ISWAP: Mun kawar da duk wata barazana — Gwamnatin Ondo
Published: 23rd, October 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Ondo ta roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu bayan gargaɗin da Hukumar Tsaro ta DSS, ta yi na cewar wasu mayaƙan ISWAP na shirin kai hari wasu sassan jihar.
A cikin wata sanarwa, Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Mista Idowu Ajanaku, ya bayyana cewa irin waɗannan rahotanni abu ne na yau da kullum a harkokin tsaro.
Ya ce hukumomin tsaro suna yawan musayar bayanai irin waɗannan domin daƙile duk wata barazana.
Ajanaku, ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati tare da hukumomin tsaro sun ɗauki matakai don kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.
“Gwamnati da hukumomin tsaro suna kan lamarin kuma suna ɗaukar duk matakan da suka dace don tabbatar da cewa Jihar Ondo ta kasance cikin aminci,” in ji sanarwar.
Ya kuma roƙi mazauna jihar da su kwantar da hankalinsu, su ci gaba da ayyukansu na yau da kullum, sannan su riƙa sanar da hukumomin tsaro idan suka ga wani abun zargi.
Kwamishinan ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta mayar da hankali sosai kan yankunan da ke iyakar wasu jihohi don kawar da kowace irin barazana.
“Don Allah kada ku firgita, kada kuma ku ɗauki doka a hannunku. Ku haɗa kai da gwamnati da hukumomin tsaro domin mu ci gaba da tabbatar da tsaron jiharmu,” in ji Ajanaku.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barazana hari ISWAP da hukumomin tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
Daga Usman Muhammad Zaria
Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jihar Jigawa ta yi kiyasin kashe kudade miliyan dubu 161 da milyan 336 domin gudanar da ayyukan hanyoyin mota da harkokin yau da kullum a sabuwar shekara ta 2026.
Babban sakataren ma’aikatar, Malam Ahmad Isah, ya bayyana haka lokacin da ya ke kare kiyasin kasafin kudin ma’aikatar a gaban kwamatin ayyuka da sufuri na majalisar dokokin jihar Jigawa.
Babban Sakataren ya yi bayanin cewar, za a yi amfani da mafi yawan kudaden ne wajen gudanar da ayyukan hanyoyin mota tsakanin gariruwa da hanyoyin burji da kuma titunan cikin gari.
Yana mai cewar, haka kuma za a gudanar da ayyukan hanyoyi a manyan makarantun jihar ciki har Jami’ar Sule Lamido da ke Kafin Hausa da kwalejin fasaha da ke Dutse da cibiyar binciken aikin gona ta Kazaure, da kwalejin koyon aikin lafiya matakin farko da ke Jahun da sauransu.
Sai dai kuma babban sakataren ya koka dangane da bukatar daukar injiniyoyi domin aiki a ma’aikatar da hukumar gyaran hanyoyin mota JIRMA da kuma daukar sabbin jami’an duba lafiyar ababen hawa wato V.I.O, idan aka yi la’akari da karancin ma’aikata saboda masu yin ritaya.
Alhaji Ahmad Isah ya kara da cewar ma’aikatar tana kokarin cimma yarjajjeniya da makarantar koyon tukin jirgin sama ta kasa da ke Zaria domin amfani da filin jirgin sama na Dutse a matsayin sansanin koyon tukin jirgin sama.
Kazalika, ya ce makarantar koyon tukun mota da ke karamar hukumar Birnin Kudu za ta amfana da wasu ayyuka a sabuwar shekara.
A nasa jawabin, shugaban kwamatin ayyuka da sufuri na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Bulangu Alhaji Yusuf Ahmad Soja, ya yi addu’ar Allah Ya sa kasafin kudin ya karfafa cigaban jihar nan a sabuwar shekara.