Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC
Published: 24th, October 2025 GMT
Jam’iyyar ADC ta nemi Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana wa ’yan Najeriya ainihin dalilin da ya sa ya sauya hafsoshin tsaron ƙasa ba zato ba tsammani.
Aminiya ta ruwaito yadda shugaban ƙasa ya sauya hafsoshin tsaron da ya naɗa shekaru biyu da suka wuce.
Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri ’Yan sanda sun kama ɗalibi da ya soki Gwamnan NejaA cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, ya ce jam’iyyar ta damu ganin yadda aka yi sauyin ba zato ba tsammani bayan jita-jitar yunƙurin juyin mulki.
“Ko da yake shugaban ƙasa yana da ikon yin irin waɗannan sauye-sauye, amma mum damu da wannan mataki biyo bayan jita-jitar yunƙurin juyin mulki,” in ji Abdullahi.
Ya ƙara da cewa amsar da gwamnatin ta bayar game da wannan jita-jitar ba yi cikakken bayani ba face ruɗani da ta jefa mutane a ciki.
ADC ta ce irin wannan sauyi na iya haifar da ruɗani a rundunar sojoji, don haka dole ne a samu dalilai masu ƙarfi kafin a yanke irin wannan hukunci.
Jam’iyyar, ta ce gwamnati tana da alhakin bayyana wa ’yan ƙasa ainahin abin da yake faruwa .
“Mu a matsayin jam’iyyar adawa, muna son zaman lafiya da ɗorewar dimokuraɗiyya a ƙasarmu.
“Abin da ke faruwa a maƙwabtan ƙasashe kamar Chadi da wasu ƙasashen yankin Sahel ya ƙara mana damuwa,” in ji sanarwar.
Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnatin Tinubu da rashin mayar da hankali, inda ta bayyana cewa matsalar tsaro na ƙara ta’azzara yayin da ’yan ta’adda da ’yan fashi ke sake yin ƙarfi a wasu yankuna na ƙasar.
“Sauya hafsoshin tsaro ba zai warware waɗannan matsalolin ba. Maimakon haka, zai sa mutane su yi zargin cewa gwamnati ta fi mayar da hankali kan siyasa da mulki sama da kare rayukan ’yan ƙasa,” in ji Abdullahi.
ADC, ta gargaɗi gwamnati cewa sauya dukkanin hafsoshin tsaro a lokaci guda na iya ƙara janyo jita-jita da hasashe marasa tushe.
Saboda haka, jam’iyyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta fito fili ta bayyana gaskiya, tare da tabbatar wa ’yan Najeriya cewa dimokuraɗiyyar ƙasar ba ta cikin hatsari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hafsoshin tsaro Tsaro sauya hafsoshin tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wasu mutum biyar sakamakon haɗura uku da suka auku a jihar.
Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya ce hatsrin farko ya faru ne da safiyar ranar Alhamis a unguwar Badawa Layin Day by Day ca Ƙaramar Hukumar Nassarawa.
Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin Jirgin sojin sama ya yi hatsari a NejaLamarin ya faru ne a wani gida mai faɗin kafa 25 da 20 wanda ya kama da wuta.
Ma’aikatan kashe gobara sun ceto wata yarinya mai shekara 10 daga a cikin gidan, amma daga baya ta rasu a asibiti.
An bai wa iyayenta gawarta.
Hatsari na biyu ya faru ne a Ƙauyen Badume Kanawa da ke Karamar Hukumar Bichi.
Wani mutum mai shekara 65, Sa’idu Gada, yana aiki a cikin rijiya lokacin da igiyar da ta ke riƙe da shi ta tsinke, ya faɗa ciki.
Ɗansa mai shekara 20, Sani Isyaku, ya shiga rijiya domin ceto shi, shi ma ya maƙale.
Wani mutum na uku, Yakubu Abdullahi mai shekara 60, ya shiga domin taimakonsu, shi ma daga bisani ya faɗa cikin rijiyar.
Ma’aikatan hukumar sun fito da su daga rijiyar, amma sun riga sun rasu.
An miƙa wa ’yan sandan Badume gawarwakinsu.
A wani lamari na daban kuma, wani yaro mai shekara 10, Hassan Iliyasu Haruna, ya zame tare da faɗa wa rijiya a Ƙaramar Hukumar Danbatta.
Ma’aikatan hukumar kashe gobara sun ceto shi, amma daga baya ya rasu.
An miƙa wa mahaifinsa gawar yaron.
Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Kano, Sani Anas, ya ja hankalin jama’a da su daina shiga rijiya domin ceto mutane, domin a cewarsa hakan na da hatsari.