Cutar karnuka: An ƙaddamar da riga-kafin karnuka 2,500 a Gombe
Published: 23rd, October 2025 GMT
Ma’aikatar Raya Kiwo ta Tarayya ta ƙaddamar da yunƙurin ƙasa baki ɗaya na yin rigakafi kyauta ga karnuka da maguna domin yaƙar cutar haukan kare inda Jihar Gombe ke shirin yin riga-kafi ga karnuka 2,500 a matakin farko.
Da take jawabi yayin bikin ƙaddamarwar da aka gudanar a Gombe, Babbar Sakatariya na Ma’aikatar, Dokta Chinyere Akujobi wadda Mataimakiyar Darakta, Dokta Salome Bawa ta wakilta ta bayyana cewa cutar haukan kare na ci gaba da hallaka dubban mutane a duk shekara a faɗin duniya, musamman a nahiyoyin Afirka da Asiya.
Ta ce, mafi yawan waɗanda ke mutuwa sakamakon cutar yara ne ’yan ƙasa da shekara 15, wanda hakan ke nuna cewa haukan kare ba wai matsalar lafiya kaɗai bace, matsala ce ta zamantakewa da ke shafar iyalai da al’umma baki ɗaya.
Dokta Bawa ta bayyana cewa, haukan kare cuta ce da za a iya kauce mata gaba ɗaya ta hanyar yin riga-kafi ga karnuka da maguna waɗanda su ne manyan hanyoyin yaɗa cutar ga mutane.
Ta ce, daga cikin allurai 26,000 na riga-kafin haukan kare da aka tanada a wannan matakin na farko, Jihar Gombe ta samu allurai 2,500, waɗanda idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, za su taimaka wajen rage yaɗuwar cutar a jihar.
A nasa jawabin, Kwamishinan Noma da Kiwo na Jihar Gombe, Mista Barnabas Malle, ya bayyana cewa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na da cikakken ƙudiri na kare lafiyar dabbobi da namun gida daga cututtuka masu cutarwa.
Ya tunatar da cewa jihar ta taɓa yin riga-kafin shanu domin kare su daga cutar huhu (anthrax) a bara, tare da yin alƙawarin ci gaba da haɗa kai da Ma’aikatar Tarayya domin faɗaɗa shirye-shiryen kiwon lafiyan dabbobi.
Farfesa Grace Sabo Nok Kia daga Kungiyar War Against Rabies Foundation ta yaba da wannan shiri, amma ta buƙaci a samar da ƙarin allurai domin tabbatar da cewa kowanne kare da mage a jihar su samu riga-kafi.
Ta buƙaci likitocin dabbobi da su tabbatar da gaskiya da adalci wajen rarrabawa da yin amfani da riga-kafin yadda ya dace.
Haka kuma ta roƙi masu karnuka da su kai dabbobinsu cibiyoyin rigakafi, tana mai cewa kawar da cutar haukan kare na buƙatar haɗin kan kowa da kowa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Cutar karnuka haukan kare
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
Wasu magidanta a garin Malam-Sidi, da ke Ƙaramar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, sun yaba da aikin haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Gombe da UNICEF sula yi wajen rage matsalar ƙarancin abinci a tsakanin ƙananan yara.
Shirin, wanda ake kira PARSNIP, yana bai wa yara masu shekaru 6 zuwa 23 wani nau’in abinci na musamman mai suna SQ-LNS.
Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a BornoWannan abincin yana ɗauke da sinadarai 24 da ke taimakawa wajen kare yara daga rashin abinci mai gina jiki da kuma bunƙasa lafiyarsu wajen girma.
A ziyarar da manema labarai suka kai, iyaye mata sun bayyana yadda shirin ya taimaka musu.
Malama Hussaina Bappayo ta ce SQ-LNS “abinci ne mai tasiri” saboda yadda ya taimaka wa yaranta sun ƙara ƙarfi da girma sosai.
Hakazalika, Malama Asmau Tela, ta ce ’yarta, wadda ta sha fama da gudawa da wasu ƙananan cututtuka, yanzu ta samy lafiya tun da ta fara cin wannan abinci.
Saboda nasarar shirin, iyaye mata da yawa suna zuwa cibiyoyin lafiya don karɓar SQ-LNS ga yaransu.
Wasu sun ce hakan ya rage musu kuɗin magani saboda yara sun daina yawan yin rashin lafiya.
Sai dai sun roƙi gwamnati da UNICEF su ƙara yawan abincin, domin yanzu ana fama da ƙarancinsa saboda buƙatar ta ƙaru.
Wasu iyayen, sun ce abincin ya taimaka sosai wajen rage yawan yara masu fama d ƙarancin abinci mai gina jiki, amma sun yi gargaɗin cewa idan ba a samun abincin, yara da yawa za su shiga hatsari.
Philomena Irene daga UNICEF ta bayyana cewa daga 2023 zuwa 2025, yara 106,248 ne suka amfana da SQ-LNS a Jihar Gombe.
Ta kuma ce sama da mata 20,347 ne suka samu horo kan kula da lafiyar uwa da jarirai, ciki har da yadda ake amfani da MUAC wajen auna girman yara.