Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa
Published: 24th, October 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa 774, inda ya tabbatar da kudurin gwamnatinsa na yaki da rashin abinci mai gina jiki da inganta yalwar abinci a fadin jihar.
An gudanar da kaddamarwar ne yayin ziyarar Mrs. Uju Rochas-Anwuka, mai bai wa Shugaban Kasa shawara ta musamman kan lafiya ( Karkashin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), wacce ta je Jigawa domin kaddamar da shirin Nutrition 774 da ke karkashin shirin sabunta kudurori na Renewed Hope Agenda.
Gwamna Namadi ya bayyana cewa Jigawa ta kasance gaba a yaki da matsalar, tare da kafa shiri na musamman da aka yi wa lakabi da Masaki tun a 2020 domin fadakar da al’umma a matakin ƙasa, wanda ya amfanar da sama da mutum miliyan 1 da dubu 300.
Ya kara da cewa gwamnati na ware Naira Miliyan 13 da rabi a kowane wata domin tallafa wa shirin na Masaki, da kuma Naira Miliyan 250 a shekara, don sayen abinci da magani tare da UNICEF, yayin da Majalisar Dokoki ke bayar da Naira Miliyan 300 a shekara.
Haka kuma, sama da mata 600 sun samu horo a shirin abincin yara na Tom Brown don samar da abinci mai gina jiki a gida tare da hadin gwiwar hukumar NAFDAC.
Gwamnan ya ce sabuwar majalisar za ta hada kai da ma’aikatun gwamnati wajen tsara da aiwatar da manufofin abinci mai gina jiki, tare da nufin sanya Jigawa ta zama ta farko da za ta cimma burin shirin gwamnatin tarayya naNutrition 774.
A jawabinta, Mrs Uju ta ce shirin na daga cikin manyan shirye-shiryen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin magance matsalar rashin abinci mai gina jiki a fadin kasar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Godswill Akpabio ya shigar da Sanata Natasha Akpoti ƙara a kotu kan zargin ɓata masa suna yana mai neman ta biya shi diyyar naira biliyan 200.
Sanata Natasha mai wakiltar jihar Kogi ta tabbatar da karɓar sammacin a shafukanta na sada zumunta, inda ta nuna jin daɗinta tana mai cewa ta samu damar bayyana hujjojinta kan zargin yunƙurin lalata da ta zarge shi da yi a baya.
“Yau 5 ga watan Disamban 2025, na karɓi sabon sammacin kotu kan ƙarar diyya ta naira biliyan 200 da Sanata Godswill Akpabio ya kai ni game da ɓata masa suna da zargin lalata,” a cewar Natasha.
“Na yi farin ciki da Sanata Akpabio ya taso da wannan batu saboda kwamatin ɗa’a na majalisa ya ƙi amincewa ya saurare ni kan batun sakamakon matar Akpabio ta shigar da ni ƙara a kotu.”
A watan Fabrairun 2025 ne Natasha ta zargi Akpabio da neman yin lalata da ita bayan rikicin da ya ɓarke a tsakaninsu, wanda ya kai ga dakatar da ita daga zaman majalisar na tsawon wata shida.