Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi
Published: 21st, October 2025 GMT
Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya rattaba hannu kan dokar ƙirƙirar sabbin masarautu 13 wadda za ta ba da damar naɗin hakimai sama 111 a faɗin jihar.
Sabbin masarautun da gwamnan ya ƙirƙira sun haɗa da: Burra, Duguri, Dambam, Bununu, Lere, Darazo, Jama’a, Lame, Toro, Ari, Warji, Giade da kuma masarautar Gamawa.
Da yake jawabi a gidan gwamnati, Bala Mohammed ya gargadi masu son siyasantar da lamarin ko kawo cikas wajen aiwatar da dokokin, yana mai cewa hukumomin tsaro za su dauki matakin da ya dace.
“Ba za mu lamunci duk wanda zai yi ƙoƙarin tayar da hankali ko ya kawo rikici ba. Duk wanda aka kama yana ƙoƙarin ɓata tsarin nan, doka za ta yi aikinta,” in ji gwamnan.
Ya ƙara da cewa duk wani jami’in gwamnati ko shugaba na gargajiya da ya aikata abin da zai ƙalubalanci manufar dokar, za a ɗauki matakin ladabtarwa a kansa.
A nasa jawabin, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, Abubakar Y. Suleiman, ya bayyana cewa dokar ta samo asali ne daga tattaunawa mai faɗi da aka yi da masu ruwa da tsaki, ciki har da sarakuna, ƙungiyoyin farar hula, da masana.
Ya ce dokar ta tabbatar da muradin gwamnati wajen kusantar da mulki da ci gaba ga jama’a, tare da ƙarfafa harkokin masarautu da inganta ayyukan gwamnati a yankunan da ke buƙatar kulawa.
“Wannan doka ba iya faɗaɗa tsarin mulki za ta yi ba, domin kuwa za ta tabbatar da adalci da daidaito ga kowane yanki na Jihar Bauchi,” in ji Kakakin Majalisar.
Ya kuma sanya hannu kan dokar tsarin fansho ta ma’aikatan kananan hukumomi, tare da alƙawarin biyan bashin fansho da ladabtarwa da ake bin tsoffin ma’aikata.
Kazalika, gwamnan ya amince da Dokar Ƙarin Kasafin Kuɗi ta 2025, domin tabbatar da ci gaban ayyukan da ake aiwatarwa a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi masarautu
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Hanya Akan Kudi Sama Da Naira Biliyan 4
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanyar Babban Sara zuwa Malam Bako zuwa Shabaru zuwa Kirgi zuwa Albasu, mai tsawon kilomita 28.2, a Karamar Hukumar Sule Tankarkar,wanda kudinsa ya kakaNaira Biliyan 4.47, a ci gaba da shirin Gwamnati da Jama’a.
Aikin hanyar zai hada fiye da kauyuka 60 tare da karfafa harkokin kasuwanci da zamantakewa a yankin.
Haka kuma, gwamnan ya bude sabuwar cibiyar kula da lafiya ta farko, da makarantar Tsangaya ta zamani, da kuma rukunin samar da ruwa a yankin.
Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin Gwamnati da Jama’a hanya ce ta karfafa gaskiya, bayyana ayyuka da kuma baiwa jama’a damar fadin ra’ayoyinsu.
“Mun zo ne mu nuna abin da muka cimma cikin shekara biyu, mu kuma saurari jama’a domin mu kara gyara inda ya kamata,” in ji shi, yana mai jaddada cewa hakikanin gwamnati ita ce wadda ke bautar al’umma.
Ya gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa gyare-gyaren da ke karfafa tattalin arzikin jihohi da kananan hukumomi, inda ya bayyana cewa Jihar Jigawa na daga cikin jihohi shida da aka zaba don fara shirin ciyar da dalibai na National Home-Grown School Feeding Programme da aka farfado da shi.
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya yaba da shirin, yana mai cewa ya zama abin koyi ga sauran jihohi wajen aiwatar da mulki tare da jama’a.
A nata jawabin, Minista a ma’aikatar Ilimi, Farfesa Suwaiba Said Ahmad, ta jinjinawa Gwamna Namadi bisa manyan ayyukan cigaba da ke canza rayuwar jama’a.
Usman Mohammed Zaria