Aminiya:
2025-12-08@12:44:23 GMT

Rasha ta miƙa wa Ukraine sojoji 1,000 da suka mutu a fagen daga

Published: 24th, October 2025 GMT

Rasha ta miƙa wa Ukraine gawarwakin sojoji 1,000 da suka mutu a fagen daga, a cewar wata hukumar gwamnatin Ukraine da ke kula da lamurran fursunonin yaƙi.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa na AFP ya ruwaito cewa ita ma Rashar ta karɓi gawarwakin sojoji 31 daga ɓangaren Ukraine.

Messi ya tsawaita kwantiraginsa da Inter Miami Jami’an tsaro sun kama Sowore saboda shirya zanga-zanga

Musayar fursunonin yaƙi da kuma gawarwakin sojoji da suka mutu na daga cikin al’amuran haɗin gwiwa da har yanzu ke gudana tsakanin Kyiv da Moscow, tun bayan mamayar da Rasha ta kai Ukraine a Fabrairun 2022.

Rahotanni daga Kyiv sun ce musayar gawarwakin na daga cikin yarjejeniyar da ɓangarorin biyu suka cimma domin bai wa iyalai damar binne ’yan uwansu cikin mutunci.

“A yau aka gudanar da musayar gawarwaki,” in ji Hedikwatar Tsare-tsaren Ukraine kan Fursunonin Yaƙi a wani saƙo da ta wallafa a shafukan sada zumunta.

Ukraine ta bayyana cewa a musayar da aka yi a lokutan baya, Rasha ta miƙa mata gawarwakin sojojinta yayin da ita ma ke mayar da na ɓangaren Rasha a cikin wani tsarin da ƙungiyar agaji ta Red Cross ke taimakawa wajen sa ido.

A watan Yuli, Agusta da kuma Satumba ne Kyiv ta sanar da karɓar gawarwakin sojoji 1,000 daga Rasha, abin da ke nuna yawan asarar rayuka da ake yi a fagen daga tsakanin ƙasashen biyu.

Hedikwatar ta ce hukumomin tsaro za su fara aikin tantance gawarwakin da aka dawo da su a nan gaba kaɗan, tana mai gode wa Ƙungiyar Red Cross ta Duniya (ICRC) bisa rawar da ta taka wajen tabbatar da nasarar musayar gawarwakin.

A watan Fabrairun bana, Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya shaida wa kafafen yada labaran Amurka cewa ƙasarsa ta rasa sojoji fiye da 46,000, sannan akwai dubbai da ake ɗauka a matsayin wadanda suka ɓata a fagen daga.

Wasu alƙaluma da kafafen labaran BBC da Mediazona suka tattara, sun tabbatar da mutuwar sojojin Rasha sama da 135,000 tun bayan fara yaƙin — duk da cewa sun ce akwai yiwuwar adadin ya zarta haka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Ukraine gawarwakin sojoji

এছাড়াও পড়ুন:

An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja

An gano gawar wani malamin makarantar Islamiyya kuma mahaifin ’ya’ya bakwai, Malam Awwal Yakubu, a cikin wani kango da ke rukunin gidaje na Talba a birnin Minna, na Jihar Neja.

Malam Awwal, yana da makarantar Islamiyya a unguwar Barikin-Saleh, an neme shi sama ko ƙasa tun ranar Alhamis ɗin da ta gabata.

’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin

An gano gawarsa ne da safiyar ranar Lahadi.

Rahotanni sun nuna cewa an ƙone al’aurarsa, sannan an samu kwalin ashana a gefen gawarsa.

Shugaban al’ummar yankin, Malam Mahmud Dalhatu Iya, ya shaida wa Aminiya cewa iyalan mamacin sun riga sun gano gawar kuma an riga an binne shi.

Ya ce, “An sanar da ni cewa an ga wata gawa ta lalace a wani gini da ba a kammala ba a cikin rukunin gidajenmu.

“Mun kai wa ’yan sanda rahoto. Muna nan lokacin da wani ya zo ya ce shi abokin mamacin ne, ya kuma ya ɓace tun ranar Alhamis. An yi wa gawar sutura don yi mata jana’iza a lokacin da nake magana da ku.”

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “A yau, 7 ga watan Disamba 2025, da misalin ƙarfe 10 na safe, an samu rahoto cewa an ga gawa a bayan rukunin gidaje na Talba da ke kan titin Kpakungu.

“Jami’an ’yan sandan Kpakungu sun je wajen kuma sun gano gawar ta lalace cikin wani gini da ba a kammala ba.

“Daga bisani iyalansa suka tabbatar da cewa Auwal Yakubu ne, mai shekaru 45, mazaunin wannan yanki.”

Ya ƙara da cewa, “Ana zargin cewa an jefar gawar ne a wajen, domin an ruwaito ya ɓace tun a ranar 4 ga watan Disamba kafin a gano shi da safiyar yau.

“An kai gawar asibiti, kuma an fara bincike don gano musabbabin rasuwarsa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike