Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
Published: 23rd, October 2025 GMT
Yanzu haka kuwa, hankula na kara karkata ga shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da Sin za ta aiwatar tsakanin shekarar 2026 dake tafe zuwa shekarar 2030, kuma masharhanta na ganin a karon gaba, Sin za ta fadada manufofinta na samar da ci gaba domin dorar da nasarorin da ta riga ta cimma.
Muhimman fannonin da ake ganin shirin na iya mayar da hankali a kansu, sun hada da tunkarar kalubalen karuwar kason al’ummar kasar masu tsayin shekaru, da kokarin warware tarnakin kasashen yamma dangane da harkokin cudanyar fasaha, yayin da Sin din ke fafada kirkire-kirkire a cikin gida.
Kamar yadda Sin ta riga ta dora dan-ba a fannonin zuba jari don cin gajiyar fannonin kimiyya da fasaha, da fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, ta kuma kai ga samun manyan nasarori, a nan gaba ma ana fatan ganin karin ci gaban kasar a wadannan fannoni.
Har ila yau, wasu muhimman fannonin da aka ga kasar Sin na mayar da hankula a kai sun hada da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da inganci, da daidaita cin gajiya tsakanin ayyukan kare muhalli da na zamanintar da tattalin arziki.
Fatan dukkanin sassan Sin, da ma masu burin nasarar kasar shi ne kamar yadda shirye-shiryenta na raya kasa na shekaru biyar-biyar guda 14 suka yi nasara, shi ma shirin karo na 15 zai cimma nasarar da ake fata, ga ita kanta Sin da ma sauran sassan duniya abokan tafiyarta.(Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya
A ranar 30 ga watan Mayun bana, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin sanya hannu kan yarjejeniyar da ta tabbatar da kafuwar kungiyar IOMed, kuma a madadin kasar Sin, ya sanya hannu kan yarjejeniyar aikinta a yankin musamman na Hong Kong.
Tun daga watan Agustan bana, kasashe 37 sun sanya hannu kan yarjejeniyar kafuwar kungiyar, kana takwas daga cikinsu sun amince da fara aiwatar da ita. A matsayin wadda ta gabatar da shawarar kafa IOMed, kuma mai masaukinta, kasar Sin na kira ga karin kasashe da su gaggauta shiga kungiyar, su kuma shiga a dama da su cikin hadin gwiwar kut-da-kut na ayyukanta, kana su samar da sabuwar gudunmawa ga wanzuwar zaman lafiya da ci gaban duniya baki daya. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA