’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa
Published: 24th, October 2025 GMT
’Yan Sanda sun sake kama dan gwagwarmaya kuma mamallakin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore, bayan wata kotun Majistare da ke Abuja, ta bayar da belinsa.
An sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa tare da wasu mutum 12 a ranar Juma’a.
Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — WikeAlƙalin kotun, Abubakar Sai’id ne, ya bayar da belin Sowore da wasu mutum 12 da aka tuhuma da tayar da hankalin jama’a, sakamakon zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin.
Lauyan Sowore, Tope Temokun, ya zargi ’yan sanda da yin amfani da karfi, inda suka yi awin gaba ba tare da wani bayani ba.
Temokun ya bayyana cewa: “Bayan kotu ta bayar da belin Sowore, sai wasu ’yan sanda ƙarƙashin jagorancin CSP Iliyasu daga Sashen CID suka mamaye harabar kotun, inda suka sa masa da sauran jama’ar da ke wajen duka, sannan suka tafi da Sowore a bainar jama’a.
“A kokarin dakatar da su na ji rauni.”
Ya ƙara da cewa ba a kai Sowore gidan yari ba, amma an tafi da shi wani waje daban wanda ba wanda ya sani.
Kotun ta bayar da belin Sowore da sauran waɗanda ake tuhuma; ciki har da Aloy Ejimakor lauyan shugaban IPOB Nnamdi Kanu da kuma ɗan uwan Nnamdi Kanu, Emmanuel Kanu, kan kudi Naira 500,000 kowanne.
Kotu ta kuma umarce su da su miƙa fasfo ɗinsu, tare da katin shaida dan kasarsu da takardun biyan haraji na shekaru uku kafin a sake su.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ’yan sanda ba su fitar da wata sanarwa ba game da sake kama Sowore ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda ta bayar da
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
Tom Barrack jakadan Amurka na musamman a kasar Siriya ya bayyana cewa gwamnatin kasar Amurka ta yi kokarinkifar da gwamnatin JMI a baya har sau biyu amma ta kasa yin haka.
Tashar talabijin ta Presstva a nan Tehran ta nakalto Barrack yana fadawa wani kamfanin dillancin labaran UAE a ranar jumma’an da ta gabata, ya kuma kara da cewa daga shekara ta 1946 ya zuwa yau gwamnatin Amurka ta yi kokarin kifar da gwamnatoci 93 biyu daga cikinsu a kasar Iran ba tare da samun nasarara ba. Amma akwai da dama wadanda suka sami nasara.
Ya ce kafin Trump ya hawo kan kujerar shugabancin Amurka mun yi kokar kifar da gwamnatin kasar har sau biyu ba tare da samun nasara ba. Barrack dai har’ila yau shi ne jakadan Amurka a kasar turkiyya.
Wannan bayanin yana zuwa ne watanni 6 da yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka kaiwa kasar wato daga ranar 13 ga watan Yuni zuwa 24 ga watan. Inda sukakashe Iraniyawa 1,064 suka kuma kaiwa fararen hula da dama hare-hare.
A cikin yakin ne gwamnatin Amurka ta kai hgare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran a fordo Naqtanz da kuma Esfahan.
Iran ta sami nasara a wannan yakin ne bayan ta kai hare-hare masu karfi kan HKI da dama, hare-haren dasuka tabbatar da cewa Iran zata iya shafe HKI da yayin ya ci gaba. Haka ma Iran ta kai hare-haren kan sansanon sojojin Amurka mafi girma a gabas ta tsakiya dake Al-udaita na kasar Qatar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri December 7, 2025 Iran Ta Zama Zakaran Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025 Dubban Mutane Suna Guduwa Daga Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025 Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci