A yau Alhamis 23 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya karyata wani rahoto na zuki-ta-malle da wata cibiyar bincike ta Amurka ta bayar kan hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da Afirka ta Yamma. Ya yi nuni da cewa, rahoton ya kawo rudani ga ra’ayoyi na kaifin basira, sannan daga bangare guda kawai aka tattaro shi, kuma har ma ya ruwaito wasu bayanan da ba a tantance ba, tare da shafa kashin kaji da kuma muzanta hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da kasashen yammacin Afirka.

Wannan ya kasance wani bakon abu a fili kuma abin kyama.

An ba da rahoton cewa, cibiyar nazarin al’amura ta Amurka ta Atlantic Council, ta fitar da rahotanni da dama a baya-bayan nan, inda ta bayyana cewa, ayyukan hakar ma’adinai, da gandun dazuzzuka da kamun kifi da kasar Sin ke yi a yammacin Afirka, sun haifar da mummunar illa ga muhallin halittu, tare da yin kira ga yankin yammacin Afirka da ya ba da hadin kai wajen karfafa sa ido kan lamarin.

A yayin da yake mayar da martani, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin na gudanar da hadin gwiwa da kasashen Afirka bisa ka’idojin gaskiya, da zuciya daya da kyakkyawar manufa, da kuma kyakkyawan ra’ayi na adalci da cin moriya, don ba da gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin Afirka da samun habaka mai dorewa, wanda gwamnatoci da jama’ar Afirka suka yi maraba da su.

Ya kara da cewa, babban abin da Afirka ke sha’awa na yin hadin gwiwa da kasar Sin shi ne bayar da misali ta fuskar samun moriyar juna da samun nasara ga bangarorin biyu. A ko da yaushe, gwamnatin kasar Sin tana bukatar kamfanonin kasar Sin da ofisoshin kasuwanci na ketare da su mutunta dokokin da suka dace da hakan. Har ila yau, za ta ci gaba da jagorantar masana’antu don aiwatar da manufar bunkasa muhalli, da shigar da kiyaye muhalli a cikin dukkan matakan tsarin hadin gwiwar Sin da Afirka. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15 October 23, 2025 Daga Birnin Sin Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka October 22, 2025 Daga Birnin Sin Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11 October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Godewa Rasha Game Da Goyon Bayan Da Ta Bata A Kwamitin Sulhu Na M D D

Babban jam’in hukumar tsaro ta kasar iran ya bayyana jin dadin kasar iran ga kasar Rasha saboda goyon bayan da ta bata a kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya kan hakkin iran a gaban kasashen turai dake kokarin kakkaba mata sabon takunkumin karya tattalin Arziki,

Babban sakataren tsaro na kasar Iran Dr Ali Larijani ya fadi hakan ne a jiya talata A wata ganawa da yayi da jakadan shugaban kasar Rasha Alexander Lavrentiev da ya kawo ziyara nan kasar iran , larijani a matsayinsa na mai bawa jagora shawara ya jinjinawa kasar rasha game da goyon bayan da take bawa kwamitin.

LarIjani da sauran jami’an gwamnatin kasar Rasha sun yi bitar matakin hadin guiwa dake tsakanin Tehran da mosko a matakin kasa da kasa da kuma sauran bangarorin daban daban na ci ba a yankin,

Jakadan ya bayyanawa jami’an gwamnatin kasar iran  yanayin da ake ciki a yankin  a baya bayan nan, da kuma hanyoyin da za’a bi wajen kara karfi don  yin aiki tare. Kuma zaman ya zo ne yan kwanaki bayan da larijani ya gana da shugaban kasar Rasha viladmir putin a mosko inda ya mika masa sakon jagora kai tsaye.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sudan: Jirgin ‘Drone’ Ya Fada Kan Tashar Jiragen Sama Na Khurtum Kafin A Sake Bude Ta October 22, 2025 Sheikh Qasim: Natanyahu Ya Zubar Da Jini Mai Yawa Amma Babu Lamuni Ga Amincin Isra’ila Nan Gaba October 22, 2025 Aragchi Da Guterres Sun Tattauna Kan Gaza Da Rikicin Yemen Ta Wayar Tarho October 22, 2025 Rasha da Habasha sun tattauna kan karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu a fannin nukiliya October 22, 2025 Sayyed al-Houthi: Mun shirya dawowa fagen daga idan Isra’ila ta ci gaba da kisan kiyashi a Gaza October 22, 2025 Nigeria: “Yan Sanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Neman Sakin Jagoran ‘Yan Awaren Biafara October 21, 2025 HKI Tana Ci Gaba Da Hana Wa Falasdinawa Abinci October 21, 2025 An Yi Fashi Da Makami A Gidan Adana Kayan Tarihin  ” Louvre” Na Kasar Faransa October 21, 2025 Yemen : An yi jana’izar babban hafsan sojin kasar Shahid al-Ghamari a Sana’a October 21, 2025 Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza October 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Trump Ya Dakatar Da Tattaunawar Kasuwanci Da Kasar Canada
  • Larabawan Yankin Tekun Fasha Sun Caccaki Sabon Shirin Isra’ila A Kan Yammacin Kogin Jordan
  • Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
  • Amurka : Shirin Isra’ila na mamaye yammacin kogin Jordan, barazana ne ga tsagaita wuta a Gaza
  • Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
  • Iran Ta Godewa Rasha Game Da Goyon Bayan Da Ta Bata A Kwamitin Sulhu Na M D D
  • Rasha da Habasha sun tattauna kan karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu a fannin nukiliya
  • Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
  • Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya