Leadership News Hausa:
2025-10-24@10:25:52 GMT

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Published: 24th, October 2025 GMT

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Baya ga haka, sabon ginin ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Zamfara da aka sake ginawa da kuma sabon ginin kwalejin fasaha da kimiyya na Jihar Zamfara (ZACAS) da aka gyara, sun yi matuƙar haskaka Gwamnatin Dauda Lawal.

Har ila yau, jihar ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari, wajen gyarawa da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.

 

A ƙoƙarinsa na rage mace-macen mata masu juna biyu da mace-macen jarirai, an ɗauki ma’aikatan kiwon lafiya tare da horar da su da sayen magunguna da kayan aiki da ɓullo da ayyukan kula da lafiyar mata da ƙananan yara kyauta.

Sannan, an gyara asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura tare da samar da kayan aiki na zamani. Haka kuma an gyara tare da samar da kayan aiki ga babban asibitin da ke Ƙaramar Hukumar Kauran Namoda a jihar. Babban asibitin da ke Kauran Namoda da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da shi, an samar da kayan aiki don isar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya yadda ya kamata. Kazalika, an sanya na’urorin bincike, gadaje, injinan ECG, injin centrifuge, injinan gwaje-gwajen jini, na’urar tantance jini ta atomatik da sauran wasu kayan aiki.

Kazalika, an kuma inganta babban asibitin Nasarawar Burkullu da ke Ƙaramar Hukumar Bukkuyum. Bayan ayyukan kiwon lafiya da suka haɗa da na gaggawa, aikin tiyata, kula da lafiyar mata da yara, tsarin wurin keɓewa, wurin ajiyar gawa, ɗakunan tiyata na maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, shagon magani, kula da mata masu juna biyu da kula da yar, duk an gina su. Sauran gyare-gyaren, sun haɗa da shingen gudanarwa, wuraren ma’aikata, masallatai da rijiyoyin burtsatse.

Haka kuma, a Ƙaramar Hukumar Maru, an gyara babban asibitin tare da samar da kayan aiki na zamani.

Gwamnan ya kuma kaƙƙamar da aikin sabunta birane, wanda ya kai ga gyara manyan tituna a jihar.

Dangane da batun tsaro kuwa, a shekarun baya-bayan nan, Zamfara ta ɗan samu jinkiri. A wannan lokaci na Gwamna Lawal, kashe-kashe da garkuwa da mutane ya ragu matuƙa a jihar. Hakan ya biyo bayan kafa jami’an tsaron da aka kafa a dukkanin kananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.

An horar da mutanen da aka zaɓo a tsanake, bisa cikakkiyar kulawar jami’an tsaron hukumar DSS, sannan suna yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro na yau da kullum, domin yaƙi da ‘yan fashi a jihar. A kwanakin baya ne gwamnan ya raba motocin aiki guda 140 da aka ware wa ƙungiyoyin tsaro daban-daban a faɗin jihar.

An haifi Dauda Lawal Dare, a ranar 2 ga Satumbar 1965, a Jihar Zamfara. Bayan kammala karatunsa na Firamare da Sakandare, ya halarci Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ya yi digirinsa na farko a fannin Kimiyyar Siyasa. Ya kuma yi digirinsa na biyu (M.Sc) a fannin kimiyyar siyasa/Hukunce-hukuncen ƙasa da ƙasa duk a jami’ar. Ya ƙara da digirin-digirgir (PhD) a fannin harkokin kasuwanci a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.

Bayan kammala karatunsa na digiri na uku, ya yi kwasa-kwasai a Makarantar Kasuwanci ta Harɓard, Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Oɗford, Makarantar Tattalin Arziƙi ta Landan, Makarantar Kasuwancin Legas da sauransu.

Gwamnan ya yi aiki a matsayin jami’in ilimin siyasa tare da MAMSER, hukumar wayar da kan jama’a, don tabbatar da adalci da dogaro da kai a Nijeriya. A 1989, ya shiga Westeɗ Nigeria Limited a matsayin mataimakin babban manaja.

An naɗa shi a matsayin mataimakin ƙaramin jami’in shige da fice (immigration), a shekarar 1994, sannan ya zama babban jami’in hulɗa da jama’a a ofishin Jakadancin Nijeriya, Washington, DC, Amurka.

A shekarar 2003, ya koma bankin First Bank, a matsayin manajan hulɗa da jama’a, kuma a lokuta daban-daban ya kasance babban manaja a ofishin Abuja. A shekarar 2011, ya samu muƙamin mataimakin shugaban zartaswa, sashen gwamnati na Arewa na bankin na First Bank, bayan ya yi ayyuka da dama. A shekarar 2012, Dauda Lawal ya zama babban darakta a sashen gwamnati na Arewa, na First Bank.

Daga baya ya shiga siyasa ya kuma tsaya takarar Gwamnan Jihar Zamfara. A zaɓen fidda gwani na APC da aka gudanar a shekarar 2018, ya sha kaye a hannun Idris Shehu Mukhtar. A zaben Gwamnan Jihar Zamfara na 2023, ya tsaya takara; kuma ya yi nasara a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya October 24, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno October 23, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC October 23, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da kayan aiki a Jihar Zamfara kiwon lafiya Dauda Lawal

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sanda A Jihar Zamfara Ta Gargadi Direbobi Game Da Rufe Lambar Mota

Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Zamfara ta  gargaɗi direbobi da sauran jama’a game da rufe lambobin motoci, musamman a cikin garin Gusau, babban birnin jihar.

Gargaɗin ya biyo bayan ƙaruwa da ake samu na rahotanni da kuma lura da direbobi da ke tafiya da lambobin motoci a rufe, wanda rundunar ta bayyana a matsayin karya dokokin hanya da ke kawo barazana ga tsaro da zaman lafiya.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya fitar, rundunar ta bayyana cewa wannan dabi’a tana nuna ƙoƙarin kaucewa binciken jami’an tsaro tare da yiwuwar taimaka wa aikata laifuka.

Sanarwar ta ƙara da cewa, Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya jaddada cewa rundunar ba za ta sake lamuntar irin wannan aiki ba.

Ya bayyana cewa an umarci jami’an rundunar da su fara aiwatar da tsauraran matakan doka, inda ya ƙara da cewa kowace mota da aka samu ta rufe lambar mota za a kama ta tare da gurfanar da mai motar a gaban doka.

CP Maikaba ya kuma shawarci jama’a da direbobi a fadin jihar Zamfara da su bi dokokin hanya tare da yin haɗin kai da ‘yan sanda wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

Ya tabbatar wa jama’a da cewa rundunar ‘yan sandan za ta ci gaba da jajircewa wajen kiyaye doka da oda, tare da ƙarfafa al’umma da su rika ba da rahoton duk wani abin da suke zargi ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

 

Daga Aminu Dalhatu 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudurin Gwamnatinsa Na Ƙara Zuba Jari A Ilimi
  • Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, Ta Kaddamar da Dakin Karatu Na Zamani a Zamfara
  • AGILE Kano Ta Tattauna da Malamai da Limamai Don Ƙarfafa Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata
  • Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
  • Babban Lauyan Jihar Kwara Ya Tabbatar da Gudanar da Adalci da Kare Hakkokin Mace
  • UNICEF Ya Tabbatar Da Anniyar Na Karfafa Jagorancin Mata A Fannin Ilimi
  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Jihar Zamfara Ta Gargadi Direbobi Game Da Rufe Lambar Mota
  • Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal