A yau Laraba 22 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana cewa, huldar diflomasiyya ta shugabanni na matukar taka rawar gani wajen jagorantar dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka, kuma shugabannin kasashen biyu suna ci gaba da cudanya da kuma sadarwa a tsakaninsu.

Shugaban Amurka Trump ya ce, yana sa ran kasashen Sin da Amurka za su cimma matsaya kan batutuwan kasuwanci a taron kolin APEC da za a yi a mako mai zuwa, amma ya ce, watakila shugabannin Sin da Amurka ba za su gana ba a lokacin. Guo Jiakun ya yi wadannan bayanai ne a lokacin da yake amsa tambayoyi game da wannan batu, inda ya yi nuni da cewa, a halin yanzu babu wani cikakken bayani dangane da ganawar shugabannin Sin da Amurka.

Game da tattaunawar gaggawa tsakanin EU da kasar Sin kan batun hana fitar da ma’adanan farin karfe da kasar Sin ta yi kuwa, Guo Jiakun ya ce, yana fatan bangaren EU zai mutunta kudurinsa na nuna goyon baya ga cinikayya cikin ‘yanci, da adawa da kariyar cinikayya, da samar da yanayin kasuwanci na gaskiya da adalci da rashin nuna wariya ga daukacin kamfanonin kasashen duniya, da daukar kwararan matakai don kiyaye tattalin arzikin kasuwanci da ka’idojin hukumar kasuwanci ta duniya (WTO), da kafe kai da fata a kan amfani da tattaunawa da tuntuba wajen warware takaddamar kasuwanci yadda ya kamata. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11 October 22, 2025 Daga Birnin Sin Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera October 22, 2025 Daga Birnin Sin Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika

Sabon bashin, ya nuna yadda Bankin ya bai wa kasar bashin da ya kai jimlar dala biliyan 5.1 tun daga ranar 31 na watan Okutobar 2025.

Kazalika, wannan sabon bashin, zai taimaka wa kashi na biyu na shirin habaka tattalin arziki a bangaren samar da makamashi da  sauye-sauye, a fannin makamashin da cimma burin da ake da shi, na rage dumamar yanayi.

A zagaye na farko na shiri,  za a kara karfafa sauye-sauye wajen tafiyar da kudade da tabbatar da ana aiki da Ka’ida da kuma sanya ido, kan yadda ake kashe kudaden Gwamnati.

Bugu da kari a zagaye na biyu kuma, manufar shi ne, a kara habaka samar da makamashi da fadada samar da wutar lantarki wanda hakan zai bayar da dama, wajen janyo kamfanonin masu zaman kansu domin su zuba jari, a fannin.

A jawabinsa Darakta Janar na Bankin a Nijeriya Abdul Kamara, ya sanar da cewa, a zagaye na farko na shirin ya hada da samar da sauye-sauye a fannin makamashi, musamman wajen habaka hanyar samar da kudaden shiga ga fannin da bai shafi Man Fetur ba.

Ya kara da cewa, shirin zai tallafa wa tsarin kasa na  NDC wanda zai fara aiki daga 2026 zuwa 2030, musamman ganin cewa, shirin yayi daidai da koƙarin da ake yi na yakar sauyin yanayi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabo Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Sheikh Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Lebanon Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba
  • Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha
  • Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi