Albanese: Wajibi A Kawo Karshen Gwamnatin Mamaya A Falasdinu
Published: 23rd, October 2025 GMT
Jami’ar mai aikin tsarawa MDD rahoto akan Falasdinu Farencesca Albanese ta bayyana cewa; tsagaita wutar yaki da aka yi a Gaza, bai wadatar ba, wajibi ne a kawo karshen tsarin mamaya a Falasdinu.
Albanese ta kuma ce Amurka ce take bai wa ‘yan mamaya cikakken goyon baya a kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu,don haka ya zama wajibi a kawo karshen yadda ‘yan mamayar suke sarrafa albarkatun al’ummar Falasdinu,sannan kuma a tarwatsa tsarin mulkin mallaka na mamaya.
A halin da ake ciki a yanzu dai Albanese tana kasar Afirka Ta Kudu, inda take halartar taron shekara-shekara akan “Nelson Mandela” za kuma ta gabatar da jawabai a wurin.
Tun a cikin watan Mayu ne dai Amurka ta kakawa ma’aikaciyar MDD takunkumi saboda matsayarta ta sukar HKI akan laifukan yaki da kuma kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rasha: Shugaba Putin Ya Sa Ido Akan Atisayen Rundunar Nukiliyar Kasar October 23, 2025 Shugaban Kasar Amurka Ya Soke Shirin Ganawa Da Takwaransa Na Kasar Rasha October 23, 2025 Venezuela Ta Sanar Da Mallakar Makamai Masu Linzami Samfurin “ Igla-s” 5,000 Domi Kare Kanta October 23, 2025 Jagora: Allamah Na’ini Ya Kasance Ma’abocin Ilimi Da Sanin Siyasa October 23, 2025 Kimanin Bakin Haure 40 Ne Suka Mutu A Kokarin Ketare wa Turai Ta Tekun Mediterranean October 23, 2025 Hamas Tayi Maraba Da Karyata Ikirarin Isra’ila da Kotun Duniya ICJ Tayi Kan UNRWA October 23, 2025 Alkalai Sun Yi Watsi Da Karar Da Yan Adawa Suka Shigar Kan Zargin Magudi A Zaben Kamaru October 23, 2025 Yahudawa A Kasashen Duniya Sunyi Kira Ga M D D Da Ta Kakabawa Isra’ila Takunkumi October 23, 2025 Ministan Leken Asiri: Iran Bata Da Tabbacin Kare Maslaharta A Tattaunawa Da Amurka. October 23, 2025 ICJ : Isra’ila ta karya dokokin duniya wajen hana shigar da kayan agaji a Gaza October 23, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Alkalai Sun Yi Watsi Da Karar Da Yan Adawa Suka Shigar Kan Zargin Magudi A Zaben Kamaru
Alkalan kotu a Kamaru sun yi watsi da bukatar da jamiyyun adawa suka ka gabatar masu ta neman ko dai su soke wasu sakamakon zaben shugaban kasar ko kuma su soke zaɓen baki daya, inda suka ce za su sanar da sakamako a ranar Litinin, sai dai ta dage lokacin daga baya.
Zanga-zanga ta barke a wasu manyan biranen kasar, inda ƴan adawa suka yi zargin an tafka kura-kurai a zaɓen na ranar 12 ga watan Oktoba.
Alkalan kotun tsarin mulki sun yi watsi da korafi har takwas da aka gabatar masu, domin a cewar su babu cikakkiyar shaida mai tabbatar da su.
Dan takarar ƴan adawa, Issa Tchiroma Bakary ya bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaben, wani ikirari da shugaba Paul Biya mai shekara 92 a duniya, wanda kuma ke neman wa’adin mulki na bakwai.
chiroma Bakary mai shekara 76 da haihuwa, tsohon kakakin gwamnatin Biya ne, wanda a yanzu yake neman kwace mulki a hannunsa.
Ya ki yarda ya tura nasa korafin zuwa kotun kundin tsarin mulkin kasa, ya zabi ayyana kansa a matsayin ”Halartacce shugaban kasa.
A wani sako da ya fitar a shafukan sada zumunta, Tchiroma Bakary ya ce ya lashe zaben bayan samun kashi 55 cikin dari na jimillar kuri’un da aka kada.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yahudawa A Kasashen Duniya Sunyi Kira Ga M D D Da Ta Kakabawa Isra’ila Takunkumi October 23, 2025 Ministan Leken Asiri: Iran Bata Da Tabbacin Kare Maslaharta A Tattaunawa Da Amurka. October 23, 2025 ICJ : Isra’ila ta karya dokokin duniya wajen hana shigar da kayan agaji a Gaza October 23, 2025 Amurka : Shirin Isra’ila na mamaye yammacin kogin Jordan, barazana ne ga tsagaita wuta a Gaza October 23, 2025 Iran ta yi maraba da hukuncin kotun faransa na yi wa Esfandiari saki bisa sharadi October 23, 2025 Kamaru: Sai ranar Litinin za’a bayyana wanda ya lashe zaben shugaban kasa October 23, 2025 Gaza : Sabani tsakanin Isra’ila, Amurka da Masar kan mataki na biyu na tsagaita wuta October 23, 2025 Araqchi: Akwai Sharuddan Da Iran Ta Gindaya Kafin Sake Komawa Kan Teburin Tattaunawa Da Amurka October 22, 2025 Mai Ba Da Shawara Kan Harkokin Tsaron Iraki Ya Gana Da Hafsan Hafsoshin Sojojin Kasar Iran October 22, 2025 Kasar Iran Ta Kai Hare-Hare A Wuraren Da Kawayen Isra’ila Ba Su San Da Su ba A Lokacin Yakin Kwanaki 12 October 22, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci