a al’umma.   Da yake jawabi, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar na Uku, wanda Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli ya wakilta, ya kira malamai da shugabanni su haɗa kai wajen...
    Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya.   A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun...
    Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya.   A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun...
    Kasar Saudiyya ta rage yawan guraben kujerun aikin hajjin da take ware wa Najeriya daga 95,000 zuwa 66,910 daga shekarar 2026. Aminiya ta ruwaito cewa a baya Najeriya ta shafe tsawon shekaru uku tana samun guraben na 95,000 a yayin Aikin Hajjin. ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi A cewar Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), wannan sauyi ya biyo bayan gazawar Najeriya wajen cika guraben da aka ware mata a hajjin shekarun 2024 da 2025. Wata sanarwa da, Mataimakiyar Darakta a Sashen Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara, ta sanya wa hannu, ta ce hakan na nufin za...
    A yammacin jiya Alhamis ne sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya gana da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin a birnin Moscow inda ya isar da sakon jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ga shugaban na Rasha. Bangarorin biyu sun tattauna batutuwa da dama da suka hada da huldar dake tsakanin kasashen biyu, da hadin gwiwar tattalin arziki, da ci gaban yankin, da kuma sauran batutuwa na kasa da kasa. A makon da ya gabata, Putin ya ce mahukuntan Isra’ila sun bukaci ya isar da sako ga Iran cewa ba su niyar sake kaddamar da wani hari a kan kasar ta Iran. “Muna ci gaba da samun sakonni daga jagorancin Isra’ila suna neman...
    A yammacin jiya Alhamis ne sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya gana da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin a birnin Moscow inda ya isar da sakon jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ga shugaban na Rasha. Bangarorin biyu sun tattauna batutuwa da dama da suka hada da huldar dake tsakanin kasashen biyu, da hadin gwiwar tattalin arziki, da ci gaban yankin, da kuma sauran batutuwa na kasa da kasa. A makon da ya gabata, Putin ya ce mahukuntan Isra’ila sun bukaci ya isar da sako ga Iran cewa ba su niyar sake kaddamar da wani hari a kan kasar ta Iran. “Muna ci gaba da samun sakonni daga jagorancin Isra’ila suna neman...
    Hakazalika, ta bai wa mata 30 masu kananan sana’o’i tallafin buhun gawayi, da kilo 10 na Shinkafa da litar man girki.   Bugu da kari, ga kungiyoyi shida na mata manoma, kowacce za ta karɓi fanfunan feshi, famfun ruwa, da kuma maganin feshin ciyawa.   Hajiya Shema’u, ta yaba da karuwar adadin mata a harkar noma, inda ta ce, manoma mata da suka yi rajista da NAWIA a yanzu sun haura 2000, yayin da wadanda ba su yi rajista ba sun kai 5,000.   Shemau ta kuma mika godiyarta ga Uwargidan gwamnan jihar Zamfara, Hajjiya Hurriya Dauda bisa namijin kokarin da take yi na bunkasa noman mata a Jihar Zamfara.   Sauran hukumomin da kungiyoyin da suke tare da NAWIA...
    Sashen kashe radadi domin gudanar da aikin tiyata ga marasa lafia na asibitin gwamnatin tarayya FMC da ke garin Birnin Kudu a jihar Jigawa ya gudanar da bikin ranar bada maganin radadi ta duniya ta bana. Kungiyar ma’aikatan bada maganin kashe radadi dan yin aikin tiyata ta Duniya ce ta kebe ranar 16 ga wata Oktobar kowacce shekara domin bikin wannan rana. Shekaru 170 ke nan da fara amfani da maganin kashe radadi, inda wasu likitoci su ka yi gwajin wannan magani a asibitin birnin Massachusetts na kasar Amurka, abin da ya kawo sauyi wajen yi wa marasa Lafia aikin tiyata daga shekara 1846. Malam Aliyu Umar Yusuf na sashen bada maganin kashe radadi na asibitin gwamnatin tarayya FMC...
    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta samu nasarar gano wasu motoci da aka sace tare da kama wasu da ake zargin ɓarayi ne masu aikata laifuka ciki har da ƙwace bindiga ƙirar gida. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a madadin Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Bello Yahaya, inda ya ce nasarorin sun biyo bayan sintiri da sahihan bayanan leƙen asiri da haɗin gwiwar al’umma. Miyetti Allah ta dakatar da shugabanninta a jihohi 3 An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi A cewar sanarwar, a ranar 13 ga Oktoba, 2025, jami’an sashin Balanga sun gano wata mota ƙirar Toyota Jeep...
    A Madagaska gobe Juma’a ne kotun tsarin mulkin kasar zata rantsar da Kanar Michael Randrianirina a matsayin shugaban kasa. Hakan na zuwa ne bayan majalisar dokokin kasar ta tsige shugaban kasar Andry Rajoelina bayan ya tsere daga kasar sanadiyyar zanga zangar data rikide zuwa bore wa gwamnatinsa saboda matsalar wutar lantarki da ruwan sha. Tunda farko dai kanar Randrianirina ya kiyasta zai rike mulki na wa’adin watanni 18 zuwa 24 lokacin da za’a kai ga gudanar da zaben raba gardama na kundin tsarin mulkin kasar. Saidai kotun tsarin mulkin kasar ta sanar da cewa, ya kamata a gudanar da zaben sabon shugaban kasa cikin kwanaki 60. Tuni Tarayyar Afirka (AU) ta dakatar da kasar ta Madagascar daga kungiyar bayan juyin...
    Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya amsa wasika daga daukacin malamai da daliban jami’ar nazarin aikin gona ta kasar Sin, inda ya taya dukkan malamai da dalibai da ma’aikatan jami’ar, da kuma wadanda suka kammala karatu a jami’ar murnar cika shekaru 120 da kafuwar jami’ar. Xi ya yi fatan jami’ar za ta ci gaba da tafiyar da harkokinta yadda ya kamata, da kudurce aniyar inganta aikin gona don amfanin kasa, da kuma zurfafa yin gyare-gyare kan hanyoyin koyarwa da ilmantarwa, da kara kokarin bincike, da kirkire-kirkire a fannin aikin gona, da kuma amfani da sakamakon binciken yadda ya kamata, ta yadda za a kai ga horar da karin kwararrun masana a fannin aikin gona, don ba da sabuwar gudummawa ga...
    Shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa a koda yaushe makiya suna neman haifar da rikici tsakanin kasashen musulmi domin raunana su, yana mai nuni da barkewar tashin hankali tsakanin Pakistan da Afghanistan. Mr. Pezeshkian ya bayyana haka ne a yayin wani taro inda ya fayyace matsayin kasar Iran dangane da takun saka tsakanin kasashen musulmi a gabashin kasar Iran. Shugaban ya kara da cewa rikicin baya-bayan nan tsakanin Afghanistan da Pakistan ya haifar da damuwa sosai a tsakanin dukkanin kasashen yankin ciki har da Iran da ke da iyaka da kasashen biyu. Ya kara da cewa, Iran za ta yi iyakacin kokarinta na ganin an rage zaman dar-dar, da inganta tattaunawa, da karfafa dankon zumunci a tsakanin...
    Wata kungiyar kare hakkin bil’adama ta Euro-med mai hedkwata a Geneva ta yi kira ga kasashen duniya da su tabbatar da shiga Gaza ba tare da ‘yan jarida, masu bincike, da masana harkokin shari’a don tattara bayanan kisan kiyashin da Isra’ila a Gaza da kuma hukunta wadanda suka aikata laifin. A cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na X, Hukumar ta ce, biyo bayan yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a Masar ranar Litinin, “Dole ne duniya ta ga abinda ya kasance a Gaza.” Kungiyar ta ce a yanzu dole ne a bar duniya ta ga irin barnar da aka yi, wa matsugunai, da kuma haddassa wahalhalun ga bil adama sanadin yakin da Isra’ila ta yi na...
    Ƙungiyar kare muradun Fulani makiyaya ta Miyetti Allah Kautal Hore ta ayyana dakatar da wasu jagororinta daga muƙamin shugabanci a jihohi uku da ke yankin Arewacin ƙasar nan. A wata sanarwa ɗauke da sa hannun sakataren hulɗa da jama’a na ƙungiyar na ƙasa ,Ambasada Muhammad Tasiu Sulaiman da aka bayyanawa manema labarai a ranar Alhamis. An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC Ƙungiyar ta ce dakatarwar ya shafi shuganta a Jihar Adamawa Usman Abubakar Yirlabe da na jihar Taraba, Banmi Bello Jane, sai na Jihar Bauchi Muhammad Hussaini Buzaye. Sanarwar ta ƙara da cewa, matakin dakatar da shugabnnin uku ya biyo bayan wasu ƙorafe-ƙorafe ne daga...
    Gwamnatin Jihar Kano ta ce nan ba da jimawa ba za a fara ƙera fanel da sauran kayayyakin samar da wutar lantarki daga hasken ranar a jihar. Hakan a cewar gwamnatin ya biyo bayan samun masu zuba jari a fannin na makamashi, bayan rattaba hannu kan yarjejeniya da kamfanoni biyu da suka shahara a fannin, wato Tricell Solar Solutions da IRS Green Energy.. ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano Ka da a ɗora wa Tinubu laifin rikicin da ke faruwa a PDP — Fayose An kulla yarjejeniyar ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Wutar Lantarki ta Karkara (REA) domin bayar da shawarwari na fasaha da daidaita ayyuka, a yayin taron Sabunta Makamashi na...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi a jawabin da ya gabatar a taron tsakiyar shekara ta ministocin harkokin wajen kungiyar yan ba ruwammu wato NAM a birnin Kampala babban birnin kasar Uganda a jiya Laraba, ya jadda bukatar hadin kai da goyon baya a tsakanin kasashen kungiyar, wajen fuskantar rashin mutunta dokokin kasa da kasa da kuma nuna iko na bangare guda. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Araqchi yana cewa yana daga cikin manufofin kafa kungiyar NAMA tabbatar da yencin ko wace kasa a duniya. Don haka akwai bukatar nuna wannan a aikace. Dangane da yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar Iran a cikin watan yunin da ya gabata, Aragchi...
    Ma’aikatar masana’antu da ma’adinai ta kasar Iran ta bayyana cewa na sami karin ci gaba a yawan karfen da kasar ke sayarwa ga kasashen waje a rabin farko na wannan shekara ta 2025 zuwa dalar Amurka billion $4. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa duk tare da takunkuman tattalin arzikin da kasashen yamma suka dorawa kasar ta bunkasa amfani da karfe ko a cikin gida sannan da wasu dabarbarun don saida su ga kasashen duniya. Labarin ya kara da cewa yawan karshen da ake samarwa a cikin gida ya karo da kasha 34% a cikin watanni 6 da suka gabata na wannan shekara ta 2025, sannan yawan karfen da iran take satarwa zuwa kasashen wajen ya...
    Baba-Ahmed, ya bayyana cewa, abin da danginsa suka fuskanta a hannun masu garkuwa da mutane a bara ya tabbatar masa da cewa rashin tsaro a yanzu yana da nasaba da siyasa. Ya kuma danganta kisan jama’ar da aka yi wa mabiya Shi’a a Zariya a shekarar 2015 da wani shiri na gwamnati don murƙushe masu sukarsu a wancan lokaci. Ya jaddada cewa El-Rufai da jam’iyyar APC ba za su iya tserewa daga alhakin halin da Nijeriya ke ciki na rashin tsaro ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato October 16, 2025 Manyan Labarai Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson October...
    Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya ce bai dace a ɗora wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, laifin rikicin da jam’iyyar PDP ke fama da shi ba. Ya bayyana haka ne yayin hira da gidan talabijin na Channels a ranar Laraba, inda ya ce shugabannin PDP ne suka haddasa matsalolinsu, ba Tinubu ko jam’iyyar APC ba. Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi NAJERIYA A YAU: Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a A cewarsa, jam’iyyar PDP “ta mutu tun tuni,” kuma ba ya cikin waɗanda za su nemi farfaɗo da ita. Ya ƙara da cewa yawancin gwamnonin da suka rage a PDP na shirin komawa jam’iyyar APC mai mulki. “Ba daidai...