Aminiya:
2025-10-21@08:04:01 GMT

Bidiyoyin baɗala: Kotu ta umarci Hisbah ta daura aure tsakanin ’yan TikTok

Published: 21st, October 2025 GMT

Wata kotun majistare da ke Kano ta umarci Hukumar Hisbah ta jihar da ta shirya ɗaura aure tsakanin wasu fitattun ’yan TikTok guda biyu — Idris Mai Wushirya da Basira Yar Guda — cikin kwanaki 60.

Kotun ta bayar da wannan umarnin ne bayan yaɗuwar bidiyon Mai Wushirwa da ’Yar Guda a kafafen sada zumunta, da Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta bayyana a matsayin “na batsa da rahsin tarbiyya.

Bidiyoyin sun nuna waɗannan ’yan TikTok ɗin suna nuna soyayya a bainar jama’a, abin da hukumomi suka ce ya saɓa da ɗabi’u da koyarwar addini da al’adun mutanen Jihar Kano.

A yayin zaman kotun ranar Litinin, Mai Shari’a Halima Wali ta yi gargaɗi cewa idan ba a ɗaura auren cikin lokacin da kotun ta ƙayyade ba, za a ɗauki hakan a matsayin raina kotu.

EFCC ta ƙwato fiye da naira biliyan 500 a shekara biyu — Shetima An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a Kano

Kotun ta kuma umurci Shugaban Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano Jihar Kano da ya tabbatar da aiwatar da wannan umarni na aure.

A makonnin baya an gurfanar da Mai Wushirwa da ’Yar Guda a gaban kotu bisa zargin yi da kuma yaɗa bidiyoyi masu nuna abin da aka bayyana a matsayin “batsa ko rashin kunya” a kafafen sada zumunta.

Tun da farko sai da kotu ta tura Mai Wushirya gidan yari saboda bullar wasu bidiyoyi da suka nuna shi yana aikata abin da hukumomi suka kira “aikata rashin kunya da tauye darajar addini” tare da yarinyar abokiyar aikinsa.

Hukumar tace fina-finai ta jaddada cewa waɗannan bidiyoyi sun karya dokokin jihar da ke haramta samarwa da yaɗa abubuwan da ke da alamar batsa ko rashin kunya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yam TikTok Yar Guda Mai Wushirya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira October 20, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing October 20, 2025 Daga Birnin Sin Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana October 20, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
  • An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a Kano
  • Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a
  • SUBEB Ta Gudanar Da Jarabawa Ga Malaman Da Ke Neman Mukaman Sakatarorin Ilimi A Jigawa
  • Kano Pillars Ta Dakatar Da Babban Kocinta Bisa Rashin Katabus A Kakar Wasa Ta NPFL
  • Kotu A Faransa Ta Yanke Hukumci Zama Gidan Yari Ga Tsohon Shugaban Kasar Nicola Sarkozi
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a Kano
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan kara aure a Kano
  • Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano