Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya
Published: 21st, October 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta amince a soma binciken yadda aka yi amfani da tallafin ƙetare da ya kai dala biliyan 4.6 da Nijeriya ta karɓa daga shekarar 2021 zuwa 2025, domin yaƙi da cututtukan HIV/AIDS, tarin fuka (TB), da zazzabin cizon sauro (maleriya).
Wannan na zuwa ne bayan ƙudirin da Honarabul Philip Agbese daga Jihar Benuwe ya gabatar a yayin zaman majalisar na ranar Talata.
Agbese ya bayyana cewa Nijeriya ta karɓi kusan dala biliyan 1.8 daga Global Fund da kuma dala biliyan 2.8 daga Hukumar Raya Kasashe ta Amurka (USAID) a tsakanin 2021–2025, sai kuma sama da dala biliyan 6 daga shirin tallafin Amurka na PEPFAR domin tallafa wa tsarin kiwon lafiya da yaƙi da cututtuka.
Sai dai ya bayyana damuwa cewa duk da wannan gagarumar gudunmawa, har yanzu Najeriya na daga cikin ƙasashen da suka fi fama da cutar HIV da tarin fuka da maleriya a duniya.
Ɗan majalisar ya yi gargadin cewa, muddin ba a dauki mataki ba, Najeriya na iya gaza cimma muradin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta sanya a ƙarƙashin manufofinta na kawo ƙarshen cututtukan HIV, tarin fuka, da zazzabin cizon sauro nan da shekarar 2030.
Dangane da hakan ne majalisar ta umurci Kwamitin Kiwon Lafiya, HIV/AIDS, TB da Malaria ya binciki yadda aka kashe kuɗaɗen, tare da kawo mata cikakken rahoto nan da makonni hudu.
Haka kuma, ta buƙaci Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, da ya gabatar da cikakken tsarin aiwatar da tallafin da majalisa ta amince da shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Tarin Fuka Zazzabin Maleriya dala biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaron kasar
Majalisar Dattawa a najeriya ta amince da tsohon hafsan sojin
kasa, Janar Christopher Musa (mai ritaya), a matsayin sabon Ministan Tsaro bayan tantance shi da aka dauki kusan awanni biyar.
A lokacin tantancewar, Musa ya ce zai inganta tsaro ta hanyar hada kai tsakanin sojoji, ’yan sanda, sauran hukumomin tsaro da al’ummomi.
Ya yi gargaɗin cewa ’yan ta’adda na kai hare-hare a Nijeriya ne saboda suna ganin kasar tana da arziki, Ya kuma yi alkawarin magance gibin tsaro da aka samu da kuma kara hadin gwiwa da kasashen makwabta.
Ya yi nuni da cewa sojoji kadai ba za su iya magance matsalar tsaro ba, ya jaddada bukatar kyakkyawar gwamnati da goyon bayan al’umma.
Sanatoci sun yaba da kwarewarsa kuma suka amince da shi baki daya. Musa zai jagoranci harkokin tsaro a Nijeriya yayin da ake ci gaba da fama da hare-haren ta’addanci, satar mutane da kuma hare-haren ’yan bindiga.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka December 3, 2025 MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI December 3, 2025 An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran December 3, 2025 Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci December 3, 2025 Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci