Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala
Published: 24th, October 2025 GMT
Manzon Allah (S.A.W.) yana da tunani mai zurfi, tunanin nan har ya shigar da shi duniyar tunani, duniyar tunani ta zamar masa gaskiya har yana tu’ammali da duniyar tunani, in ji mai wannan littafin masanin falsafa. Manzon Allah (S.A.W.) cikin gaskiya ya shiga ya yi tafakkuri, ya ya ibada, ya yi zikiri har ya koma asalinsa har ya haɗu da haƙiƙarsa ta Muhammadiyya (S.
Manzon Allah (.S.A.W.) yana da tunani mai zurfi, yana da yalwar tunani da ƙarfi, kai har abin da ƙwaƙwalwarsa take shirya masa sai ya zama gaskiya, gashi yana gani, in ƙarya ne ya za a yi a gani, a’a wannan gaske ne dama ana haka, kuma mumini a imaninsa idan ya yi imani aljannar nan sai ya ganta tun daga nan duniya, Allah ya kiyaye idan wuta ce sai ya ganta tun a nan, idan mala’iku ne sai ya gan su, duk ba wani abu ba ne zai iya ganin su tun daga nan duniya, ko Annabi ne zai iya ganin shi tun daga nan duniya. Wannan duniyar nan ga baki ɗaya wani ɗigo ne a cikin wannan duniyar ta tunani, ita ma wannan duniyar ta tunani ɗan ɗigo ce a cikin duniyar haƙiƙa.
Mafalsafin nan yake cewa Manzon Allah (S.A.W.) mutum ne mai ɗaukaka da tsarki da ya kai kowane irin matsayi na mai girma (S.A.W.), don haka wata wuya ko wani bala’i bai jin sa, ba wai bai jin sa a haƙiƙa ba ko ya dame shi ba, yana ji amma abin da yake so ya kai ya hana shi jin zafin wannan bala’i.
Manzon Allah yana da ƙarfin hankali wanda ya fi ƙarfin misaltuwa, yana da ƙarfin hankali, sannan yana da ƙarfin haƙuri, abin da zai samu wani gwarzon ya yi raki da ihu, amma Manzon Allah (S.A.W.) sai a yi a gama ba ka san an yi ba. Yana da ƙarfin niyya kamar yadda ya fara faɗa a farko.
Yake cewa ko ka ji an ce yana da wasu abubuwa, ba ana nufin laifi ba ne mai sunan laifi, a’a wani hali ne ya kawo dole ya yi wannan abun, ko kai ne ka zama shugaban jama’a dole ka yi wannan abin, yake cewa dole ce ta kawo, masalaha ce ta kawo kasancewarsa shugaba, kasancewarsa shugaba kuma jagora, ta sa dole sai ya yi wannan, ashe idan da adalci ba za ka kama shi da wannan laifi ba, amma a wajen mai wannan abu laifi ne, ka ga Sayyadina Ali shi ne ya yi irin wannan, ai a yanayin gudanar da mulki dole akwai tsarin da sai an buge shi, ka ga kamar a hukuncin da aka yanke wa Bani Ƙuraiza suka ce a tafi kotun Attaura, wannan hukuncin da ya bi hukuncin Attaura ne, kuma ba Manzon Allah ne ya yi wannan hukunci ba Sa’ad bin Muaz ne ya yi, Manzon Allah (SAW) kuma ya zartar, maslaha ce ta kawo kasancewarshi shugaba, ka ga idan da adalci ba za ka kama shi da wannan ba.
Bafalsafin, yake cewa Manzon Allah (S.A.W.) ya ci nasara wajen zaburar da al’ummarsa, wannan canza al’umma da ya yi, wanna juyi da ya kawo wa al’umma shi ne ya tabbata har yau. Manzon Allah (S.A.W.) bai yi shekara talatin (30) da rasuwa ba sai da mulkin al’ummarsa na larabawa ya kama tun daga Pakistan har ya zuwa Danja, duk mulkinsu ne gaba ɗaya, kuma su mutanen waɗannan wurare duk sun yarda da karatunsa, sun yarda da iliminsa, saboda Allah Ya tsarkake shi, kuma ya sa shi abin bi ne, (S.A.W.) Allah ya tabbatar da ambatonsa a cikin duk wasu shugabanni da aka yi masu tsarki.
Manzon Allah ya taɓa tambayar Jibril (A.S.) me ake nufi da “Wa rafa’ana laka zikirak”sai Jibri (A.S.) ya ce ya tambayo masa, sai ya ce abin da ake nufi shi ne duk lokacin da aka ambaci sunan Allah sai an ambace ka cikin Sallah da cikin ambatonsa da sauransu, saboda (Manzon Allah) ya ƙare cikin Halarar Allah, saboda matsayin da ya kai (S.A.W).
Imamu Zuhuri, (malamin hadisi ne), yana cikn salafus salihin, yake cewa da mutum zai yanka saniya ko ya yanka rago ko kaza da sunan Manzon Allah (S.A.W.) ya halatta a ci, saboda me, saboda Ubangiji ya ce “Wa rafa’ana laka zikirak” ya kawo ambatonsa a wajen, amma in da irin shuwagabanninmu ne na nan sai su ce Haram. Amma sun ce da kirista zai iya yin yanka musulmi ya ci, Allah ya ce abincinsu halal ne a wajenmu, mu ma namu halal ne a wurinsu, sai dai ban da giya da alade da Allah ya haramta (don babu wani abinci na alade da za a kawo ka ci), ka ga bambancin karatun malamai na baya da na yanzu, na baya suna da zurfin tunani.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: yana da ƙarfin
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa
Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanar da shirinsa na ɗaga darajar Kwalejin Jinya ta Nafisatu da ke Kwankwaso zuwa cikakkiyar Jami’ar Kiwon Lafiya albarkacin bikin zagayowar ranar haihuwarsa.
Taron na wannan Talatar, 21 ga watan Oktoban 2025, ya gudana ne a garinsa na Kwankwaso da ke Karamar Hukumar Madobi, inda aka yaba da ci gaban da makarantar ta samu tun daga kafuwarta a 2019 zuwa yanzu.
Tinubu ya naɗa sabon Minista Alƙaluman wucin-gadi na nuna Paul Biya ya lashe zaɓen KamaruKwankwaso ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin ƙara buɗe damammaki ga mata matasa su sami ilimin kiwon lafiya mai zurfi.
Ya jaddada cewa makarantar ita ce ta farko a Najeriya da ke karɓar dalibai mata kaɗai.
Ya kuma gode wa gwamnatin Jihar Kano bisa tallafa wa shirin ungozoma na Community Midwives, wanda ke taimakawa wajen inganta lafiyar mata a ƙauyuka.
A nasa jawabin, Farfaesa Saleh Ngaski Garba, shugaban majalisar gudanarwar makarantar, ya bayyana cewa kwalejin ta taimaka sosai wajen bai wa mazauna ƙauyen ilimin jinya da ungozoma, kuma yanzu tana da ɗalibai sama da 400 da suka kammala karatu.
Kwankwaso ya ce gina jami’ar zai amfanar da Kano da Najeriya baki ɗaya.