An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a Kano
Published: 20th, October 2025 GMT
Wata Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a unguwar Danbare a Jihar Kano, ta gurfanar da wani mutum mai suna Malam Shaddadu bisa zargin sayar da gidan ɗansa ba tare da izini ba.
Ɗan mutumin wanda ya gabatar da ƙara, Muhammad Shaddadu, ya shaida wa kotu cewa, lamarin ya samo asalin ne tun bayan da mahaifinsa ya saya wa wasu ‘yan uwansa biyu da suke uba ɗaya babura masu kafa uku da aka fi sani da Adaidata Sahu.
Sai dai daga baya, tsautsayi ya rutsa da ɗaya daga cikinsu wanda ɓata-gari suka kai masa hari har suka kashe shi, kuma suka yi awon gaba da baburinsa.
Muhammad ya bayyana cewa kwatsam sai mahaifinsa ya ɗora masa alhakin faruwar lamarin, inda ya kai shi har gaban kotu kuma aka tsare shi a gidan yari.
Amma daga baya kotu ta wanke shi daga tuhumar da ake yi masa, kuma bayan ya dawo gida, ya gano cewa mahaifinsa ya sayar da gidansa, bisa zaton cewa ba zai dawo ba.
Yayin da aka karanta masa ƙunshin tuhumar a kotu, mahaifin ya musanta zargin, yana mai cewa ba shi da laifi.
Sai dai alƙalin kotun, Malam Munzali Idris Gwadabe, wanda ya bayyana cewa lamarin a matsayin rikicin cikin gida tsakanin uba da ɗa, ya miƙa shari’ar zuwa kotun sasanci domin ta jiɓanci taƙaddamar da ke tsakanin ɓangarorin biyu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗa Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa
Majalisar Dattawa ta sanar da aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocinta waɗanda suka haɗa har da na tsaro da na tattara bayanan sirri, sakamakon ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.
Shugaban Majalisar Dattawan, kuma shugaban kwamitin majalisar kan harkokin zaɓe, Sanata Godswill Akpabio ne ya sanar da hakan yayin zaman na yau Talata.
Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe Tinubu ya naɗa Janar CG Musa sabon Ministan Tsaron NijeriyaA sabbin sauye-sauyen da majalisar ta aiwatar, Sanata Yahaya Abdullahi daga Jihar Kebbi ya zama shugaban kwamitin tsaro da na tattara bayanan sirri bayan ya bar kujerar kwamitin tsare-tsare na ƙasa.
An naɗa Sanata Shehu Buba daga Bauchi a matsayin shugaban kwamitin harkokin Kiwo, bayan cire shi daga kujerar kwamitin tsaro da tattara bayanan sirri a makon da ya gabata.
Haka kuma, Sanata Mustafa Musa daga Yobe ya karɓi ragamar shugabancin kwamitin tsare-tsare na ƙasa.
A ɓangaren kwamitin Sojin Sama kuma, Sanata Osita Ngwu daga Enugu wanda shi ne mataimakin shugaban Marasa Rinjaye a Majalisa ya zama muƙaddashin shugaban kwamitin bayan rashin lafiya ta hana tsohon shugaban ci gaba da aiki.
Majalisar ta ce waɗannan sauye-sauyen na da nufin ƙarfafa aikin sa ido da inganta duk wasu hanyoyin ɗaukar mataki kan batutuwan tsaro da ke tasowa a faɗin ƙasar.