Gwamnatin Jihar Sokoto Ta Amince da Sauya Amfani da Naira Biliyan 526 a Kasafin Kuɗin 2025
Published: 24th, October 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Sokoto ta amince a rika sauya kuɗaɗe da aka ware wasu wurare zuwa swasu idan can ya fi na farko amfani ga al’umma (virement) na naira biliyan 526 a cikin kasafin kuɗin shekarar 2025.
Shugaban taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 12 na bana, Gwamna Ahmad Aliyu, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na da cikakken ƙuduri wajen gina Jihar Sokoto mai ingantaccen tattalin arziki ta hanyar aiwatar da muhimman sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaban al’umma.
Gwamna Aliyu ya bayyana cewa wannan sauyin kasafi an tsara shi ne domin ƙarfafa zuba jari a fannoni masu muhimmanci kamar gina manyan ayyukan raya kasa, inganta ayyukan jin kai, da haɓaka tasirin gudanar da ayyuka — ba tare da ƙara girman jimillar kasafin kuɗin shekara ba.
Da yake bayani ga manema labarai bayan taron, Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Alhaji Aminu Iya, ya ce canjin kasafin zai mai da hankali kan kuɗaɗen da za a yi amfani da su wajen aiwatar da ayyukan ci gaban jama’a kai tsaye.
A cewarsa, majalisar ta amince da aiwatar da wasu muhimman ayyuka, ciki har da: bita (workshop) na Hukumar Sufurin Jihar Sokoto da ware naira miliyan 75 domin kula da motocin gwamnati, da kuma sayen motocin aiki ga Ma’aikatar Kuɗi ta Jihar Sokoto.
A fannin ilimi kuwa, Kwamishinan Ilimin Firamare da Sakandare, Farfesa Adan Ahmad Ala, ya sanar da cewa majalisar ta amince da naira miliyan 930 domin siyan kujera da tebura 15,000 ga makarantu na firamare da sakandare a fadin jihar.
Nasir Malali
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato Kasafi Jihar Sokoto
এছাড়াও পড়ুন:
Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
Kotu ta yanke wa wani wanda ya yi wa wata yarinya ’yar shekara 12 fyaɗe hukuncin ɗaurin rai-da-rai a Ƙaramar Hukumar Guba ta Jihar Yobe.
Babbar Kotun Jihar Yobe da ke zaune a ƙaramar hukumar Gujba ta yanke wa mutumin mai shekaru 31 mai suna Ali Kwano.
An gurfanar da shi ne a kan zargin ya kai yarinyar cikin aji a ƙaramar makarantar sakandare ta je-ka-ka-dawo da ke garin Bumsa, inda ya yi lalata da ita da ƙarfi.
Ya yaudari yarinyar ce bayan ya gaya mata cewa ta jira shi a cikin aji bisa cewar zai sayi ƙosai.
Bayan da ta shiga ajin sai ya kama hannunta, ya rufe bakinta ya danne ta a ƙasa sannan ya yi lalata da ita da ƙarfi.
Ƙasashen waje na taimaka wa ’yan ta’adda a Najeriya —Sheikh Gumi ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a KanoAlƙaliyar da ke jagorantar shari’a, Mai Shari’a Amina Shehu, ta same shi da laifi, don haka ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai bisa ga sashe na 3 na dokar haramta cin zarafin mutane, ta Jihar Yobe ta Shekarar 2020.