Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa
Published: 24th, October 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa 774, inda ya tabbatar da kudurin gwamnatinsa na yaki da rashin abinci mai gina jiki da inganta yalwar abinci a fadin jihar.
An gudanar da kaddamarwar ne yayin ziyarar Mrs. Uju Rochas-Anwuka, mai bai wa Shugaban Kasa shawara ta musamman kan lafiya ( Karkashin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), wacce ta je Jigawa domin kaddamar da shirin Nutrition 774 da ke karkashin shirin sabunta kudurori na Renewed Hope Agenda.
Gwamna Namadi ya bayyana cewa Jigawa ta kasance gaba a yaki da matsalar, tare da kafa shiri na musamman da aka yi wa lakabi da Masaki tun a 2020 domin fadakar da al’umma a matakin ƙasa, wanda ya amfanar da sama da mutum miliyan 1 da dubu 300.
Ya kara da cewa gwamnati na ware Naira Miliyan 13 da rabi a kowane wata domin tallafa wa shirin na Masaki, da kuma Naira Miliyan 250 a shekara, don sayen abinci da magani tare da UNICEF, yayin da Majalisar Dokoki ke bayar da Naira Miliyan 300 a shekara.
Haka kuma, sama da mata 600 sun samu horo a shirin abincin yara na Tom Brown don samar da abinci mai gina jiki a gida tare da hadin gwiwar hukumar NAFDAC.
Gwamnan ya ce sabuwar majalisar za ta hada kai da ma’aikatun gwamnati wajen tsara da aiwatar da manufofin abinci mai gina jiki, tare da nufin sanya Jigawa ta zama ta farko da za ta cimma burin shirin gwamnatin tarayya naNutrition 774.
A jawabinta, Mrs Uju ta ce shirin na daga cikin manyan shirye-shiryen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin magance matsalar rashin abinci mai gina jiki a fadin kasar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Karfafa Dangantaka Da NAFDAC
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa zata kara karfafa dankon zumunta da Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa NAFDAC.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin da mahukunta hukumar NAFDAC suka ziyarce shi a ofishin sa dake Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana farin cikinsa da ziyayar, inda ya jaddada bukatar aiki tare domin cimma dukkan nasarar da ake bukata a tsakanin hukumomin biyu.
Da yake bayani dangane da shirin da hukumar alhazan take yi, Labbo yace dukkanin shirye-shirye sunyi nisa na rigistar kujerun aikin hajji shekarar 2026.
Yana mai cewar, hukumar NAFDAC tana cikin masu ruwa da tsaki na hukumar jin dadin alhazan jihar.
Alhaji Ahmed Labbo, yayi nuni da cewar akowane lokaci za’a iya bukatar tattauna muhimman bayanai na shirye-shiryen aikin hajji domin bada ta su gudunmuwar.
Tun farko a jawabin sa, sabon Shugaban hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC a jihar jigawa, Alhaji Mansur Muhammad yace makasudin ziyarar shi ne domin gabatarwa gami da neman goyan bayan hukumar jin dadin alhazan ta jihar.
Ya kara da cewar, hukumar tana daga cikin hukumomi dake aiki tare da hukumar NAFDAC musamman a lokacin fara jigilar maniyyata.
Mansur Muhammad yace za su ci gaba da bai wa hukumar cikakken hadin kai da goyan baya a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
Usman Mohammed Zaria