Yanzu haka kuwa, hankula na kara karkata ga shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da Sin za ta aiwatar tsakanin shekarar 2026 dake tafe zuwa shekarar 2030, kuma masharhanta na ganin a karon gaba, Sin za ta fadada manufofinta na samar da ci gaba domin dorar da nasarorin da ta riga ta cimma.

 

Muhimman fannonin da ake ganin shirin na iya mayar da hankali a kansu, sun hada da tunkarar kalubalen karuwar kason al’ummar kasar masu tsayin shekaru, da kokarin warware tarnakin kasashen yamma dangane da harkokin cudanyar fasaha, yayin da Sin din ke fafada kirkire-kirkire a cikin gida.

 

Kamar yadda Sin ta riga ta dora dan-ba a fannonin zuba jari don cin gajiyar fannonin kimiyya da fasaha, da fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, ta kuma kai ga samun manyan nasarori, a nan gaba ma ana fatan ganin karin ci gaban kasar a wadannan fannoni.

 

Har ila yau, wasu muhimman fannonin da aka ga kasar Sin na mayar da hankula a kai sun hada da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da inganci, da daidaita cin gajiya tsakanin ayyukan kare muhalli da na zamanintar da tattalin arziki.

 

Fatan dukkanin sassan Sin, da ma masu burin nasarar kasar shi ne kamar yadda shirye-shiryenta na raya kasa na shekaru biyar-biyar guda 14 suka yi nasara, shi ma shirin karo na 15 zai cimma nasarar da ake fata, ga ita kanta Sin da ma sauran sassan duniya abokan tafiyarta.(Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka October 23, 2025 Daga Birnin Sin An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15 October 23, 2025 Daga Birnin Sin Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

 

A ranar 30 ga watan Mayun bana, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin sanya hannu kan yarjejeniyar da ta tabbatar da kafuwar kungiyar IOMed, kuma a madadin kasar Sin, ya sanya hannu kan yarjejeniyar aikinta a yankin musamman na Hong Kong.

 

Tun daga watan Agustan bana, kasashe 37 sun sanya hannu kan yarjejeniyar kafuwar kungiyar, kana takwas daga cikinsu sun amince da fara aiwatar da ita. A matsayin wadda ta gabatar da shawarar kafa IOMed, kuma mai masaukinta, kasar Sin na kira ga karin kasashe da su gaggauta shiga kungiyar, su kuma shiga a dama da su cikin hadin gwiwar kut-da-kut na ayyukanta, kana su samar da sabuwar gudunmawa ga wanzuwar zaman lafiya da ci gaban duniya baki daya. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa October 21, 2025 Daga Birnin Sin Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba October 21, 2025 Daga Birnin Sin Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta? October 21, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15
  • Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
  • Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka
  • Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera
  • Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
  • Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
  • Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin
  • Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia