Aminiya:
2025-12-07@18:47:38 GMT

DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a Kaduna

Published: 23rd, October 2025 GMT

Jami’an Hukumar Tsaro ta DSS sun kama wasu mutum uku da ake zargi da sayar da wa ’yan bindiga makamai da harsasai a Jihar Kaduna.

An kama su ne bayan wani samame da jami’an DSS suka kai a ƙananan hukumomin Igabi da Kachia.

’Yan uwana 8 sun rasu a fashewar tanka a Neja — Wani Mutum Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio

An kama ɗaya daga cikinsu mai shekaru 30, a kan titin Nnamdi Azikiwe Bypass da ke Igabi.

An gano bindiga ƙirar AK-47 guda biyu, bindigar PKT guda ɗaya, harsasai sama da 200.

Sauran mutum biyu kuma an kama su ne a ƙauyen Doka da ke Ƙaramar Hukumar Kachia, a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna.

An kama su suna ƙoƙarin yi wa ’yan bindiga safarar AK-47 guda uku a cikin wata mota ƙirar Volkswagen Golf.

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya yaba wa hukumar DSS bisa wannan nasara, inda ya ce gwamnatinsa ba za ta bar wani ɗan ta’adda ko mai aikata laifi ya samu mafaka a jihar ba.

Ta bakin Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Barista Sule Shuaibu, gwamnan ya kuma gode wa Shugaba Bola Tinubu da Darakta-Janar na DSS bisa goyon bayan da suke bai wa tsaro a jihar.

Ya ce tsarin zaman lafiya da gwamnatinsa ta ƙirƙiro wanda ya haɗa da tattaunawa da haɗin kai a tsakanin al’umma ya taimaka wajen rage laifuka a faɗin jihar.

Ya gargaɗi masu aikata laifi da su daina ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.

Hukumar DSS ta ce tana gudanar da bincike a kan waɗanda ta kama, kuma za ta tabbatar da cewa an hukunta su.

Hakazalika, ta jaddada ƙudirinta na daƙile safarar makamai a Jihar Kaduna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Safarar Makamai zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa Hamas ta bayyana cewa za ta mika makamanta ne kawai ” idan Isra’ila ta kawo karshen mamaya, tana mai jaddada cewa ba za a iya kwance damarar makamai ba a cikin yanayin da ake ciki na zaluncin soja da siyasa.

Babban jami’i a ofishin siyasa na Hamas kuma babban mai shiga tsakani na kungiyar, Khalil al-Hayya, ne ya bayyana hakan inda yake cewa idan mamayar ta kare, za a sanya wadannan makaman a karkashin ikon gwamnatin kasar Falasdinu.”

Ofishinsa ya fayyace cewa kalmar “ƙasa” tana nufin “ƙasar Falasɗinawa mai zaman kanta” mai cikaken iko.

“Har yanzu ana ci gaba da tattaunawa game da kwance makamai tsakanin kungiyoyi daban-daban da masu shiga tsakani, kuma yarjejeniyar tana cikin farkon matakanta ne kawai,” in ji shi.

“Mun yarda da tura sojojin Majalisar Dinkin Duniya a matsayin dakarun masu sa ido kan iyakokin da kuma tabbatar da kare yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza,” in ji Khalil al-Hayya.

Ma’aikatar Lafiya ta Falasdinawa a Gaza ta sanar a ranar Lahadi cewa tun lokacin da yarjejeniyar tsagaita wuta ta fara aiki, gwamnatin Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 367 tare da raunata wasu 953.

Sojojin Isra’ila sun kuma karya yarjejeniyar tsagaita wuta akalla sau 591 tsakanin 10 ga Oktoba zuwa 2 ga Disamba, ta hanyar hare-haren sama, manyan bindigogi da kuma harbi kai tsaye, a cewar ofishin manema labarai na gwamnati a Gaza.

Tun bayan fara kai hari kan kisan kare dangi da Isra’ila ta yi wa Gaza a ranar 7 ga Oktoba, 2023, akalla Falasdinawa 70,354 ne aka kashe, yawancinsu mata da yara, yayin da sama da 171,030 suka jikkata.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda 20, kwangilolin haɗin gwiwa na fasaha guda biyar
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara