Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Sanar Da Wa’adin Biyan Kafin Alkalami Na Shekarar 2026
Published: 22nd, October 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna ta yi kira ga Maniyyata Aikin Hajjin 2026 da su biya kafin alkalami nan da ranar 14 ga watan Nuwamban 2025.
Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Ibrahim Datti ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba 22 ga watan Oktoban 2025.
Hukumar wacce ta ce kudin kama kujerar kar su gaza Naira Miliyan Biyu, ta ce Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON, na kokarin sama wa Maniyyata rangwame bisa kudin kujera da ta sanar a baya.
Ta kara da cewa duk wanda bai biya ba kafin karshen wa’adin da ta bayar, ba zai sami kujerar Aikin Hajjin Bana ba.
Har ila yau Hukumar ta ce Maniyyata za su iya yin rajista a ofisoshinta da ke sakatariyar Kananan Hukumomi 23 na Jihar Kaduna, ko kuma hedikwatar hukumar a kan titin Katsina, da ke cikin garin Kaduna.
Hukumar ta kuma ja kunnen Maniyyata da su guji yin mu’amala da duk wanda ba ma’aikacinta ba, tare da gujewa bai wa kowa kudadesu a hannu.
Rel/Safiyah Abdulkadir
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai
এছাড়াও পড়ুন:
Bidiyoyin baɗala: Kotu ta umarci Hisbah ta daura aure tsakanin ’yan TikTok
Wata kotun majistare da ke Kano ta umarci Hukumar Hisbah ta jihar da ta shirya ɗaura aure tsakanin wasu fitattun ’yan TikTok guda biyu — Idris Mai Wushirya da Basira Yar Guda — cikin kwanaki 60.
Kotun ta bayar da wannan umarnin ne bayan yaɗuwar bidiyon Mai Wushirwa da ’Yar Guda a kafafen sada zumunta, da Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta bayyana a matsayin “na batsa da rahsin tarbiyya.”
Bidiyoyin sun nuna waɗannan ’yan TikTok ɗin suna nuna soyayya a bainar jama’a, abin da hukumomi suka ce ya saɓa da ɗabi’u da koyarwar addini da al’adun mutanen Jihar Kano.
A yayin zaman kotun ranar Litinin, Mai Shari’a Halima Wali ta yi gargaɗi cewa idan ba a ɗaura auren cikin lokacin da kotun ta ƙayyade ba, za a ɗauki hakan a matsayin raina kotu.
EFCC ta ƙwato fiye da naira biliyan 500 a shekara biyu — Shetima An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a KanoKotun ta kuma umurci Shugaban Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano Jihar Kano da ya tabbatar da aiwatar da wannan umarni na aure.
A makonnin baya an gurfanar da Mai Wushirwa da ’Yar Guda a gaban kotu bisa zargin yi da kuma yaɗa bidiyoyi masu nuna abin da aka bayyana a matsayin “batsa ko rashin kunya” a kafafen sada zumunta.
Tun da farko sai da kotu ta tura Mai Wushirya gidan yari saboda bullar wasu bidiyoyi da suka nuna shi yana aikata abin da hukumomi suka kira “aikata rashin kunya da tauye darajar addini” tare da yarinyar abokiyar aikinsa.
Hukumar tace fina-finai ta jaddada cewa waɗannan bidiyoyi sun karya dokokin jihar da ke haramta samarwa da yaɗa abubuwan da ke da alamar batsa ko rashin kunya.