Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Published: 25th, October 2025 GMT
Ya bayyana cewa sarakuna suna taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba, musamman a fannin ilimi, inda ya ce zai tabbatar yara sun koma makaranta.
Haka kuma, ya ce zai goyi bayan gwamnati a ɓangaren kiwon lafiya da tsaro, domin inganta rayuwar jama’a.
Sabon Sarkin, wanda kuma shi ne shugaban hukumar kula da ilimi a matakin farko (SUBEB) ta Jihar Bauchi, ya bayyana farin cikinsa da godiyarsa ga Allah da Gwamna Bala Muhammad saboda wannan dama da ya samu.
Ya yi alƙawarin yin aiki tuƙuru domin ci gaban masarautarsa da Jihar Bauchi gaba ɗaya, tare da kira ga jama’ar Duguri da su haɗa kai wajen gina masarautar.
“Mu mutanen Duguri a shirye muke mu taimaka wa gwamnati a duk abin da ta ce. Za mu tura yara makaranta, za mu karɓi rigakafi, kuma za mu ci gaba da zaman lafiya da maƙwabtanmu. Muna godiya sosai ga Gwamna Bala Muhammad bisa wannan dama,” in ji Sarki Adamu.
Sarkin ya bai wa Gwamnan Bauchi sarautar ‘Yariman Duguri.
Da yake miƙa takardar naɗin sarautar, Sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi, Aminu Hammayo, ya ce Gwamna Bala Muhammad ya yi amfani da dokar masarautu ta shekarar 2025, musamman sashe na 16 da 17, wajen tabbatar da wannan naɗi.
Ya tunatar da sabon Sarki da ya tafiyar da harkokin masarautar bisa kundin tsarin mulkin ƙasa, dokokin Jihar Bauchi, da umarnin gwamnati, tare da tabbatar da adalci da gaskiya a shugabancinsa.
Gwamnan ya yi fatan sabon Sarkin zai jagoranci masarautar cikin zaman lafiya, haɗin kai, da samar wa al’ummar Duguri da Bauchi ci gaba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Jihar Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan kubutar da yan makaranta 100 daga cikin wadanda ‘yan ta’adda suka sace a wata makaranta a jihar Naija a cikin watan Nuwamban da ya gabatata.
Tashar talabijan ta almayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto kamfanin dillancin labaran reuters na cewa jami’an tsaron kasar sun sami nasarar kubutar da yan makaranta har 100 daga cikin wadanda yan ta’adda suka sacesu a wata makarantar cocin Khatolica a cikin jihar Naija.
Kafin haka an ce yara kimani 50 sun tsere daga hannun yan ta’addan bayan an sacesu.
Tashar talabijin ta ‘Chennel TV ‘ ta bada labarin cewa sakin yan makarantan, amma bata nuna hotunansu ba kuma bata yi wani karin bayani ba.
Sannan kungiyar kiristoci ta Najeriya a jihar Naija ta bada sanarwan cewa wau yan bindiga sun sace yara 12, a ranar 21 ga watan Nuwamban da ya gabata, a makarantar Sianth Mary a garin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025 Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci