Aminiya:
2025-12-06@05:34:42 GMT

Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi

Published: 21st, October 2025 GMT

Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya rattaba hannu kan dokar ƙirƙirar sabbin masarautu 13 wadda za ta ba da damar naɗin hakimai sama 111 a faɗin jihar.

Sabbin masarautun da gwamnan ya ƙirƙira sun haɗa da: Burra, Duguri, Dambam, Bununu, Lere, Darazo, Jama’a, Lame, Toro, Ari, Warji, Giade da kuma masarautar Gamawa.

Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi Fashewar tankar mai ta yi ajalin mutum 30 a Neja

Da yake jawabi a gidan gwamnati, Bala Mohammed ya gargadi masu son siyasantar da lamarin ko kawo cikas wajen aiwatar da dokokin, yana mai cewa hukumomin tsaro za su dauki matakin da ya dace.

“Ba za mu lamunci duk wanda zai yi ƙoƙarin tayar da hankali ko ya kawo rikici ba. Duk wanda aka kama yana ƙoƙarin ɓata tsarin nan, doka za ta yi aikinta,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa duk wani jami’in gwamnati ko shugaba na gargajiya da ya aikata abin da zai ƙalubalanci manufar dokar, za a ɗauki matakin ladabtarwa a kansa.

A nasa jawabin, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, Abubakar Y. Suleiman, ya bayyana cewa dokar ta samo asali ne daga tattaunawa mai faɗi da aka yi da masu ruwa da tsaki, ciki har da sarakuna, ƙungiyoyin farar hula, da masana.

Ya ce dokar ta tabbatar da muradin gwamnati wajen kusantar da mulki da ci gaba ga jama’a, tare da ƙarfafa harkokin masarautu da inganta ayyukan gwamnati a yankunan da ke buƙatar kulawa.

“Wannan doka ba iya faɗaɗa tsarin mulki za ta yi ba, domin kuwa za ta tabbatar da adalci da daidaito ga kowane yanki na Jihar Bauchi,” in ji Kakakin Majalisar.

Ya kuma sanya hannu kan dokar tsarin fansho ta ma’aikatan kananan hukumomi, tare da alƙawarin biyan bashin fansho da ladabtarwa da ake bin tsoffin ma’aikata.

Kazalika, gwamnan ya amince da Dokar Ƙarin Kasafin Kuɗi ta 2025, domin tabbatar da ci gaban ayyukan da ake aiwatarwa a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi masarautu

এছাড়াও পড়ুন:

Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi

Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna, ya rasa ransa bayan fada ya barke a lokacin bikin radin suna a ƙauyen Kwata da ke Karamar Hukumar Warji ta Jihar Bauchi.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da sa’insa ta barke tsakanin wasu matasa ta rikide ta zama fada, wanda ya bar Haruna cikin rashin hayyacinsa.

Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

“Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna na ƙauyen Kwata, Karamar Hukumar Warji, Jihar Bauchi, ya riga mu gidan gaskiya bayan rikici mai tsanani da ya barke a bikin radin suna a ranar 2 ga watan Disamba, 2025,” in ji Zagazola Makama, masani kan harkokin tsaro a yankin arewa maso gabas.

Ya kara da cewa rashin jituwa tsakanin wasu matasa a wajen bikin ta rikide zuwa fada, lamarin da ya bar wanda abin ya shafa ya suma nan take.

An ce an garzaya da Haruna zuwa Asibitin Gwamnati na Warji, amma ya rasu a yayin da ake masa jinya.

Da aka tuntubi mai magana da yawun ’yan sanda na jihar, Ahmed Wakili, ya ce yana cikin taro kuma ya yi alƙawarin dawowa da bayani, sai dai bai yi hakan ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi
  • Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaron kasar
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi