Ya ce tallafin da Shugaba Tinubu ya amince da shi ba rance ba ne, wani bangare ne na yunkurin gwamnati na cire shingen da ke hana ’yan kasuwa ci gaba.

 

Ya ƙara da cewa gwamnati ta kafa asusun Naira Biliyan 75 da sunan tallafin ga ƙananan masana’antu da yan kasuwa (MSME Intervention Fund), wanda ke bai wa ’yan kasuwa rancen har zuwa Naira miliyan 5 da kaso tara cikin ɗari (9%) a matsayin kudin ruwa, da kuma Naira biliyan 50 a ƙarƙashin shirin Shugaba kasa Bola Tinubu da ke bai wa ƙanana ’yan kasuwa tallafin kuɗi kyauta bisa wasu sharuɗɗa domin bunƙasa kasuwanci (Presidential Conditional Grant Scheme) da ke ba da tallafin Naira 50,000 ga ’yan kasuwa miliyan ɗaya a fadin kasar.

 

Haka kuma, gwamnatin ta samar da Asusun Tallafin Masana’antu daga Gwamnati (Manufacturers Fund) na Naira biliyan 75 don tallafa wa masana’antu wajen rage tsadar samar da kayayyaki da sufuri.

 

Mataimakin shugaban ƙasan ya ce sama da ’yan kasuwa 39,000 a jihar Katsina sun amfana da shirye-shiryen gwamnatin tarayya, inda aka raba Naira Biliyan 2.5 a matsayin tallafi da rance mai rangwame.

 

A ƙarƙashin shirin RAPID, Shettima ya ce ’yan kasuwa 23 daga yankunan karkara sun samu fiye da Naira Miliyan 112 don faɗaɗa kasuwancinsu. Ya kuma yaba wa Gwamna Dikko Raɗɗa bisa kafa KASEDA, yana mai cewa Katsina na zama cibiyar ci gaban masana’antu, noma, da kasuwancin yanar gizo a Arewacin Nijeriya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja October 22, 2025 Manyan Labarai Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki  October 22, 2025 Manyan Labarai Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe

Kotu ta yanke wa wani wanda ya yi wa wata yarinya ’yar shekara 12 fyaɗe hukuncin ɗaurin rai-da-rai a Ƙaramar Hukumar Guba ta Jihar Yobe.

Babbar Kotun Jihar Yobe da ke zaune a ƙaramar hukumar Gujba ta yanke wa mutumin mai shekaru 31 mai suna Ali Kwano.

An gurfanar da shi ne a kan zargin ya kai yarinyar cikin aji a ƙaramar makarantar sakandare ta je-ka-ka-dawo da ke garin Bumsa, inda ya yi lalata da ita da ƙarfi.

Ya yaudari yarinyar ce bayan ya gaya mata cewa ta jira shi a cikin aji bisa cewar zai sayi ƙosai.

Bayan da ta shiga ajin sai ya kama hannunta, ya rufe bakinta ya danne ta a ƙasa sannan ya yi lalata da ita da ƙarfi.

Ƙasashen waje na taimaka wa ’yan ta’adda a Najeriya —Sheikh Gumi ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano

Alƙaliyar da ke jagorantar shari’a, Mai Shari’a Amina Shehu, ta same shi da laifi, don haka ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai bisa ga sashe na 3 na dokar haramta cin zarafin mutane, ta Jihar Yobe ta Shekarar 2020.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Iran Da Pakisatan Sun Amince ِDa Dawoda Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi