Aminiya:
2025-12-07@15:52:53 GMT

Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio

Published: 23rd, October 2025 GMT

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce tsarin zabe a Najeriya ya samu gagarumin ci gaba tun bayan da jam’iyyar PDP ta bar mulkin kasar a matakin tarayya.

Akpabio, wanda aka zabe shi sau biyu a matsayin gwamna karkashin PDP kuma ya fara shiga majalisar dattawa a karkashin jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a lokacin karatu na biyu a kan dokar gyaran tsarin zabe a zaman majalisa da aka yi a ranar Laraba.

Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026

“Ina da tabbacin cewa ni da Sanata Abaribe, wanda muka shafe kusan shekaru 25 muna cikin harkar siyasa, na san ba mu damu da jam’iyya ba, ana iya lashe zabe a ko’ina.

“Ka na da ƙwarewa sosai, amma za ka yarda da ni cewa tun bayan faduwar PDP, zabe ya inganta matuka a wannan ƙasa.

“Na tuna, ina da kusanci da yawancin shugabannin ƙasa tun daga 1999, kuma a 2007 lokacin da na ci zabe a matsayin gwamna, shugaban ƙasa na lokacin, Allah ya jiƙansa, Shugaba Yar’Adua, ya fito fili ya ce zaben da ya kawo shi mulki yana da lam’a.

“Ya ce cike yake da kura-kurai da magudi. Tun daga lokacin, muka fara rufe guraben da ke haifar da matsala.”

Akpabio ya ƙara da cewa duk da cewa ’yan Najeriya na fuskantar ƙalubale, tsarin ya inganta.

“Ka duba zaben da ya gabata, har sai da muka je Kotun Koli muna muhawara kan ko lashe babban birnin tarayya kadai ya isa ya sa dan takara ya zama shugaban ƙasa,” in ji shi.

“Hankali kawai ya isa ya gaya mana cewa ba haka dokar zabe take nufi ba,” in ji Akpabio.

Shugaban majalisar dattawa ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki bayan PDP ta fadi zabe a shekarar 2015.

Ya tsaya takarar Sanata a 2019 a karkashin jam’iyyar APC, amma bai ci ba.

Sai dai tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa shi minista daga bisani, kafin a 2023 kuma ya ci zaben sanatan daga jiharsa ta Akwa Ibom, sannan aka zabe shi shugabancin majalisar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi

Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna, ya rasa ransa bayan fada ya barke a lokacin bikin radin suna a ƙauyen Kwata da ke Karamar Hukumar Warji ta Jihar Bauchi.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da sa’insa ta barke tsakanin wasu matasa ta rikide ta zama fada, wanda ya bar Haruna cikin rashin hayyacinsa.

Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

“Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna na ƙauyen Kwata, Karamar Hukumar Warji, Jihar Bauchi, ya riga mu gidan gaskiya bayan rikici mai tsanani da ya barke a bikin radin suna a ranar 2 ga watan Disamba, 2025,” in ji Zagazola Makama, masani kan harkokin tsaro a yankin arewa maso gabas.

Ya kara da cewa rashin jituwa tsakanin wasu matasa a wajen bikin ta rikide zuwa fada, lamarin da ya bar wanda abin ya shafa ya suma nan take.

An ce an garzaya da Haruna zuwa Asibitin Gwamnati na Warji, amma ya rasu a yayin da ake masa jinya.

Da aka tuntubi mai magana da yawun ’yan sanda na jihar, Ahmed Wakili, ya ce yana cikin taro kuma ya yi alƙawarin dawowa da bayani, sai dai bai yi hakan ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Ya Yi Wani  Hatsari a Neja
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi