Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Published: 24th, October 2025 GMT
Ga Dukkan Alamu Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti
Waɗannan ginshiƙai, an tsara su ne bisa manufofin sanya hannun jari a cikin dukkanin ƙananan hukumomi 16 na jihar. A cikin shekaru uku, manyan ayyuka 577 zuwa 368 aka kammala, sannan kuma 209 da ake kan gudanar da su a halin yanzu, sun shafi garuruwa da ƙauyuka sama da 200, ana kuma ci gaba da haɓaka harkokin ilimi, kiwon lafiya, wutar lantarki, noma da kuma samar da haɗin kai.
Ayyukan Da Suka Game Mutane
Babu ayyukan da Oyebanji ya yi fiye da na abubuwan more rayuwa.
Sabbin hanyoyi kamar Ikere zuwa Igbara zuwa Odo, Ogotun zuwa Ikogosi, Isinbode zuwa Ara zuwa Ikole, shataletalen titin Ado-Ekiti (Phase I), da Omu zuwa Ijelu zuwa Itapa, sun yi matuƙar buɗe sabbin hanyoyin tattalin arziƙi.
Haka nan, ya ƙara inganta hanyoyin birane irin su; aikin titin Otel na Spotless, ‘GRA Third Eɗtension’ da gadar sama ta Okeyinmi, wanda ake kan ginawa a halin yanzu.
Sai kuma filin jirgin saman dakon kaya na Jihar Ekiti, wanda hukumar NCAA ta share kwanan nan, don gudanar da harkokin kasuwanci, kazalika, akwai kuma wata ƙofa da ke sanya Ekiti a matsayin cibiyar dabarun Kudu-maso-Yamma.
Saka hannun jari mai kama da juna, gami da Cibiyar Fasaha da Al’adu ta ƙasa da ƙasa da kuma ɗakin jinya mai gadaje 80 a babban asibitin koyarwa na jihar ta Ekiti (KSUTH), na nuna kyakkyawan nazarin gwamnatin fiye da wa’adin sa. Ya gina ba don yabo ba, sai don ya bar tarihi.
Yin Noma A Matsayin Tanadi
Noma na ɗaya daga cikin tsarin tattalin arziƙin da Oyebanji ya sanya a gaba. Sama da matasa 5,000 ne suka tsunduma cikin harkar noma da hada-hadar kasuwancinsa, ƙarƙashin wasu tsare-tsare irin su kiwon kaji ‘Broilers Scheme’ a gonar Erifun da kuma shirin dawo da matasa harkar noma.
Zuba hannun jarin da gwamnati ta yi a fannin da kuma share filaye kyauta, ɗakunan kwanan ɗalibai, taraktoci da na’urorin gona na zamani a yankin gonar Oke Ako, ya inganta samar da abinci da ayyukan yi a karkara.
Har ila yau, domin kiyaye filayen noma, an ɗauki ma’aikatan Amotekun 400 da kuma masu aikin gona, suna tsaron al’umma kai tsaye tare sauran amfanin na gona.
Yadda Ya Bai Wa Ilimi Muhimmanci
Ga Gwamna Oyebanji, batun ilimi ya wuce a ce ana kashe kudi; illa wani abu ne da ke kama da zuba jari.
Ya ƙara ba da tallafin karatu a duk wata ga manyan makarantu daga Naira miliyan 767.8 zuwa Naira biliyan 1.27, tare da kawar da basussukan albashi da inganta hanyoyin samar da kuɗaɗe.
A duk faɗin ƙananan hukumomi, an sake gina ɗaruruwan ajujuwa da ɗakunan gwaje-gwaje, cibiyar ayyuka ta yara masu nakasa da kuma azuzuwa 16 da aka sanya wa alluna koyo na zamani.
Sai kuma, ɗaukar malaman makaranta 1,600 da wasu ma’aikata 200, ya ƙarfafa ingancin koyarwa, tare da tabbatar da cewa; koɗawane ajujuwa sun ci gaba da kasancewa kamar yadda ya kamata.
Ya kuma ɗauki kowane ajujuwa a matsayin shukar da ya yi, kana kuma zai girbe gobe.
Lafiya Ita Ce Komai
A ɓangaren kiwon lafiya, gwamnati ta bayar da sakamakon da ake buƙata.
Sashin kula da lafiyar jarirai da cibiyoyin diyya na EKSUTH, na kula da dubban mutane a halin yanzu; ana kan gina katafaren asibiti mai gadaje 80 da manyan asibitoci biyar a Oye, Ijan da Ifaki Ekiti, inda ake yin gyaransu baki-ɗaya.
A ɓangaren tsarin Inshorar Lafiya ta Jihar Ekiti, ’yan fansho 19,000 ne ke samun kulawa ta fuskar kiwon lafiya kyauta. Sama da 3,700 an yi musu tiyata kyauta, an yi wa aƙalla mutum 600,000 gwajin zazzaɓin cizon sauro, sannan an rarraba magungunan kimanin 500,000 a dukkanin faɗin jihar.
An kuma ɗauki wasu ƙwararru a ɓangaren na kiwon lafiya su kimanin 250 aiki, domin tabbatar da kulawa ta isa ga waɗanda suka taɓa jin kamar an manta da su.
Gwamnatin Kowa Da Kowa Wadda Ke Ƙoƙarin Kare Lafiyar Jama’a
Haɗuwa da jama’a ya zama alamar jagorancin Oyebanji.
Gwamnatinsa ta gyara gidan kula da mata da ’yan matan da aka yi watsi da su tare da samar da kayayyakin sana’o’i ga nakasassu da kuma gudanar da ayyukan shawo kan ambaliyar ruwa da ta kai sama da Naira miliyan 300 a ƙarƙashin shirin nan ‘WASH’.
Sabbin hanyoyin magudanar ruwa a Ado ta Ekiti, sun yi matuƙar rage haɗarin ambaliya, yayin da ƙarin layukan wutar lantarki na kƁ 33 da na IPP suka inganta samar da wutar lantarki ga manyan cibiyoyin gwamnati.
Dawo Da Martabar Ma’aikata
Ɗaya daga cikin ma’anar mulkin Oyebanji, shi ne tausayawa al’umma. Ya ɓullo da tsarin ɗaukar jama’a a mota kyauta, musamman ma’aikatan gwamnati da ɗalibai, ya kuma kawar da basussukan fansho da aka daɗe ana bin su, ya biya Naira biliyan 4.9 ga ‘yan fansho su kimanin 2,260 kashi na farko, Naira biliyan 1.3 zuwa 348 da suka yi ritaya a Ƙaramar Hukumar Ado da kuma sama da Naira biliyan 40 a faɗin jihar cikin shekaru uku kacal. Yana mulki cikin tausayawa, sannan kuma Jihar Ekiti ta san haka.
Tallafa Wa Matasa Da Kuma Masana’antu
Matasan Jihar Ekiti, sun samu kulawar gaske a ƙarƙashin Oyebanji.
Cibiyar koyar da dabarun sana’o’i da ke Ado Ekiti, Aso-Oke da kuma gyaran rukunin yaɗuwar Oodua, sun sake farfaɗo da masana’antun gargajiya da na ƙere-ƙere.
Ta hanyar haɗin gwiwa da SMEDAN, sama da matasa 5,000 aka horar kan harkokin kasuwanci da na ilimin kuɗi, yayin da masu sana’a 250 suka samu takardun shaida na kasuwanci da kuma matakai na gaske don dogaro da kai na matasa.
Samun Haɗin Kai A Gwamnati
Wataƙila babbar nasarar Oyebanji, ta ta’allaƙa ne kan samun haɗin kai a siyasance. Domin kuwa, ya samu nasarar haɗa kan ‘yan siyasar Jihar Ekiti wanda ba kasafai aka cika samu ba.
Duk tsofaffin gwamnonin da aka yi a baya kamar Niyi Adebayo, Ayo Fayose, Segun Oni da Kayode Fayemi, sun yaba wa ƙasƙantar da kansa ta hanyar rashin girman kai.
Shugaban majalisar dattawa, Opeyemi Bamidele ya bayyana shi a matsayin ‘mutumin da ba kasafai ake samun irinsa wajen tawali’u da sauƙin kai ba.
Wannan yarjejeniya ta haifar da kwanciyar hankali a siyasa, wanda ya ba da damar ci gaba mai ɗorewa da kwanciyar hankali na rayuwar jama’a.
Daga Farkon Rayuwarsa Zuwa Samun Ɗaukakarsa
An haife shi a ranar 21 ga Disambar 1967, a Ikogosi-Ekiti, Oyebanji yana alfahari da zama a gida Nijeriya. Ya yi digirinsa na farko a fannin Kimiyyar Siyasa B.Sc. daga Jami’ar Jihar Ondo (yanzu EKSU) da kuma digirinsa na biyu M.Sc. a fannin hulɗa da ƙasa da ƙasa daga Jami’ar Ibadan.
Tsohon malami ne, ma’aikacin banki, kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka ƙirƙiro Jihar Ekiti a shekarar 1996, ya kwashe sama da shekaru 11 yana aikin gwamnati.
Ya auri Dakta Olayemi Oyebanji, babbar malama a jami’ar Ibadan, Allah ya albarkace su da samun ‘ya’ya uku.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Naira biliyan kiwon lafiya Jihar Ekiti
এছাড়াও পড়ুন:
Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
167-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma, ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtada Muttari, ko kuma cikin littafin Mathnawa na Maulana Jalaluddeen Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin wannan Shirin.
/////….Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan al-Mujtaba(a) dan Fatimah (s) diyar manzon Allah (s) da muke kawo maku. A cikin shirimmu da ya gabata munyi maganar
Dalilin da suka sa sojojin Imam Al-Hassan (a) suka kasa yakar sojojin Mu’awiya dan Abusufyan. Daga ciki mun bayyana cewa, kha’inci da son duniya a cikin sojojin Imam (a) ya ka suna son kama shi su mikawa mu’awiya don su su Aminta su kuma samu daukaka a wajensa.
Kamar yadda dan dan’uwan Sa’adu dan Mas’ud Athaqafi ya zo yana kudaitar da Amminsa ya kama Imam Al-Hassan (a) wanda yake jinya a gidansa ya mikawa Mu’awiya saboda ya sami aminci da da kuma daukaka. Munji da Sa’adu Athaqafi ya la’anesu ya kuma nisantar da shi, yana kuma neman tsarin Allah daga sharrinsa.
Daga ciki mun ambaci yadda Mu’awiya ya yada akidun karya dangane da banu Umayya a Sham, saboda jahilcinsu. Ya kirkoro hadidan karya ya jinginawa manzon Allah (s) tare da taimakon wasu sahabban manzon Allah wadanda suke tare da shi. Daga cikin wadan nan hadisan da suka kirkiro har da cewa Banu Umayya sune dangin manzon Allah (s) wadanda suka cancanci gadonsa.
Wannan akidar ta wanzu a kasar Sham har zuwa lokacinda Abul Abbas wanda aka fi saninsa da Saffah, sarki na farko daga cikin sarakunan Abbasiyawa ya kwace kasar Sham, sannan shuwagabannin manya manyan kungiyoyi da kabilu suka zo masa, suna rantsewa da Allah kan cewa basu taba sanin cewa manzon Allah (s) yana da dangi wadanda suka cancanci gadonsa ba in banda banu umayya.
Dangane da wannan Ibrahim dan Muhajir Al-Bajali mutumin Kufa yayi wata kisida yana fada a cikinta, yana cewa
Ya ku mutane ! Ku Saurara, Zan baku labarin * Abin mamaki, wanda yafi ban mamaki .
Abin mamaki daga Abdushamsi (banu umayya), Lalle su* Sun budewa mutane Kofofin karya.
A riyawarsu, Sun gaji Ahmadu (manzon Allah(a))* Amma banda amminsa Abbas dan Abdul Muttalib.
Sun yi karya, na rantse da Allah, bamu sans hi ba* Kan cewa ba wanda zai sami gado sai sai wanda yake kusa.
Malaman tarihi sun bayyana cewa, mutanen sham- saboda wadan nan hadisan karya, wadanda Mu’awiya da abokan aikinsa suka yada a cikinsu, suna ganin sarakunan banu umayya sarakunan addinin musulunci ci, kuma Mu’awiya khalifan Allah ne a bayan kasa. Haka ma dansa Yaziz (la’anenen wanda ya kashi jikan manzon Allah (s) wato Imam Al-Hussain (a), to shi ma khalifan Allah ne a bayan kasa).
Wadan nan al-amura suka sa mutanen sham suke matukar biyayya ga Mu’awiya dan Abusufyan, haka ma sauran sarakunan banu Umayya da su zo bayansa, har saida al-amura suka bayyana bayan faduwar daularsu kimani shekaru 80 bayan da mu’awiya ya kwace iko daga hannun Imam Al-hassan (a).
Sannan mu’awiya ya yi amfani da damar da ya samu na biyayyar da mutanen sham suke masa, ya nesantar da su daga addinin musulunci na gaskiya, da gangan yake sabawa sharia ya kuma sabawa sunnar manzon Allah (s).
Sannan saboda irin biyayyar da mutanen sham sukewa Mu’awiya, Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a) yayi gurin, ina ma yana da Mabiya, wadanba basa sabawa umurnin shugabansu kamar yadda mutanen sham suke biyayya ga mu’awiya har yana fadawa mutanen Iraki wani lokaci, ina da za’a yi masa musayar daya daga cikinsu da mutum 10 daga cikin Irakawa. Wadanda ba abinda aka sansu da shi sai tashe tashen hankula da jayayya da shuwagabanninsu. Shugabansu ya fada su fada.
Sannan mutanen sham, kafin shigarsu addinin musulunci su kiristoci ne, karkashin daular Ruma da gabas wanda yake jagorantar yankin daga kasar Turkiya a lokacin. Don haka sun saba da gwamnatin da biyayya ga shugaba da kuma tsarin rayuwa mai nutsuwa, ba kamar larabawa kafin musulunci ba.
Don haka su mutanene masu saukin hali, amma basu da wayo ko kuma amfani da hankali a cikin al-amura don fahintar gaskiya. Danga ne da wannan malaman tarihi sun bayyana cewa, bayan yakin siffin wani mutumin Iraki ya je kasar Sham da rakuminsa, sai ya hadu da wani mutumin sham wanda yace ai rakumin nasa nasa. Ragima da shiga tsakaninsu, har suka je gaban Mu’awiya.
Mutumin sham ya kawo shaidu kimani 50 suka tabbatar da cewa rakumin na miji nasa ne, sai mu’awiya ya yanke hukunci kan cewa a mayarwa mutumin sham, rakumin.
Sai mutumin Iraki ya fadawa Mu’awiya ai wannan taguwa ce (macce ba rakumi) na mijiba!.
Amma sai mu’awiya yace masa hakunci ya rika wuce ka mayarma da damar. A lokacinda aka watse, sai mu’awiya ya aika a kira mutumin Iraki ya zo. A lokacinda ya zo, sai yace masa nawa kudin taguwarka sai ya fada, sai ya ninka masa ya kuma fada masa, idan ka je Iraki ka fadawa Aliyu dan Abitalib (a) kan cewa, na tanaji mutanen sham dubu 100 don yakarsa, ba wani daga cikinsa wanda yake iya bambata tsakanin rakumi na miji da taguwa ta mace.
Wannan ya nuna irin rashin wayewa da fahintar mutanen sham a lokacin, don haka Mu’awiya ya yi amfani da jahilcinsu ya yakar iyalan gidan manzon Allah (a) da su. Ya sauya al-amura da dama na addini, ya kuma takurawa iyalan gidan manzon Allah (a) da mabiyansu, ya sunnata kashesu da la’antarsu a kan mimbarorin musulmi na tsawon shekaru kimani 60 bayan sulhuntawa da Imam Al-Hassan kamar yadda zamu gani a nan gaba.
Don haka Mu’awiya ya barsu cikin jahilci, cikin duhu bayan duhu, suna masu dimwa a cikin al-amarinsu, baya barin wani ya zo ya farkar da su ko kuma su su je wani wuri a cikin daular musulunci inda zasu gano gaskiyan al-amari. Su gano kariyar Mu’awiya da kuma banu umayya gaba daya.
Sai kuma rarraba da hadin kai, kasar Sham bata da rarrabar kai na akidu da kuma kabilanci wanda ake da su a kasar Iraki.
Don haka su kalma guda ce ta hada su, basa da sabani a tsakaninsu, akidar Khawarijawa bata shigo masa ba. Hakama basa da matsala tsakanin shuwagabannin kabilu da Mu’awiya. Yana bawa shuwagabannin kudaden da suka gabata don su rike masa kabilunsu. Iran wannan kabilun Iraki suke nema amma Ahlul Baiti suka bayyana hakan ya sabawa adalci. Rabon shugaban kabila shi ne rabon mabiyansa. Ba’a bashi fiye da rabonsa.
Don haka hadin kan da aka samu a cikin gida yana da cikin sirrin nasarorin da Mu’awiya ya yi ta samu a kan sojojin Imam Al-Hassan (a).
A wani bangare kuma Mu’awiya ya karfafa sojojinsa ne bayan da ya sami hadin kai a cikin gida. Ya sulhunta da daular Roma da ta rage a lokacin, ya kuma bata kudade masu yawa don kada ta tada masa yaki.
Sannan a cikin gida ya na karban haraji mai yawa a wajen mutane, yana karban zakka hatta a cikin kayakin da ba’a masu zakka.
Mun san cewa dukiyoyi iri 8 ne ake masu zakka, amma Mu’awiya yana karban zakka. Kuma yana matsawa kwarai wajen karban zakka da kuma haraji. Mu’awiya ya tilasta wa mutanen sham bada abinda ake kira da Farisanci :hadayar Niruz” wanda babu a cikin addinin musulunci.
Niruz sabuwar shekara ce ta Iraniyawa da kuma kabilun da suke yankin Asiya kamar Kurdawa da sauransi, musulunci bai san da shi ba. Ya kuma halatta wasu abubuwan da shari’a ta haramta, mai yuwa bai san shari’a ta haramta su ba, amma sau da dama da gangan yake sabawa addinin musulunci yana sani da matsayinsa.
Wani lokaci yakan halatta wani abu ko ya haram tashi da gangan don ya sabawa sharia. Da kuma kuma ya sauka abubuwan adiinin, kama daga hukunce-hukunce zuwa ibada da sauranci, kuma da gangana.
Har’ila yau Imam Al-Hassan (a) ya ki mutanen kufa ne bayan sun kashe mahaifinsa Amirul muminina (a) . Muntum wanda yake rayuwa a cikinsu, cikin talaunci, sannan yana matukan kokari wajen ganin sun rayuwa cikin jin dadi, da kuma adalci a tsakaninsu. Yana rayuwa cikinsu kamar rayuwar daya daga cikinsu. Amma sai wasu daga cikinsu suka fito suka kasheshi ba tare da yayi masu laifi ba, ba tare da dauki dukiyoyinsu, ba tare da ya tsokanesu. Wannan al-amarin ya bar tabo babba a zuciyar Imam Al-Hassan (a) kuma tun lokacin yake taka tsantsan da su. Yake kuma ganin basu cancanci su zana mataimakansa ba. Saboda laifukan da suka aikata, na kashe mahaifinsa, wasiyin kakansa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri December 7, 2025 Iran Ta Zama Zakaran Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025 Dubban Mutane Suna Guduwa Daga Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci