Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447
Published: 22nd, October 2025 GMT
Sanarwar ta ce, “Domin rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta wajen samun kula da lafiya, gwamnatin Dauda Lawal ta ƙaddamar da wannan shiri na musamman domin tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi da ke buƙatar jinya.”
Shirin, wanda aka fara a watan Agusta 2023, ya riga ya isa ga marasa lafiya sama da 3,400 zuwa asibitoci daban-daban ta hanyar tsarin ‘tele-screening’, wanda ke bai wa ƙwararrun likitoci damar lura da marasa lafiya daga ƙauyuka da yankunan karkara cikin gundumomi 14 na jihar.
Bangarorin da aka kula da lafiya a zagaye na goman da suka haɗa da; mutum 1,659 marasa lafiya masu kumburin ciki da irin sa. Mutum 1,081 masu ciwon ido da aka yi wa tiyata. Mutum 118 marasa lafiya masu cutar VVF da aka yi wa tiyata.
Sanarwar ta bayyana cewa, wannan shiri ya zama wata nasara ga gwamnatin jihar wajen kai ingantacciyar kulawar lafiya ga jama’a, musamman a yankunan da ke da ƙarancin cibiyoyin jinya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: marasa lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro
Majalisar Dattawan Najeriya za ta tantance wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa a matsayin Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, a zamanta na yau Laraba.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga ofishin Shugaban Masu Rinjaye na majalisar, Opeyemi Bamidele.
Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan TsaroSanarwar ta ce majalisar ta karɓi buƙatar Shugaban Ƙasa Tinubu na tabbatar da wanda aka naɗa Ministan Tsaro.
Sanarwar ta ƙara da cewa za a karanta wasikar a gaban majalisar a ranar Laraba, sannan kuma za a ci gaba da tantance wanda aka naɗa nan take.
Opeyemi ya bayyana cewa majalisar ba za ta iya jinkirta irin wannan buƙata ba a wannan lokaci mai muhimmanci, domin ta shafi muhimman abubuwan da suka shafi ƙasar.
A ranar Talat ace Tinubu ya aike da sunan Christopher gaban majalisar domin amincewa bayan murabus din tsohon Ministan, Muhammad Bdaru Abubakar.
Kafin nadin nasa dai, Christopher shi ne tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya da Tinubu ya sauke tare da ragowar manyan hafsoshi a kwanakin baya.