Sheikh Qasim: Natanyahu Ya Zubar Da Jini Mai Yawa Amma Babu Lamuni Ga Amincin Isra’ila Nan Gaba
Published: 22nd, October 2025 GMT
Shugaban kungiyar Hizbullah Ta Kasar Lebanon Sheikh Na’em Qasim ya bayyana cewa, ya bayyana cewa Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu ya zubar da jinin mutanen yankin yammacin Asia da dama, amma wannan bai bashi lamunin cewa haramtacciyar kasar Isra’ila (HKI) zata zauna lafiya a yankin nan gaba ba.
Tashar tal;abijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban kungiyar yana fadar haka a jiya Talata a wani bikin kaddamar da littafi wanda yake bayyana ra’yin Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaie dangane da wakoki da kidekide.
Yace: Duk tare da zubar da jinin mutanen yankin a duk a lokacinda ya ga dama, Netanyahu ba zai ce yana da lamuni na zaman lafiya ga HKI a nan gab aba.
Sheikh Qassem ya bayyana cewa gwamnatin HKI ta kasa cimma manufarta ta mamayar kasar Lebanon, duk tare da taimakon da ta samu daga manya-manyan kasashen duniya don cimma wannan manufar.
Ya ce HKI bayan fara yakin tufanul Aksa a shekara ta 2023, ta fuskanci turjiya mai tsanani daga kungiyar Hizbullah a yakin da kungiyar ta shiga don tallafawa Gaza, ta kuma ga yadda kungiyar ta maida yakin ya zama mafi muni ga yake-yaken HKI a tarihin yankin. Kuma ta gamu da asarar sojoji da makamanta, musamman tankunan yakin mirkava. Har zuwa watan Nuwamba na shekarar da ta gabata, a lokacinda tanemi tsagaita wuta.
Sheikh Qassem ya yi gargadi da Amurka da kuma HKI kan shirinsu na Isra’ila babba, don kasar Lebanon ba zata kasance cikin shirinsu ba.
Kafin haka dai Natanyahu ya gabatar da shirin ‘Isra’ila babba’ wanda ya hada da kasashen Lebanon, Jordan, Siriya , Iraqi Masar da kuma Saudiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Aragchi Da Guterres Sun Tattauna Kan Gaza Da Rikicin Yemen Ta Wayar Tarho October 22, 2025 Rasha da Habasha sun tattauna kan karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu a fannin nukiliya October 22, 2025 Sayyed al-Houthi: Mun shirya dawowa fagen daga idan Isra’ila ta ci gaba da kisan kiyashi a Gaza October 22, 2025 Nigeria: “Yan Sanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Neman Sakin Jagoran ‘Yan Awaren Biafara October 21, 2025 HKI Tana Ci Gaba Da Hana Wa Falasdinawa Abinci October 21, 2025 An Yi Fashi Da Makami A Gidan Adana Kayan Tarihin ” Louvre” Na Kasar Faransa October 21, 2025 Yemen : An yi jana’izar babban hafsan sojin kasar Shahid al-Ghamari a Sana’a October 21, 2025 Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza October 21, 2025 Equatorial Guinea ta zargi Faransa da karan-tsaye wa zaman lafiya a kasar October 21, 2025 Faransa : Sarkozy, ya fara zaman gidan yari na shekara 5 October 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza
Kasashen Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a Gaza
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da mai baiwa kasar Iraki shawara kan harkokin tsaro Qasim al-Araji sun bukaci kasashen duniya da su dakatar da kisan gillar da gwamnatin Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a zirin Gaza.
Al-Araji, wanda ke jagorantar wata tawagar jami’an tsaro a kasar Iran, ya gana da Araghchi a yammacin jiya Litinin, inda suka yi musayar ra’ayi da su kan hanyoyin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, da kuma tattauna halin da ake ciki a Gaza da Lebanon.
Dukkan jami’an biyu sun bayyana damuwarsu kan yadda Isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, sannan sun bukaci kasashen duniya da su dauki matakin dakatar da kisan kiyashi da laifukan da gwamnatin mamaya ke yi wa Falasdinawa, tare da tabbatar da isar da kayan agajin jin kai.
Araghchi ya bayyana kyakkyawar alakar da ke tsakanin Tehran da Bagadaza daga dukkan fannoni, inda ya jaddada bukatar ci gaba da tuntubar juna da karfafa hadin gwiwa kan harkokin tsaro, musamman a fannin kula da kan iyaka.
Al-Araji ya kuma yi wa Araghchi bayanin ci gaban da aka samu wajen aiwatar da yarjejeniyar tsaro ta tsakanin Iran da Iraki, yana mai jaddada aniyar Bagadaza na ci gaba da tabbatar da ita.
Ya yaba da hadin kai da tsayin daka da al’ummar Iran suke da shi wajen tunkarar wuce gona da iri na kasashen waje, yana mai tabbatar da cewa Iraki ba za ta taba bari a yi amfani da yankinta wajen yin barazana ga ‘yancin kai ko tsaron kasar Iran ba. Bangarorin biyu sun kara jaddada bukatar hadin kan kasashen musulmi wajen tunkarar manufofin wuce gona da iri na Isra’ila
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Equatorial Guinea ta zargi Faransa da karan-tsaye wa zaman lafiya a kasar October 21, 2025 Faransa : Sarkozy, ya fara zaman gidan yari na shekara 5 October 21, 2025 Gaza : Falasdinawa 97 sojin Isra’ila suka kashe tun bayan cimma yarjejeniya October 21, 2025 Iran Da Faransa Zasu Yi Musayar Fursinoni, Esfandiari Tana Daga Cikin Wacce Za’a Sallama October 21, 2025 Gaza: Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa 57 A Cikin Sa’o’i 24 Da Suka Gabata October 21, 2025 Kakakin Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Babu Wata Tattaunawa Da HKI October 21, 2025 Tom Barak: Saudiyya na gab da kulla alaka da Isra’ila a hukumance October 21, 2025 Kremlin: Rasha a shirye take don fadada hadin gwiwa da Iran a dukkanin fannoni October 21, 2025 Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Trump Cewa; Su Ci Gaba Da Mafarkinsu October 20, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Yin Riko Da Hakkokin Kasarta October 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci