Jami’an tsaro sun kama Sowore saboda shirya zanga-zanga
Published: 23rd, October 2025 GMT
Jami’an ‘yan sandan Najeriya sun kama ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore, bisa ci gaba da zanga-zangar neman a saki shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu.
Sowore, wanda aka kama a ranar Alhamis a birnin Abuja, wasu jami’ai dauke da bindiga ne suka yi masa dirar mikiya, sannan suka tafi da shi zuwa wani wuri da ba a bayyana ba tukuna.
Lauya mai kare haƙƙin ɗan adam kuma mai rajin kare ’yancin jama’a, Deji Adeyanju, ya tabbatar da faruwar lamarin ga wakilinmu.
“Eh, Sowore yanzu haka ’yan sanda sun kama shi,” in ji shi.
Har yanzu ba a bayyana dalilin da ya sa aka kama shi ba, amma an ji wasu daga cikin jami’an na cewa an tafi da shi ne saboda ci gaba da tayar da hankalin jama’a.
A ranar Alhamis ce dai Sowore ya jagoranci shirya zanga-zangar neman a saki mai fafutukar neman kafa ƙasar Biafra, Nnamdi Kanu, inda daga bisani jami’an tsaro suka tarwatsa su.
Bayan kammala zanga-zangar dai, jami’an tsaron sun kuma kama kanin Kanu da kuma lauyansa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
ISWAP: Mun kawar da duk wata barazana — Gwamnatin Ondo
Gwamnatin Jihar Ondo ta roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu bayan gargaɗin da Hukumar Tsaro ta DSS, ta yi na cewar wasu mayaƙan ISWAP na shirin kai hari wasu sassan jihar.
A cikin wata sanarwa, Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Mista Idowu Ajanaku, ya bayyana cewa irin waɗannan rahotanni abu ne na yau da kullum a harkokin tsaro.
NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026 Idan Tinubu ya gaza zai yi wuya a samu shugaban da zai yi nasara — Shehu SaniYa ce hukumomin tsaro suna yawan musayar bayanai irin waɗannan domin daƙile duk wata barazana.
Ajanaku, ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati tare da hukumomin tsaro sun ɗauki matakai don kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.
“Gwamnati da hukumomin tsaro suna kan lamarin kuma suna ɗaukar duk matakan da suka dace don tabbatar da cewa Jihar Ondo ta kasance cikin aminci,” in ji sanarwar.
Ya kuma roƙi mazauna jihar da su kwantar da hankalinsu, su ci gaba da ayyukansu na yau da kullum, sannan su riƙa sanar da hukumomin tsaro idan suka ga wani abun zargi.
Kwamishinan ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta mayar da hankali sosai kan yankunan da ke iyakar wasu jihohi don kawar da kowace irin barazana.
“Don Allah kada ku firgita, kada kuma ku ɗauki doka a hannunku. Ku haɗa kai da gwamnati da hukumomin tsaro domin mu ci gaba da tabbatar da tsaron jiharmu,” in ji Ajanaku.