Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-23@12:57:21 GMT

Gwamna Yusuf Ya Gwangwaje Kano Pillars Da Sabbin Motocii

Published: 23rd, October 2025 GMT

Gwamna Yusuf Ya Gwangwaje Kano Pillars Da Sabbin Motocii

Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ta bai wa ƙungiyar kwallon ƙafa ta Kano Pillars Football Club sabbin motoci uku domin sauƙaƙa musu matsalolin sufuri a yayin gasar Premier ta shekarar 2025/2026 da ke gudana.

 

Motocin sun haɗa da babbar motar Marcopolo mai kujeru 29 don ɗaukar ’yan wasa, motar samfurin Hummer, da kuma Sharon da za a yi amfani da ita wajen harkokin gudanarwa da sufuri.

 

A lokacin da yake mika makullai da takardun motocin a madadin Gwamnan, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Malam Ibrahim Umar Farouk, ya roƙi matasan jihar masu son wasanni da su ci gaba da zama masu bin doka da oda tare da guje wa duk wani abu da zai bata sunan jihar.

 

Ya bayyana cewa wannan kyauta ta nuna yadda Gwamna Yusuf ke da ƙwarin gwiwa wajen ƙarfafa matasa da bunƙasa harkokin wasanni a jihar.

 

A nasa jawabin, Kwamishinan Matasa da Wasanni, Mustapha Kwankwaso, ya bayyana godiyarsa ga Gwamna Yusuf bisa wannan babban ci gaba da zai ƙara wa ’yan wasan kwarin gwiwa da jin daɗin aiki.

 

Ya kuma yi kira ga magoya bayan ƙungiyar Sai Masu Gida da su kasance masu ladabi da biyayya tare da ci gaba da nuna goyon baya cikin lumana.

 

Da yake mayar da martani, Manajan Janar na Kano Pillars FC kuma kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa (MON, OON), ya yaba wa Gwamna Yusuf bisa goyon baya da ƙaunar da yake nuna wa ƙungiyar.

 

Ahmed Musa ya kuma roƙi gwamnatin jihar da ta ba da girmamawa ta musamman ga tsohon kyaftin ɗin ƙungiyar, Rabiu Ali, domin tunawa da gudunmawar da ya bayar wajen bunƙasa kwallon ƙafa a Najeriya, yana mai kiran sa da “ɗaya daga cikin fitattun ’yan wasa mafiya tasiri da suka taka leda a tarihin NPFL.”

 

A halin yanzu, ƙungiyar Kano Pillars za ta karɓi bakuncin Niger Tornadoes ta Minna a wasansu na ranar goma ta gasar NPFL a wannan Asabar, a filin wasa da suka ɗauka a matsayin gida na wucin gadi — Filin Muhammadu Dikko da ke Katsina.

 

Khadijah Aliyu

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Yusuf Kano Pillars

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 2 Wajen Binciken Albarkatun Kasa

Majalisar zartarwa ta jihar Jigawa ta amince da kashe Naira biliyan 2.55 domin gudanar da binciken na musamman, wanda zai mayar da hankali kan albarkatun mai, gas, da sinadarin uranium, tare da cikakken binciken kimiyyar kasa kan ma’adinai a fadin jihar.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya fitar, ya bayyana cewa wannan muhimmin shiri na gwamnatin yanzu babban mataki ne na gaba wajen cika alkawarin gwamnati na ganowa da kuma amfani da albarkatun kasa masu tarin yawa da ke cikin jihar Jigawa.

A cewarsa, wannan bincike zai samar da bayanai masu muhimmanci game da ma’adinai, da mmn fetur da iskar gas da ke karkashin kasa, wanda zai taimaka wajen yanke shawara mai inganci, jawo hankalin masu zuba jari, da kuma tallafawa ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

Ya kara da cewa, majalisar ta sake jaddada kudirin gwamnati na bunkasa tattalin arziki ta hanyar bincike da hakar albarkatun kasa bisa tsari da kuma amfani da bayanai na kimiyya.

Sagir ya jaddada cewa, ta hanyar zuba jari a nazarin kimiyyar kasa mai inganci, jihar na da burin samar da sababbin hanyoyin samun kudaden shiga, bunkasa damar samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma shimfida tubalin ci gaban masana’antu.

Ya kara da cewa, binciken albarkatun kasa, da mai da iskar Gas zai kasance a hannun kwararrun masana, bisa bin ka’idoji da dokokin kasa da kasa, domin tabbatar da sahihanci, inganci, da amfani mai tsawo na sakamakon da za a samu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 2 Wajen Binciken Albarkatun Kasa
  • Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
  • Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja
  • Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo
  • Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi
  • Muna Samun Gagarumin Cigaba Wajen Dawo Da Zaman Lafiya A Zamfara-Gwamna Lawal
  • Kano Pillars ta dakatar da Kocinta
  • Kano Pillars Ta Dakatar Da Babban Kocinta Bisa Rashin Katabus A Kakar Wasa Ta NPFL