Yadda Zanga-zangar Kanu ta ja wa ’yan kasuwa da ma’aikata asara
Published: 21st, October 2025 GMT
Harkokin kasuwanci sun tsaya cik a wasu sassan Abuja sakamakon zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar ’yan ta’addan IPOB da ke neman ɓallewa daga Najeriya, Nnamdi Kanu, inda masu ’yan kasuwa da ma’aikata da dama suka yi asarar kuɗaɗen shiga.
A yankunan Wuse, Banex da Mararaba, shaguna da kasuwanni da dama sun kasance a rufe saboda fargabar tashin hankali.
“Na kasa buɗe shagona yau saboda kowa yana tsoron tashin hankali. Ko da ka bude, babu wanda zai fito saye da wannan yanayin tsoro,” in ji Peter Ayuba, mai sayar da na’urorin lantarki a kasuwar Wuse.
A Smart Bridge Plaza da Zuma Garden da ke unguwar Utako, yawancin shaguna an kulle su, sai kaɗan ne suka buɗe. Wani ma’aikaci a shagon sayar da magani ya ce ba su yi ciniki sosai ba saboda rashin kwastomomi.
An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a Kano NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUUSu ma ’yan kasuwa masu yawon talla, zanga-zangar ta shafi kasuwancinsu. Agnes Ojeh, mai sayar da ayaba da gyaɗa, ta ce duk da gargaɗin da aka yi mata kada ta fito, sai da ta fito saboda tana da yara da take ciyarwa.
Ta ce, “Na fito ne daga Mpape, duk da akwai sojoji a kan hanyoyi, amma ban sayar sosai ba saboda mutane ba su fito ba.”
Wani mai shagon aski da ya bayyana kansa da “Black Governor” ya ce kasuwar Wuse ta zama tamkar fanko saboda yawancin ’yan kasuwa musamman ’yan ƙabilar Ibo ba su buɗe shaguna ba.
“Kasuwar ta kasance shiru har zuwa kusan ƙarfe shida na yamma,” in ji shi. “Kasuwar Utako ma an rufe da farko, daga baya ne aka buɗe bayan jami’an tsaro sun dawo da doka.”
Ya kara da cewa an kama wasu matasa da suka tada zaune tsaye a yankin Zone 6 domin dawo da zaman lafiya. Wani ɗan sanda a Utako ya tabbatar mana cewa an kai waɗanda aka kama ofishin SARS da ke Guzape.
A yankunan kasuwanci kamar Central Area, Jabi da Nyanya, ofisoshi da dama sun yi aiki kaɗan kaɗan saboda ma’aikata da dama sun makara ko kuma ba su fito gaba daya ba. Wani ɗan kasuwa a Mararaba, Uche, ya ce da dama daga cikin masu shaguna sun zauna a gida bayan jin labarin cewa masu zanga-zanga na nufin shiga tsakiyar birnin.
Duk da cewa zuwa misalin ƙarfe uku na rana, an fara samun ɗan kwanciyar hankali a wasu sassan Abuja, amma jama’a da dama sun ce zanga-zangar ta dagula musu rayuwa.
Wasu ’yan kasuwa sun ce sun rasa kusan duk kuɗin shigarsu na ranar Litinin, musamman waɗanda ke sayar da kaya masu saurin lalacewa.
Yanayin garin su KanuA Umuahia, babban birnin jihar Abia inda Kanu ya fito, ma zanga-zangar ta durƙusar da harkokin kasuwanci yayin da jama’a suka kulle shaguna da kasuwanni.
Masu zanga-zangar sun bayyana a wurare daban-daban suna waƙa da rawa suna kuma kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya saki Kanu.
An lura cewa babu motoci a tituna, bankuna, tashoshin mai, manyan kasuwanni da makarantu — duka a rufe suke.
A garin Afaraukwu, inda Kanu ya fito, mazauna yankin sun taru suna waƙar neman a sake shi. Wani da ya ce sunansa Chidi ya tambayi dalilin ci gaba da tsare Kanu a ofishin DSS.
Fadar Shugaban Kasa ta magantuMai ba Shugaban Kasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya buƙaci a dauki mataki kan lauyan Kanu, Barista Ejimakor, saboda shiga zanga-zangar da aka yi a Abuja.
Onanuga ya zargi Ejimakor da “saɓa dokokin aikin lauya” bayan da ya shiga zanga-zangar neman a sake Kanu.
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Onanuga ya ce: “Ban san abin da Ejimakor yake tunani ba lokacin da ya shiga wannan zanga-zanga mai ban dariya.”
Ya ce lauya ya kamata ya san cewa batun Kanu yana gaban kotu, kuma akwai dokar ‘sub judice da ta haramta irin wannan tsoma baki.
Ya ƙara da cewa Ejimakor ya zaɓi hanyar siyasa da ba ta da tushe a doka domin tasiri kan shari’ar. “Ya kamata hukumar lauyoyi su ɗauki mataki saboda wannan rashin ladabi da rashin kiyaye ƙa’idar aikin lauya,” in ji shi.
Ra’ayoyin MasanaWani Farfesa a fannin shari’a, Okoh Akubo (SAN), ya bayyana cewa shari’ar Kanu ta zama abin damuwa.
“An taɓa wanke shi daga wasu tuhume-tuhume amma gwamnati ta ci gaba da sake gabatar da sababbi, shi ya sa shari’ar ke ci gaba har yanzu,” in ji shi.
Shi ma Farfesa Eno Cyprain daga cibiyar Institute of Law Research and Development ta Majalisar Dinkin Duniya da ke Washington DC, ya ce ya dace a saki Kanu ba tare da wani sharaɗi ba.
Ya ce idan gwamnati tana tsoron kalamansa, kotu na iya saka masa takunkumi maimakon tsare shi da ya zama tauye haƙƙinsa na faɗin albarkacin baki.
Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta HURIWA ta soki yadda aka gudanar da zanga-zangar #ReleaseNnamdiKanuNow tana cewa tsare Kanu ya zama “azabar hadin gwiwa ga ƙabilarsa da magoya bayansa.”
Neman haɗin kan Kudu da ArewaMasani kan tsaro, Dakta Kabiru Adamu, ya bayyana tsawon shari’ar Kanu a matsayin “rashin nasarar tsarin shari’a” da kuma “bala’i ga ƙasa.”
Ya ce lokaci ya yi da gwamnati za ta haɗa masu ruwa da tsaki daga yankunan kudu maso gabas da Arewa domin samun hanyar sulhu ta siyasa.
“A gaskiya, shari’ar ta yi tsawo saboda dokokinmu ba su fayyace laifin da ake tuhumar Kanu da shi ba,” in ji shi.
Ya ce gwamnati na buƙatar “tsarin fita cikin mutunci” da zai kwantar da hankali a duka ɓangarorin kasar — musamman saboda ɓarnar da ta shafi rayuka, dukiyoyi da harkokin kasuwanci.
Shari’ar Kanu za ta ci gabaBayan rahoton Ƙungiyar Likitoci ta Ƙasa (NMA) ga Babban Kotun Tarayya a Abuja cewa lafiyar Kanu ba ta da hatsari, an tsara cigaban shari’ar sa ranar Alhamis, 23 ga Oktoba.
Alƙali James Omotosho ya ɗage karar zuwa wannan rana domin Kanu da lauyansa su fara kare kansu a shari’ar ta ta’addanci da ake yi masa.
A baya jami’an DSS sun shaida wa kotu cewa kalaman Kanu da kafa ƙungiyar tsaro ta Eastern Security Network (ESN) ne suka haddasa asarar rayuka da dukiyoyi a lokacin zanga-zangar #EndSARS a 2020
Kanu an dawo da shi daga Kenya a watan Yuni 2021 domin fuskantar sababbin tuhume-tuhume.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan kasuwa kasuwa Shari a zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
Ana binciken wani tsohon ma’aikacin jinya a qasar Italiya bisa zargin ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu kuma ya je ma’aikatar fansho a matsayin mahaifiyarsa don neman fanshonta. Haka kuma an gano ya voye gawarta a cikin gidansa har tsawon shekaru uku bayan mutuwarta.
Mutumin xan Italiya ya saka tufafin mahaifiyarsa da ta mutu sannan ya yi kwalliya da gazar da jan-baki kamar yada take yi, ya je bankin da take ajiya yana neman a biya shi kuxi fanshonta, bayan ya voye gawarta a gida.
Mutumin mai shekaru 56, ma’aikacin jinya da ya rasa aikinsa a garin Mantua, ya sami damar karvar dubban kuxi na Yuro kafin asirinsa ya tonu, kamar yadda Jaridar Corriere della Sera ta Italiya ta ruwaito.
An kuma yi zargin cewa, ya naxe gawar mahaifiyarsa, Graziella Dall’Oglio, sannan ya voye ta a cikin firji a gidansu har tsawon shekara uku ba tare da ya sanar da ma’aikatar fansho ba, inda ya riqa zuwa yana cire kuxin fanshon da ake tura mata yana bidirin gabansa.
Mis Dall’Oglio ta rasu kimanin shekara uku da suka gabata, tana da shekara 82. Amma xanta bai bayar da rahoton mutuwarta a hukumance ba, maimakon haka ya naxe gawarta a cikin zane, ya saka ta a cikin wata jakar ajiye kaya sannan ya voye ta a gidan.
Rahotanni sun ce, ya yi shigar mahaifiyarsa, sanye da jan-baki da hoda da gazar da kuma sarqa, sannan ya tafi sabunta katin shaidarta da ya qare a ofishin gwamnati da ke wajen Borgo Virgilio.
Bayanai sun nuna cewa, ya yi wa kansa aski sannan ya sanya gashin mata a kansa kamar irin na mahaifiyarsa da ta rasu, kuma ya sanya kayan ado kamar yadda ta saba.
Jaridar ta bayyana cewa, wannan wani sabon salon damfara ce kamar irin na fim xin ‘Mrs Doubtfire’, wanda aka yi a shekarar 1993 da Robin WilliaMis da ya fito a ciki. Mutumin ya bayyana a ofishin gwamnati da ke wajen Mantua a farkon wannan watan, inda aka yi zargin ya bayyana kansa a matsayin Mis Dall’Oglio.
Wani ma’aikacin ma’aikatar fansho ne ya harvo jirginsa, inda ya lura da cewa, akwai alamar tambaya game da ‘matar’ da take neman a canza mata katin. Musamman da yake ya san wacce take da ainihin katin ba ta da kaurin wuya, sannan kuma muryarta ba ta maza ba ce. Wannan ce ta sanya ma’aikacin bai wata-wata ba cikin sauri ya kai rahoto ga ‘yan sanda nan da nan kuma ya sanar da magajin garin Mantua.
’Yan sanda sun ce, da isarsu sai suka kwatanta hotunan Mis Dall’Oglio na gaske da na xanta da ya yi shigar burtu kuma sun fahimci cewa, akwai lauje a cikin naxi.
Bincike ya nuna xan ya karvi kuxin fanshonta na shekaru uku da suka kai kusan Fam 47,000 kuma da mallakar gidaje uku, a cewar rahotanni.
Bayan an kama shi, ‘yan sanda sun je gidansa, inda suka gano gawar Mis Dall’Oglio da aka voye a xakin wanki.
“Ya shigo ofishin ma’aikatar fansho yana sanye da dogon siket, ya yi ado da jan baki da jan-farce da sarqa da ‘yan kunne irin na tsofaffi,” Francesco Aporti, magajin garin Borgo Virgilio ya shaida wa Jaridar Corriere della Sera.
“Amma sai dai yana da kaurin wuya, sannan kuma fatar hannunsa ba ta yi kama da na tsohuwa ‘yar shekara 85 ba.
“Muryarsa kuma ta maza ce duk da yake ya yi shigar mata. Amma da a ce ba a lura da waxannan abubuwa ba da ya ci lalai.”
Da yake magana game da mahaifiyar wanda ake zargin, magajin garin ya ce, “Wataqila ta mutu ne saboda dalilai na rashin lafiya, amma za a tabbatar da hakan ne kawai ta hanyar binciken gawar.” Wannan labari ne mai ban mamaki kuma abin baqin ciki ne qwarai.”
‘Yan sandan Italiya sun ce, gawar mahaifiyar an naxe ta da zanin gado sannan aka saka ta a wata jakar kaya, aka sanya ta cikin firji.
Daga baya ’yan sanda sun xauki gawar zuwa wajen ajiye gawarwaki a asibitin da ke yankin don yin gwajin qwaqwaf da nufin gano musabbabin rasuwarta. Yanzu haka ana binciken mutumin a kan laifukan zamba da voye gawar da ya yi ba bisa qa’ida ba.