Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Zamfara ta  gargaɗi direbobi da sauran jama’a game da rufe lambobin motoci, musamman a cikin garin Gusau, babban birnin jihar.

Gargaɗin ya biyo bayan ƙaruwa da ake samu na rahotanni da kuma lura da direbobi da ke tafiya da lambobin motoci a rufe, wanda rundunar ta bayyana a matsayin karya dokokin hanya da ke kawo barazana ga tsaro da zaman lafiya.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya fitar, rundunar ta bayyana cewa wannan dabi’a tana nuna ƙoƙarin kaucewa binciken jami’an tsaro tare da yiwuwar taimaka wa aikata laifuka.

Sanarwar ta ƙara da cewa, Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya jaddada cewa rundunar ba za ta sake lamuntar irin wannan aiki ba.

Ya bayyana cewa an umarci jami’an rundunar da su fara aiwatar da tsauraran matakan doka, inda ya ƙara da cewa kowace mota da aka samu ta rufe lambar mota za a kama ta tare da gurfanar da mai motar a gaban doka.

CP Maikaba ya kuma shawarci jama’a da direbobi a fadin jihar Zamfara da su bi dokokin hanya tare da yin haɗin kai da ‘yan sanda wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

Ya tabbatar wa jama’a da cewa rundunar ‘yan sandan za ta ci gaba da jajircewa wajen kiyaye doka da oda, tare da ƙarfafa al’umma da su rika ba da rahoton duk wani abin da suke zargi ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

 

Daga Aminu Dalhatu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lambar Mota Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

 

“Wadanda aka nada sun bayyana a gaban kwamitin don tantancewa a ranar Talata, 14 ga Oktoba, 2025,” in ji shi. “Kwamitin bai samu koke ko korafe-korafe ba a kansu, sun nuna shiri da cancanta akan ayyukan da aka zabo su”.

 

Ya bayyana sunayen wadanda aka tantance a matsayin: “Aminu Yusuf (Jihar Neja) – Shugaba, Joseph Haruna Kigbu (Jihar Nasarawa) – Kwamishina, Tonga Betara Bularafa (jihar Yobe) – Kwamishina.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi October 21, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja October 21, 2025 Manyan Labarai An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba October 21, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 2 Wajen Binciken Albarkatun Kasa
  • MTN zai rufe ofisoshi 101 a Kano, Borno da Adamawa saboda gyare-gyare
  • Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal
  • Jihar Kwara Ta Ware Naira Biliyan 8 Don Biyan Haƙƙin Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Borno rufe makarantun jihar saboda rigakafin ƙyanda da Polio
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Hanya Akan Kudi Sama Da Naira Biliyan 4
  • Muna Samun Gagarumin Cigaba Wajen Dawo Da Zaman Lafiya A Zamfara-Gwamna Lawal