Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Published: 20th, October 2025 GMT
Sinawa kan ce, bisa mataki mataki ake yin tafiya tsawo. Lallai nasarorin da kasar Sin ta cimma, sun faru ne sakamakon yadda al’ummomin kasar suka hada karfi da karfe a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma suka yi ta yin kokari ba tare da kasala ba bisa shirye-shiryen raya kasa da gwamnati ta tsara na shekaru biyar biyar.
In an yi nazari a kan tsarin shirye-shiryen raya tattalin arziki da zaman al’umma na kasar Sin na shekaru biyar biyar, to, za a fahimci yadda kasar Sin ke gudanar da harkokinta. Tsarin ya shaida mana wata hanyar zamantar da kasa da ta sha bamban da ta kasashen yammacin duniya, wanda ya samar da darasi abin koyi ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa wajen gaggauta bunkasa ayyukan masana’antunsu.
A bana ne ake kammala aiwatar da shirin bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma na shekaru biyar biyar karo na 14 a kasar Sin. Daga yau Litinin 20 ga wata har zuwa ranar Alhamis 23 ga wata, za a gudanar da cikakken zama karo na hudu na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 20, inda za a fi mai da hankali a kan tattauna shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, don tabbatar da taswirar raya kasar cikin shekaru biyar masu zuwa, wato daga 2026 zuwa 2030. Mene ne alkiblar bunkasar kasar Sin nan da shekaru biyar masu zuwa, kuma wadanne damammaki ne kasar za ta samar wa duniya? Ba shakka, taron zai ba mu amsa. Sai dai abin da muke da tabbaci a kai tun yanzu shi ne, kasar Sin za ta kare niyyarta ta fadada bude kofarta ga duniya, kuma za ta kare niyyarta ta samar da damammaki ga kasashen duniya, haka kuma za ta kare niyyarta ta inganta dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya yadda ya kamata don a ci moriyar juna da kuma samun nasara tare.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA
কীওয়ার্ড: na shekaru biyar biyar kasar Sin na a kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bayyana Cewa: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Kuduri mai lamba 2231 ya ƙare aiki a yau
A cikin wata wasika da ya aike wa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ministan harkokin wajen kasar Iran ya tabbatar da cewa a karshe kuduri mai lamba 2231 ya kare a yau, kuma duk wani kira na farfado da shi ko dawo da wa’adin kudirorin da ya kare, ba shi da wani tushe na shari’a, kuma ba zai iya haifar da wani tasiri na tilasta aiki da shi ba.
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Sayyid Abbas Araqchi ya aike da wasika zuwa ga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da kuma shugaban kwamitin sulhu dangane da kawo karshen kuduri mai lamba 2231. Wasikar ta bayyana cewa: A ci gaba da wasikun da ya aike a baya, ciki har da na baya-bayan nan na ranar 27 ga watan Satumba 2025, daga karshe ya sanar da cewa, kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kawo karshen kuduri mai lamba 2231, daidai da ƙayyadaddun tanadinsa.
A cikin wannan wasika na nanata matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran kamar haka: Shekaru 10 da suka gabata, shirin hadin gwiwa na hadin gwiwa (JCPOA) ya fara aiki tare da amincewa da kuduri mai lamba 2231 (2015), yana mai nuni da imanin da kasashen duniya ke da shi cewa diflomasiyya da cudanya tsakanin bangarori daban-daban su ne mafi inganci hanyoyin warware rikice-rikice.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran, Rasha, Da China Sun Jaddada Rashin Halaccin Dawo Da Tsohon Takunkumi Kan Iran October 18, 2025 Masani Kan Harkokin Tsaro Ya Ce: Makami Mai Linzamin Iran Kirar Ghadir Ya Aike Da Sako Ga Isra’ila October 18, 2025 Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: An Rusa Gaza Gaba Daya October 18, 2025 Joseph Kabila Ya Koma Kasarsa Domin Kalubalantar Hukuncin Kisa Da Aka Yanke Kansa October 18, 2025 Gaza Ta Bukaci A Binciki Isra’ila Kan Sace Sassan Jiki A Gawarwakin Falasdinawa October 18, 2025 Hamas Ta Bukaci A Kafa Kotun Kasa Da Kasa Kan Gawarwarkin Da Isra’ila Ta Dawo Mata Da Su. October 18, 2025 Madagascar : An rantsar Da Michael Randrianirina A Matsayin Shugaban Kasar October 18, 2025 Iran Ta yi Tir Da Harin da Isra’ila Ta kai Kudancin Kasar labanon. October 18, 2025 Majalisar Dattawa Za Ta Gana Da Ministan Ilimi Kan Batun Yajin Aikin Asuu. October 18, 2025 Gaza ta bukaci a binciki Isra’ila kan sace sassan jiki a gawarwakin falasdinawa October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci