Gwamantin Nijar ta ƙara albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikata
Published: 23rd, October 2025 GMT
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanar da yin ƙarin albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikata daga cfa 30,000 zuwa cfa 42,000, wanda ya yi daidai da naira 108,780 a Najeriya.
Wannan ƙarin albashi na daga cikin matakan gwamnatin domin inganta rayuwar ma’aikata da ƙarfafa su wajen gudanar da ayyukansu na yau da kullum, kamar yadda gwamnatin ta sanar.
Majalisar Ministocin gwamnatin ce ta ɗauki wannan mataki a taron da ta gudanar jiya Laraba, inda kuma minsitocin suka tattauna hanyoyin da za a tabbatar da cewa ƙarin albashin zai shafi dukkan ma’aikatan gwamnati ba tare da rarrabewa ba.
Wannan mataki ya zo ne bayan da gwamnatin ta lura da ƙaruwar farashin kayan abinci da sauran kayan masarufi a ƙasar.
Gwamnatin ta bayyana cewa wannan ƙarin albashi zai taimaka wajen rage wahalhalu da ma’aikata ke fuskanta, musamman wajen biyan bukatun yau da kullum kamar abinci, sufuri, da kuma ilimin yara.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: ketare ƙarin albashi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso
“Allah ya albarkace mu da shugaba mai tsoron Allah da kishin jama’a – mutum ne mai kaunar al’ummar jihar Kano da Nijeriya, kuma me aiki tukuru domin ganin ci gabansu,” in ji Yusuf.
Ya kuma jaddada kudirin sa na ciyar da jihar gaba bisa tsarin falsafar Kwankwasiyya, wanda ke jaddada hidima, rikon amana, da tallafawa.
A nasa jawabin, Kwankwaso ya bukaci ‘ya’yan jam’iyyar NNPP da na Kwankwasiyya na kasa baki daya da su ci gaba da hada kai da kuma jajircewa wajen ci gaban jam’iyyar.
Ya kuma mika godiyarsa ga shugaban NNPP na kasa Dr. Ajuji Ahmed, da sauran shugabannin jam’iyyar daga jihohi sama da 30, da masu biyayya da suka halarci bikin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA