Leadership News Hausa:
2025-12-09@18:56:21 GMT

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Published: 24th, October 2025 GMT

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Bugu da kari, Han ya ce, zamanantar da aikin gona da raya yankunan karkara tana da matukar muhimmanci a cikin aikin zamanantarwa irin ta kasar Sin, saboda haka ya kamata a ba wannan bangare fifiko. Ya ce shawarwarin da kwamitin kolin JKS ya gabatar na jaddada bukatar mai da raya harkoki masu alaka da aikin gona da raya yankin karkara da kyautata rayuwar manoma, a matsayin abu mai matukar muhimmanci, da tabbatar da bunkasar birane da yankin karkara na bai daya, da kuma hanzarta wajen inganta karfin kasar a fannin raya aikin gona.

 

A yayin taron, direktan hukumar raya kasa da gyare-gyare ta kasar Sin, Mr. Zheng Shanjie ya bayyana cewa, “kirkira da habaka sabbin abubuwa” na nufin habakawa da karfafa sabbin masana’antu da masana’antun da za su bullo a nan gaba. A shekarar 2024, tattalin arzikin “sabbin abubuwa uku” (wato sabbin masana’antu da sabbin nau’o’in cinikayya da sabbin hanyoyin kasuwanci) na Sin ya kai kashi 18% cikin alkaluman GDP na kasar. Shawarar da kwamitin tsakiyar JKS ya gabatar game da shiri na 15 na ci gaban tattalin arziki da zamantakewa na shekaru biyar-biyar, ya yi kira da a kirkiro sabbin masana’antu masu muhimmanci, da gaggauta habaka gungun masana’antu masu muhimmanci kamar sabbin makamashi, sabbin kayayyakin aiki da bangaren harkokin sararin samaniya, da tattalin arzikin kasa, wanda zai haifar da kasuwanni da darajarsu za ta wuce Yuan tiriliyan 1. Kazalika shawarar ta yi kira da a shirya da wuri don kafa masana’antu na nan gaba, kamar ta fasahar lissafi ta quantum da kirkirar kayayyakin halitta da makamashin hydrogen da na nukiliya da hada kwakwalwar bil adam da na’ura da fasahar wayar hannu na zamani, da sauransu, wadanda za su zama sabbin hanyoyin habaka tattalin arziki. Wadannan masana’antu a shirye suke don kara karfi wajen kokarin habaka masana’antar fasaha a nan kasar Sin, a cikin shekaru 10 masu zuwa.

 

Ministan kula da cinikayya na kasar Sin Wang Wentao ya bayyana a yau Juma’a cewa, kasar za ta fadada bude kofarta ga kasashen waje yayin aiwatar da shirin raya kasa na shekaru 5, na 15.

 

Wang Wentao ta kara da cewa, tsakanin shekarar 2026 zuwa ta 2030, za a yi kokarin fadada ba da damar shiga kasuwa da bangarorin da za a kara bude wa kofa, a bangaren bayar da hidimomi. Ministan ya ce wadannan na cikin shawarwarin da kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya gabatar wajen tsara shirin na 15 dake da burin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin, wanda aka amince da shi yayin zama na 4 na kwamitin kolin da aka kammala jiya Alhamis.

 

A cewarsa, sauran manyan ayyuka sun hada da raya sabbin harkokin cinikayya da samar da karin hanyoyin zuba jari tsakanin Sin da kasa da kasa da kuma daukaka hadin gwiwar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. (Safiyah Ma, Amina Xu, Fa’iza Muhammad Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan October 24, 2025 Daga Birnin Sin Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15  October 24, 2025 Daga Birnin Sin Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu October 24, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki

Kungiyar Habbaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka – Ecowas – ta sanar da tura rundunar ko-ta-kwana domin taimaka wa sojojin Jamhuriyar Benin wajen kakkabe sojojin da suka yi yunkurin juyin mulki.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar da yammacin jiya Lahadi, ta ce “Shugaban Ecowas, bisa ga amincewar shugabannin kasashen kungiyar ya amince da tura dakarun ko-ta-kwana zuwa Jamhuriyar Benin nan take.

Dakarun sun kunshi sojoji daga kasashen Najeriya da Saliyo da Cote d’Ivoire da kuma Ghana. Kuma za su taimaka wa gwamnati da kuma dakarun Jamhuriyar Benin wajen kare martabar kundin tsarin mulki da na kasar ta Benin.”

Rahotanni daga jamhurriyar Benin na nuni da cewa an kama sojoji da dama bayan wani yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba , Mutanen da aka kama sun haɗa da waɗanda ake zargi da jagorantar yunƙurin juyin mulkin.

A wata sanarwa da ya yi a gidan talabijin, ministan harkokin cikin gidan kasar Alassane Seidou, ya bayyana cewa dakarun kasar sun yi nasarar dakile yunkurin bayan da sojoji suka bayyana a gidan talabijin na kasar suna ikirarin cewa sun tsige shugaba Talon.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025  Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki
  • Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara
  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila
  • Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21