Aminiya:
2025-10-24@22:43:24 GMT

Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC

Published: 24th, October 2025 GMT

Jam’iyyar ADC ta nemi Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana wa ’yan Najeriya ainihin dalilin da ya sa ya sauya hafsoshin tsaron ƙasa ba zato ba tsammani.

Aminiya ta ruwaito yadda shugaban ƙasa ya sauya hafsoshin tsaron da ya naɗa shekaru biyu da suka wuce.

Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri ’Yan sanda sun kama ɗalibi da ya soki Gwamnan Neja

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, ya ce jam’iyyar ta damu ganin yadda aka yi sauyin ba zato ba tsammani bayan jita-jitar yunƙurin juyin mulki.

“Ko da yake shugaban ƙasa yana da ikon yin irin waɗannan sauye-sauye, amma mum damu da wannan mataki biyo bayan jita-jitar yunƙurin juyin mulki,” in ji Abdullahi.

Ya ƙara da cewa amsar da gwamnatin ta bayar game da wannan jita-jitar ba yi cikakken bayani ba face ruɗani da ta jefa mutane a ciki.

ADC ta ce irin wannan sauyi na iya haifar da ruɗani a rundunar sojoji, don haka dole ne a samu dalilai masu ƙarfi kafin a yanke irin wannan hukunci.

Jam’iyyar, ta ce gwamnati tana da alhakin bayyana wa ’yan ƙasa ainahin abin da yake faruwa .

“Mu a matsayin jam’iyyar adawa, muna son zaman lafiya da ɗorewar dimokuraɗiyya a ƙasarmu.

“Abin da ke faruwa a maƙwabtan ƙasashe kamar Chadi da wasu ƙasashen yankin Sahel ya ƙara mana damuwa,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnatin Tinubu da rashin mayar da hankali, inda ta bayyana cewa matsalar tsaro na ƙara ta’azzara yayin da ’yan ta’adda da ’yan fashi ke sake yin ƙarfi a wasu yankuna na ƙasar.

“Sauya hafsoshin tsaro ba zai warware waɗannan matsalolin ba. Maimakon haka, zai sa mutane su yi zargin cewa gwamnati ta fi mayar da hankali kan siyasa da mulki sama da kare rayukan ’yan ƙasa,” in ji Abdullahi.

ADC, ta gargaɗi gwamnati cewa sauya dukkanin hafsoshin tsaro a lokaci guda na iya ƙara janyo jita-jita da hasashe marasa tushe.

Saboda haka, jam’iyyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta fito fili ta bayyana gaskiya, tare da tabbatar wa ’yan Najeriya cewa dimokuraɗiyyar ƙasar ba ta cikin hatsari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hafsoshin tsaro Tsaro sauya hafsoshin tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, Ta Kaddamar da Dakin Karatu Na Zamani a Zamfara

Uwargidan Shugaban Ƙasa ta Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta kaddamar da Dijital E-Learning Library a Gusau, Jihar Zamfara — ɗaya daga cikin jihohi goma da aka zaɓa a faɗin ƙasar domin aiwatar da wannan muhimmin aiki ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) tare da haɗin gwiwar Hukumar bunkasa ayukkan fasaha ta kasa (NITDA).

A yayin bikin kaddamarwar, Sanata Tinubu ta bayyana cewa wannan aiki ba wai game da fasaha da kwamfuta kawai ba ne, amma yana nufin ƙarfafa matasa, rage gibin fasaha (digital divide), da kuma buɗe sabbin ƙofofin ilimi da ƙirƙira ga al’ummar Zamfara da ma Najeriya baki ɗaya.

Uwargidan Shugaban Ƙasa, wacce Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta wakilta, ta bayyana cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaba a kowace al’umma.

Ta ce, a wannan zamani na dijital, samun kayan koyon zamani ba wata alfarma ba ce, amma wajibi ne domin ci gaban ilimi.

A cewarta, ta hanyar wannan dijital library, dalibai, malamai, masu bincike da ma jama’a gaba ɗaya za su sami damar shiga manyan bayanai, albarkatu da dama na ilmantarwa a sauƙaƙe.

Sanata Tinubu ta bayyana cewa Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) yana da burin tallafa wa ilimi, ƙirƙira da ci gaban zamantakewa, kuma wannan E-Learning Library na ɗaya daga cikin manyan alamu na hangen nesa na shirin.

Ta kuma yaba wa Ma’aikatar Sadarwa, Ƙirƙira da Tattalin Arzikin Dijital da kuma NITDA bisa ƙwarewar su wajen aiwatar da aikin.

A nata jawabin, Uwargidan Gwamnan Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta nuna godiya mai zurfi ga mijinta, Gwamna Dauda Lawal, bisa jajircewarsa wajen inganta harkar ilimi a jihar.

Ta shawarci dalibai, malamai da masu bincike da su amfani da wannan cibiyar ta dijital yadda ya kamata, domin bunƙasa ilimi da gina kyakkyawar makoma ga matasa da ƙarni masu zuwa.

Tun da fari, Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Zamfara, Malam Wadatau Madawaki, wanda Maryam Yahaya, Babban Sakataren Ma’aikatar, ta wakilta, ya yaba wa Sanata Oluremi Tinubu bisa ƙoƙarinta wajen bunƙasa ilimin dijital ta hanyar kafa wannan E-Learning Library ƙarƙashin shirin Renewed Hope Initiative.

Kwamishinan ya bayyana aikin a matsayin babbar nasara wajen bunƙasa ƙirƙira, haɗa kai ta hanyar fasaha da kuma tabbatar da ingantaccen ilimi ga ’yan Zamfara.

Haka kuma, ya yaba wa Uwargidan Gwamna Hajiya Huriyya Dauda Lawal bisa wakiltar Uwargidan Shugaban Ƙasa da kuma irin goyon bayanta da jajircewa wajen cigaban ilimi a jihar.

Madawaki ya ƙara da cewa wannan E-Learning Library na tafiya da hangen nesa na Gwamna Dauda Lawal, wanda tun bayan hawa mulki ya ayyana dokar ta-baci kan ilimi, matakin da ya haifar da gagarumin ci gaba a fannin ilimi a jihar.

Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
  • Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya
  • Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu
  • Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — Wike
  • Matasa Dubu Ɗaya Za Su Samu Horon Fasahar Zamani A Nasarawa — Remi Tinubu
  • Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, Ta Kaddamar da Dakin Karatu Na Zamani a Zamfara
  • Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas?
  • Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio