Majalisar dokokin jihar Yobe, ta yi kira ga bangaren zartarwa na gwamnatin jihar da ta dauki matakan gaggawa domin magance yawaitar haduran ababen hawa a garuruwan Ngelzarma, Damagum da Dogon Kuka da ke kan hanyar Damaturu zuwa Potiskum.

Majalisar ta yi wannan kiran ne bayan gabatar da kudiri da dan majalisa mai wakiltar mazabar Damagum, Maina Digma Gana, ya yi kan yawaitar hadura a wadannan garuruwa.

Waɗanda ke son rusa Kano ba za su yi nasara ba — Sanusi II MTN zai rufe ofisoshi 101 a Kano, Borno da Adamawa saboda gyare-gyare

Gana, ya bayyana cewa yawaitar haduran ababen hawa a yankin abun damuwa ne, don haka ya zama wajibi gwamnati ta dauki mataki don kare rayukan jama’a.

Ya kara da cewa daga watan Janairun 2025 zuwa yanzu, sama da mutane 30 ne suka rasa rayukansu a garin Damagum sakamakon haduran ababen hawa a hanyar Damaturu zuwa Potiskum.

Dan majalisar, ya bukaci gwamnatin jihar da ta gina shatale-tale a Damagum tare da samar da wasu matakan rage gudun mota a titunan da suka ratsa garuruwan Ngelzarma da Dogon Kuka.

Ya ce hakan zai taimaka wajen rage gudu da direbobi ke yi, wanda shi ne ke janyo yawan hadura da asarar rayuka.

Da yake goyon bayan kudirin, shugaban masu rinjaye na majalisar, Nasiru Hassan Yusuf, wanda ke wakiltar mazabar Damaturu, tare da dan majalisa mai wakiltar mazabar Karasuwa, Adamu Dala Dogo, sun bukaci hukumar kiyaye hadura ta kasa (FRSC) da hukumar YOROTA su kara wayar da kan direbobi kan illar tuƙin ganganci da gudun wuce kima.

Kakakin majalisar , Rt. Honarabul Chiroma Buba Mashio, ya yi kira ga ’yan majalisar da ke wakiltar al’umma a majalisun tarayya da su gabatar da lamarin a gaban majalisar dokokin kasa, domin samun guiwar gwamnatin tarayya wajen magance matsalar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hanya hatsarin mota Majalisar Dokokin Yobe yawaitar hadura

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Nemi Alkalai Su Kara Kaimi Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukaci Alkalan Najeriya su kasance masu gaskiya, rikon amana da tsoron Allah wajen yanke hukunci. Ya ce duk wata al’umma tana fara rushewa ne idan bangaren shari’a ya lalace.

Ya bayyana cewa gwamnati na kokarin inganta walwala da albashin Alkalan domin karfafa ikon cin gashin kansu.

Da yake bude taron bita na EFCC da NJI a Abuja, Shugaban  wanda Mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta  ya ce adalcin Alkalai ne ginshikin ci gaban kasa.

Ya nuna damuwa kan yadda ake jinkirta shari’o’in manyan laifukan rashawa, yana mai cewa an fi hanzarta shari’ar masu laifin yanar gizo.

Shugaba Tinubu ya jaddada cewa ba a taba kare kowa saboda siyasa a gwamnatinsa ba, inda ya bayyana cewa EFCC ta samu nasarar gurfanar da mutane sama da 7,000 tare da karbo kadarori fiye da Naira Biliyan 500 cikin shekaru biyu.

Ya bukaci Alkalan su ci gaba da koyon sabbin dabaru, musamman wajen shari’o’in yanar gizo da laifukan kuɗi, tare da tunatar da su cewa cin hanci yana shafar kowa.

A nata bayanin Babbar Alkalin Najeriya, Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta bukaci Alkalan su tabbatar da yin adalci ba tare da jinkiri ko son zuciya ba.

Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, ya yaba da hadin kan da Alkalan je basu, yana mai cewa nasarorin da aka samu sun nuna jajircewa wajen yaki da cin hanci da rashawa.

 

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Najeriya Ta Amince Da Dokar Daurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Kananan Yara Fyade
  • Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya
  • Fashewar tankar mai ta yi ajalin mutum 30 a Neja
  • Kakakin Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Babu Wata Tattaunawa Da HKI
  • Muna Samun Gagarumin Cigaba Wajen Dawo Da Zaman Lafiya A Zamfara-Gwamna Lawal
  • Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Karbi Bakwancin Takwaransa Na Iraki
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro
  • Tinubu Ya Nemi Alkalai Su Kara Kaimi Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa
  • Grossi: Za a iya warware batun Shirin nukiliyar Iran ne kawai ta hanyar diflomasiyya