Sinawa kan ce, bisa mataki mataki ake yin tafiya tsawo. Lallai nasarorin da kasar Sin ta cimma, sun faru ne sakamakon yadda al’ummomin kasar suka hada karfi da karfe a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma suka yi ta yin kokari ba tare da kasala ba bisa shirye-shiryen raya kasa da gwamnati ta tsara na shekaru biyar biyar.

Shirye-shiryen cike suke da burikan da kasar Sin ke neman cimmawa, wadanda kuma suka shaida kokarin da al’ummar kasar suka yi da ma wahalhalun da suka sha. Idan aka fara wani sabon shirin, to, an bude sabon babi na bunkasa kasar ke nan. Ma iya cewa, tarihin shirye-shiryen raya tattalin arziki da zaman al’umma na kasar Sin na shekaru biyar biyar, tamkar tarihin bunkasuwar kasar Sin ne.

 

In an yi nazari a kan tsarin shirye-shiryen raya tattalin arziki da zaman al’umma na kasar Sin na shekaru biyar biyar, to, za a fahimci yadda kasar Sin ke gudanar da harkokinta. Tsarin ya shaida mana wata hanyar zamantar da kasa da ta sha bamban da ta kasashen yammacin duniya, wanda ya samar da darasi abin koyi ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa wajen gaggauta bunkasa ayyukan masana’antunsu.

 

A bana ne ake kammala aiwatar da shirin bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma na shekaru biyar biyar karo na 14 a kasar Sin. Daga yau Litinin 20 ga wata har zuwa ranar Alhamis 23 ga wata, za a gudanar da cikakken zama karo na hudu na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 20, inda za a fi mai da hankali a kan tattauna shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, don tabbatar da taswirar raya kasar cikin shekaru biyar masu zuwa, wato daga 2026 zuwa 2030. Mene ne alkiblar bunkasar kasar Sin nan da shekaru biyar masu zuwa, kuma wadanne damammaki ne kasar za ta samar wa duniya? Ba shakka, taron zai ba mu amsa. Sai dai abin da muke da tabbaci a kai tun yanzu shi ne, kasar Sin za ta kare niyyarta ta fadada bude kofarta ga duniya, kuma za ta kare niyyarta ta samar da damammaki ga kasashen duniya, haka kuma za ta kare niyyarta ta inganta dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya yadda ya kamata don a ci moriyar juna da kuma samun nasara tare.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025 Ra'ayi Riga Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa October 12, 2025 Ra'ayi Riga Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka October 7, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: na shekaru biyar biyar kasar Sin na a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya soke iyakance adadin kuɗin da mutum ko kamfani za su iya ajiyewa a banki sannan ya ƙara yawan kudin da za a iya fitarwa a mako da ₦100,000 zuwa ₦500,000.

Wannan na cikin wata sanarwa da Daraktar Sashen Tsarin Kuɗi da Dokoki ta bankin, Dr. Rita Sike, ta sanya wa hannu kuma ta fitar ranar Laraba.

Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi

A cewar bankin, an yi sauye-sauyen manufofin ne da nufin rage tsadar sarrafa kuɗi, magance matsalolin tsaro, da kuma dakile haɗarin safarar kuɗi ba bisa ka’ida ba da ke da alaƙa da dogaro da mu’amalar kuɗi kai tsaye.

CBN ya ce manufofin da suka gabata kan kuɗi an gabatar da su ne domin rage amfani da kuɗi kai tsaye da ƙarfafa amfani da hanyoyin biyan kuɗi ta intanet.

Sai dai, sauye-sauyen tattalin arziki da na gudanarwa sun sa dole a sake duba dokokin domin daidaita su da halin da ake ciki a yanzu.

Daga ranar 1 ga watan Janairun 2026, an soke iyakance adadin kuɗin da za a iya ajiye gaba ɗaya, kuma ba za a sake cajin kuɗin da ake ɗauka a kan ajiya mai yawa ba.

Sabbin dokokin sun jingine iyakance fitar kuɗi na mako gaba ɗaya ga mutum ɗaya zuwa ₦500,000, yayin da na kamfanoni ya koma ₦5m.

Kazalika, dokar ta ce fitar kuɗin da ya wuce waɗannan iyakokin zai jawo ƙarin caji na kaso cikin 100 ga mutum ɗaya da kuma kaso biyar cikin 100 ga kamfanoni, inda za a raba kuɗin da aka tara da bankuna bisa tsarin 40:60 tsakanin CBN da bankunan da abin ya shafa.

CBN ya kuma umarci bankuna da su tabbatar da cewa sun saka dukkan nau’o’in kuɗi a cikin na’urar ATM domin sauƙaƙa samun kuɗi.

Babban bankin ya kuma umarci bankuna da su rika gabatar da rahoton wata-wata ga Sashen Kula da Bankuna, Sashen Kula da Sauran Hukumomin Kuɗi, da Sashen Kula da Tsarin Biyan Kuɗi domin tabbatar da bin doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  •  An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • MDD ta bukaci a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma janyewa daga Tuddan Golan na Siriya
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa
  • Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau