Pezeshkian: Iran za ta gwammace takunkumi a kan mika wuya
Published: 24th, October 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce kasarsa za ta gwammace ta fuskanci takunkumin maimakon mika wuya ga manufofin ‘yan mulkin malla.
“Mun cimma yarjejeniya da bangarori na Turai, amma ra’ayin Amurka ya bambanta, kuma abu ne na hankali kan cewa Iran ba zata mika wuya ga dukkanin abin da Amurka take bukata ba, domin hakan ya yi hannun riga da maslahar Iran.
Amurka da kawayenta, wadanda ake kira da E3, sun ki amincewa da wani daftarin kuduri daga Rasha da China, wanda ya nemi jinkirta aiwatar da tsarin dawo da takunkumai kan Iran a karkashin yarjejeniyar nukiliya ta JCPOA.
Pezeshkian ya kara da cewa Amurkawa “suna son mu ba su dukkan sinadarin uranium da aka tace, wanda ba za a amince da shi ta kowace hanya ba.”
Shugaban na Iran ya nanata cewa da alama Amurka za ta matsa kaimi don “fara mayar da martani” na takunkumin a cikin watanni masu zuwa, yana mai kara jaddada cewa idan aka tilastawa Iran yin zabi, to za ta zabi abin da ya dace da maslaharta da al’ummarta, maimakon biyan bukatar da ta yi hannun riga da maslahar kasa, yana mai shan alwashin cewa “duk da haka, za mu magance dukkan matsalolinmu.”
Ya ba da tabbacin cewa, an dauki matakan da suka wajaba don wannan yanayin, yana mai nuni da kawancen Iran da kasashe makwabta, BRICS, da kasashen kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, da kuma juriyar al’ummar Iran, duka za su taimaka wajen shawo kan wannan lamarin.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump: Amurka na shirin kai hare-hare a Venezuela October 24, 2025 Ivory Coast: Ayyukan ma’adinai na fuskantar tsaiko yayin da Ouattara ke neman wa’adi na 4 October 24, 2025 Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi October 24, 2025 Larabawan Yankin Tekun Fasha Sun Caccaki Sabon Shirin Isra’ila A Kan Yammacin Kogin Jordan October 24, 2025 Albanese: Wajibi Ne A Kawo Karshen Gwamnatin Mamaya A Falasdinu October 23, 2025 Rasha: Shugaba Putin Ya Duba Atisayen Rundunar Nukiliyar Kasar October 23, 2025 Shugaban Amurka Ya Soke Shirin Ganawa Da Takwaransa Na Rasha October 23, 2025 Venezuela Ta Sanar Da Mallakar Makamai Masu Linzami Samfurin “ Igla-s” 5,000 Domin Kare Kanta October 23, 2025 Jagora: Allamah Na’ini Ya Kasance Ma’abocin Ilimi Da Sanin Siyasa October 23, 2025 Kimanin Bakin Haure 40 Ne Suka Mutu A Kokarin Ketarawa Turai Ta Tekun Mediterranean October 23, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa har yanzu Amurka ba ta nuna sha’awarta ta shiga “tattaunawa mai ma’ana ba,” yana mai sake nanata cewa dole ne Washington ta fara amincewa da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya na zaman lafiya a karkashin Yarjejeniyar hana yaduwar Makaman Nukiliya ta (NPT).
A wata hira ta musamman da aka yi da kamfanin dillancin labarai na Japan Kyodo a ranar Asabar, ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa an kaiwa cibiyoyin nukiliya na Jamhuriyar Musuluncihari da bama-bamai, wanda ya lalata su sosai” a lokacin harin Isra’ila da Amurka a watan Yuni.
Araghchi ya jaddada cewa wadannan hare-haren sun kasance “wataƙila mafi girman keta dokokin kasa da kasa” da aka taba yi wa wata cibiya da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ke sa ido a kai.
Ministan harkokin wajen na Iran ya ce Jamhuriyar Musulunci da IAEA sun cimma yarjejeniya a birnin Alkahira a farkon wannan shekarar da zata duba wuraren da suka lalata.
Duk da haka, wannan tsari ya shiga cikin matsala lokacin da Amurka da kasashen Turai uku da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar nukiliya ta 2015 suka nemi a dawo da takunkumin da Majalisar Tsaron Majalisar Dinkin Duniya ta sanya wa Iran a baya.
Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya kara da cewa babbar matsalar ita ce rashin amincewar Washington da ‘yancin Iran na mallakr fasahar nukiliya ta zaman lafiya, gami da wadatarwa, a karkashin NPT.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci