Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
Published: 23rd, October 2025 GMT
Yanzu haka kuwa, hankula na kara karkata ga shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da Sin za ta aiwatar tsakanin shekarar 2026 dake tafe zuwa shekarar 2030, kuma masharhanta na ganin a karon gaba, Sin za ta fadada manufofinta na samar da ci gaba domin dorar da nasarorin da ta riga ta cimma.
Muhimman fannonin da ake ganin shirin na iya mayar da hankali a kansu, sun hada da tunkarar kalubalen karuwar kason al’ummar kasar masu tsayin shekaru, da kokarin warware tarnakin kasashen yamma dangane da harkokin cudanyar fasaha, yayin da Sin din ke fafada kirkire-kirkire a cikin gida.
Kamar yadda Sin ta riga ta dora dan-ba a fannonin zuba jari don cin gajiyar fannonin kimiyya da fasaha, da fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, ta kuma kai ga samun manyan nasarori, a nan gaba ma ana fatan ganin karin ci gaban kasar a wadannan fannoni.
Har ila yau, wasu muhimman fannonin da aka ga kasar Sin na mayar da hankula a kai sun hada da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da inganci, da daidaita cin gajiya tsakanin ayyukan kare muhalli da na zamanintar da tattalin arziki.
Fatan dukkanin sassan Sin, da ma masu burin nasarar kasar shi ne kamar yadda shirye-shiryenta na raya kasa na shekaru biyar-biyar guda 14 suka yi nasara, shi ma shirin karo na 15 zai cimma nasarar da ake fata, ga ita kanta Sin da ma sauran sassan duniya abokan tafiyarta.(Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47
Jami’an Rundunar Leƙen Asiri ta musamman a Jihar Kwara sun cafke wani tsohon ɗan gidan yari mai suna Godday Agaadi da bindiga ƙirar AK-47.
An kama Emmanuel Okah ne bayan an same shi da bindigar AK-47 da harsashi guda 25 a jikinsa, a lokacin da yake sanye da kayan ’yan sanda.
Dubunsa ta cika ne yana ƙoƙarin satar talotalo a unguwar Omu Aran da ke ƙaramar hukumar Irepodun.
Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Adekimi Ojo, ya bayyana a taron manema labarai a ƙarshen mako cewa binciken da jami’an suka gudanar ne ya kai ga cafke Agaadi.
An kama sojojin da suka yi yunƙurin juyin mulki a Benin An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a NejaYa ƙara da cewa bincike ya ci gaba har ya kai ga kama wasu mutane biyu da ake zargin abokan aikinsa, ciki har da wani boka mai shekaru 41 mai suna Oyeniyi Olabode.
Kwamishinan ya ce babban wanda ake zargi tsohon ɗan gidan yari ne da ke da tarihin aikata laifukan tashin hankali a yankin Omu Aran.
’Ya tabbatar da cewa dukkansu uku suna hannun ’yan sanda, kuma ana ci gaba da bincike domin gano sauran mambobin ƙungiyar.