Jagoran Ya Mayar Da Martani Ga Trump Cewa; Su Ci Gaba Da Mafarkinsu
Published: 20th, October 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga shugaban Amurka Trump cewa: su ci gaba da mafarkinsu!
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei a yayin da yake tsokaci kan kalaman shugaban Amurka a yayin ziyarar da ya kai yankunan da aka mamaye, ya ce Trump cikin alfahari ya ce kasarsa ta yi luguden bama-bamai tare da lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, yana mai mayar msa da martani cewa: “To, su ci gaba da yin mafarkinsu!”
A yayin ganawarsa da safiyar yau da zakaran wasanni kuma wadanda suka lashe gasar Olympics ta kasa da kasa, Jagoran ya kara da cewa: Duk abin da kuke yi ana danganta shi da Iran da kuma al’ummar kasar ne, kuma wannan tuta da zakarun Iran suka daga yana da matukar kima, kamar yadda sujjadar godiya da addu’o’in da dan wasan kasar Iran ya yi bayan samun nasara wata kyakkyawar alama ce ta al’ummar Iran.
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya yi ishara da muhimmancin tallafawa matasa masu hazaka yana mai cewa: Wadannan matasa da suke halartar gasar Olympics ta kimiyya, taurari ne masu haskawa a yau, amma nan da shekaru goma za su haskaka rana idan suka ci gaba da aiki da kokari, y ace: Yana kuma kira ga jami’ai da kada su yi watsi da wadannan matasa, kuma kada su gamsu da abin da suka samu ya zuwa yanzu, sai dai suna shimfidar hanyar ci gaba mai bunkasa ce.
Ya kara da cewa, “Idan tauraro ya ci gaba da tafiya, nan da shekaru goma zai zama rana mai haskaka wa wasu hanya, kuma ta hanyarsu za a iya cimma manyan ayyuka.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Yin Riko Da Hakkokin Kasarta October 20, 2025 Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Karbi Bakwancin Takwaransa Na Iraki October 20, 2025 Wakilin Amurka Na Musamman A Siriya Ya Matsa Don Ganin Kasashen Saudiyya Da Lebanon Da Kuma Siriya Sun Kulla Alaka Da Isra’ila October 20, 2025 Kungiyar Kare Hakkin Bil-Adama Ta Amnesty Ta Zargi Gwamnatin Tanzaniya Da Musgunawa ‘Yan Adawa October 20, 2025 Dakarun kare Juyin Musulunci Na Iran Sun Bayyan Shirinsu Na Karfafa Dabarun Hadin Guiwa Da yamen October 20, 2025 October 20, 2025 Kotu A Faransa Ta Yanke Hukumci Zama Gidan Yari Ga Tsohon Shugaban Kasar Nicola Sarkozi October 20, 2025 Isra’ila Ta Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta Sau 80 Ta Kashe Mutane 97 Ta Jikkata 230 October 20, 2025 Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Mukaman Gwamnatin Tinubu inji Shugaban FCC October 20, 2025 Grossi: Za a iya warware batun Shirin nukiliyar Iran ne kawai ta hanyar diflomasiyya October 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha
Rundunar Sojan Ruwa ta IRGC ta fara wani atisayen soji a yankin kudancin Iran a Tekun Fasha, wanda ya kunshi rundunonin sojoji da dama.
An yi wa atisayen lakabi da “Eightedar” (Ikon Kasa), domin girmama kwamandan da ya yi shahada Mohammad Nazeri, wani babban jami’in sojin ruwa na IRGC.
Ana gudanar da atisayen a cikin ruwan Tekun Fasha, yankin tekun Nazeat (Abu Musa, Greater Tunb, Lesser Tunb, da Tsibiran Siri), Mashigar Hormuz.
Abin lura ne cewa Mohammad Nazeri shi ne kwamandan rundunonin kwamando na rundunar sojin ruwa ta IRGC.
An san shi sosai a Iran saboda rawar da ya taka wajen kama ma’aikatan jirgin ruwan Amurka goma—maza tara da mace daya—wadanda suka shiga ruwan Iran a ranar 12 ga Janairu, 2016.
An kama su ne bayan da jirgin ruwansu ya nutse cikin ruwan Iran kusa da Tsibirin Farsi, wani sansani a tsakiyar Tekun Farisa wanda ya kasance sansanin jiragen ruwan kai hari na gaggawa na Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci tun daga shekarun 1980.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya December 4, 2025 Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Gaza December 4, 2025 Iran: Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi December 4, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta Kama Olmert Da Livni December 4, 2025 Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro December 4, 2025 Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka December 3, 2025 MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI December 3, 2025 An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran December 3, 2025 Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci