Aminiya:
2025-12-05@14:35:59 GMT

NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU

Published: 20th, October 2025 GMT

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin makonni huɗu domin ta warware duk wata tankiya da ke tsakaninta da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da sauran ƙungiyoyin jami’o’i da na manyan makarantu.

Shugaban NLC, Kwamared Joe Ajaero, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin ganawa da ’yan jarida a Labour House da ke Abuja.

An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a Kano APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno

Ajaero ya ce, idan gwamnati ta gaza kammala tattaunawa da ƙungiyoyin cikin wa’adin da ta bayar, NLC ba za ta yi wata-wata ba wajen ɗaukar matakin da ya dace ta hanyar amfani da dukkan wani tanadi da doka ta yi.

Ya kuma bayyana cewa sun gano cewa wasu ƙungiyoyin haɗin gwiwa a ƙarƙashin NLC suna ganawa da jami’an gwamnati ba tare da izini ko umarni daga uwar ƙungiya ba, wanda shi ne dalilin da ya sa yarjejeniyoyi da dama ba a cika su ba.

Jawabin da Kwamared Ajaero ya yi na zuwa ne bayan taron da NLC ta yi da shugabannin ƙungiyoyin jami’o’i ciki har da ASUU, SSANU, NASU da NAAT.

A makon da ya gabata ne ASUU ta ayyana yajin aikin gargaɗi na makonni biyu, bayan ƙarewar wa’adin na kwanaki 14 da ta bai wa gwamnati, dangane da batutuwan da suka shafi walwala da jin daɗin ma’aikata, albashi, da aiwatar da yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin ASUU da gwamnatin tarayya tun a shekarar 2009.

Sai dai Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya ce bai kamata ASUU ta shiga yajin aiki ba, domin a cewar tattaunawa ta ta yi nisa, kuma gwamnati ta saki Naira biliyan 50 na kuɗaɗen alawus ɗin malaman jami’o’i, tare da ware Naira biliyan 150 a cikin Kasafin 2025 domin gyaran jami’o’in.

A yayin taron da NLC ta gudanar, Kwamared Ajaero ya jaddada cewa daga yanzu, ƙungiyar ƙwadago ko wata ƙungiya a ƙarƙashinta ba za ta sake ganawa da jami’an gwamnati ba tare da izini ba, musamman waɗanda ke da alhakin aiwatar da yarjejeniyoyin da ake sanya hannu a kai.

Ya kuma soki matakin da gwamnatin ta ɗauka na amfani da dokar “ba aiki, ba albashi” kan mambobin ASUU yana mai cewa:

“Mun yanke shawarar bai wa gwamnati wa’adin mako huɗu domin ta kammala dukkan tattaunawa a wannan bangare. Mun fara da ASUU, amma matsalolin sun wuce na ASUU kaɗai.

“Idan bayan mako huɗu ba a kammala komai ba, za mu kira taron gaggawa na ƙasa domin ɗaukar matakin gama-gari, wanda dukkan ma’aikata da ƙungiyoyi a faɗin ƙasa za su shiga ciki.”

Ya ƙara da cewa, “Zamanin sanya hannu kan yarjejeniyoyi da yi wa ƙungiyoyin da ke neman haƙƙinsu barazana ya ƙare.

“Wannan batu na ‘ba aiki, ba albashi’ daga yanzu zai zama ‘ba albashi, ba aiki’. Saboda mun gano cewa fiye da kashi 90 cikin 100 na yajin aikin da ake yi a ƙasar nan na faruwa ne saboda rashin cika ƙa’idar yarjejeniyoyi.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina

Wata gobara da ta tashi da safiyar Litinin ta kashe magidanci da matarsa da ’ya’yansa uku a unguwar Kofar Sauri da ke cikin garin Katsina.

Wadanda gobarar ta rutsa da su sun haɗa da Muhammad Habibu mai shekara 35, matarsa Fatima Muhammad, da ’ya’yansu uku; Khadija, Abubakar, da Aliyu, wadanda dukkansu suka ƙone har lahira.

Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro

Gobarar ta kuma lalata dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

An gano cewa Muhammad Habibu ma’aikaci ne na wucin gadi a hukumar ruwa ta jihar Katsina kafin rasuwarsa.

Kodayake ba a tabbatar da ainihin dalilin gobarar ba tukuna, mazauna yankin suna zargin ta faru ne sakamakon tashin wuta mai ƙarfi lokacin da aka dawo da lantarki a yankin.

An ce gobarar ta fara ne daga falon gidan sannan ta bazu cikin sauri zuwa sauran sassan gidan, yayin da iyalin ke tsaka da sharer barci.

Bayanai sun ce lokacin da suka fahimci hatsarin, wutar ta riga ta toshe dukkan hanyoyin fita.

Ɗan uwa ga waɗanda suka rasu, Kasim Aliyu, ya ce da misalin ƙarfe 3:00 na safe ya ji muryar wata mace daga nesa tana karanta kalmar shahada: “Innalillahi wa inna ilayhi raji’un.” Da farko ya ɗauka al’ada ce, sai da misalin ƙarfe 3:30 na safe ya fara jin akwai matsala.

Kasim ya ƙara da cewa: “Mai gidan ƙanina ne ubanmu ɗaya. Gobarar ta kama gidan da misalin ƙarfe 3:00 na safe. Na ji wani abu a lokacin amma ban gane ba sai da aka kira ni da misalin ƙarfe 4:00 na safe aka shaida min cewa ƙanina da iyalinsa gaba ɗaya sun mutu a gobarar. Allah ya jikan su.”

Shaidun gani da ido sun ce ƙoƙarin makwabta da masu taimakon gaggawa wajen kashe gobarar ya ci tura.

Sun yi korafin cewa jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Katsina sun iso daga baya amma zuwan nasu bai yi wani tasiri ba sosai.

Wani mazaunin yankin, Musa Hamza, ya ce: “Ina ganin lokacin da hukumar kashe gobara ta iso, mutanen cikin gidan sun riga sun mutu a gobarar. Amma zan iya cewa sun yi iya ƙoƙarinsu wajen kashe wutar, sai dai ba su samu nasarar ceto iyalin ba. Allah ya jikan su.”

Wani makwabci, Magaji Bala, ya yi korafi cewa mazauna yankin sau da yawa suna shafe kwanaki ba tare da lantarki ba, sai kuma tashin wuta mai ƙarfi ya jawo barna duk lokacin da aka dawo da wuta.

“Irin wannan lamari ya taɓa faruwa a wasu sassan garin Katsina. Kwanan nan ma kusan irin haka ya faru. Wannan ya sa dole mutane su yi taka-tsantsan,” in ji shi.

Da aka tuntubi Babban Jami’in Kashe Gobara na jihar Katsina, Rabe Audi Kurmuyal, ya tabbatar da cewa ma’aikatansa sun kashe gobarar, sabanin ikirarin da ake yi cewa sun iso daga baya.

Wasu mazauna sun dora laifin kan matsalar sauyin wuta da ake yawan samu daga kamfanin rarraba na shiyyar Kano (KEDCO), suna cewa yawan katsewa da dawowa da ƙarfin lantarki mai yawa na lalata kayan lantarki.

Sai dai kamfanin ya musanta zargin, inda ya ca ba zai yiwu a ce laifinsu ba ne, kasancewar gidan shi kadai ya kone a unguwar mai gidaje sama da 5,000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta