Leadership News Hausa:
2025-12-06@20:26:16 GMT

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Published: 22nd, October 2025 GMT

Wannan tsarin na taimaka wa yara su samu ilimi mai zurfi da zai ba su damar daidaita da tsarin rayuwarsu na yau da kullum.

Makarantun suna da ɗakunan kwana, gidajen malamai, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru, kayan karatu, da cibiyar koyon sana’o’i kamar ɗinki, sassaƙa, kwamfuta, da sauransu.

Haka kuma, gwamnan ya gyara Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Zamfara da kuma Kwalejin Fasaha da Kimiyya ta Zamfara (ZACAS).

A ɓangaren lafiya kuwa, gwamnatinsa ta gyara asibitoci da cibiyoyin lafiya da dama a faɗin jihar.

Don rage mace-macen mata da jarirai a yayin haihuwa, ya ɗauki ƙarin ma’aikatan lafiya, tare da samar da magunguna da kayan aiki, tare d harkar kyautata kiwon lafiya ga mata masu juna biyu da yara kyauta.

Asibitin Ƙwararru na Yeriman Bakura an gyara shi gaba ɗaya tare da samar da kayan aiki na zamani.

Asibitin Gwamnati na Kauran Namoda ma an sabunta shi da kayan gwaje-gwaje, kujerun haihuwa, injinan ECG, da sauran kayan asibiti na zamani.

A Nasarawa Burkullu, an gina sabbin sassa a Asibitin Gwamnati, ciki har da ɗakin agajin gaggawa, ɗakin tiyata, ɗakin haihuwa, ɗakunan jinya na maza da mata, ɗakin gwaje-gwaje, da ɗakin magani.

Haka kuma an samar da masallatai, gidajen ma’aikata, da rijiyoyin burtsatse.

A ƙaramar hukumar Maru, Asibitin Gwamnati ma an gyara shi tare da sanya kayan aiki na zamani.

Gwamnan, ya kuma ƙaddamar da shirin sabunta birane wanda ya haɗa da gyaran manyan hanyoyi da gine-gine a biranen jihar.

A ɓangaren tsaro, Jihar Zamfara ta samu sauƙin yawaitar hare-hare a ’yan shekarun nan.

An rage kashe-kashe da satar mutane sosai.

Wannan ya faru ne saboda ƙirƙirar rundunar ‘Community Protection Guards’ a kowace ƙaramar hukuma 14 da ke jihar.

An zaɓi mutanen ne bayan cikakken bincike da DSS ta jagoranta, sannan aka horar da su don taimaka wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan ta’adda.

Gwamnan ya kuma raba motoci 140 ga hukumomin tsaro daban-daban a jihar.

Tarihin Gwamna Dauda Lawal

An haifi Dauda Lawal a ranar 2 ga watan Satumba, 1965 a Jihar Zamfara.

Ya kammala karatunsa na digiri da digiri na biyu a Fannin Siyasa a Jami’ar Ahmadu Bello, da ke Zariya, sannan ya yi digirin digirgir a Fannin Kasuwanci a Jami’ar Usmanu Danfodiyo, da ke Sakkwato.

Hakazalika, ya yi kwasai-kwasai na horo a Harvard Business School, Oxford University, London School of Economics, da Lagos Business School.

Kafin ya shiga siyasa, ya yi aiki a MAMSER, sannan ya yi aiki a Ofishin Jakadancin Nijeriya a Washington DC a matsayin jami’in shige da fice.

Daga baya ya koma aiki a bankin First Bank of Nigeria, inda ya zama Daraktan Ayyukan Jama’a na Arewa.

Ya shiga siyasa a shekarar 2018, inda ya tsaya takarar gwamna a jam’iyyar APC, amma bai yi nasara ba.

A zaɓen 2023, ya tsaya takarar gwamna a jam’iyyar PDP kuma ya lashe zaɓen, tare da Gwamnan Jihar Zamfara.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci October 22, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta October 22, 2025 Labarai Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma

Daga Usman Muhammad Zaria

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya yaba da gagarumin cigaba a harkar noma da Gwamna Umar Namadi ya samar cikin shekaru biyu kacal na mulkinsa.

Ya bayyana haka ne a masarautar Gumel cikin Jihar Jigawa, yayin kaddamar da sabon masallacin Juma’a da Gidauniyar Kashim Shettima ta gina a matsayin wani ɓangare na bikin zagayowar cikar Sarkin Gumel shekaru 45 a kan karaga.

A cewarsa, abin sha’awa ne yadda Gwamna Umar Namadi ya mayar da harkar noma a jihar Jigawa zuwa ta zamani cikin shekaru biyu kacal.

Ya jinjina wa Gwamnan da al’ummar Jihar Jigawa bisa wannan ci gaba mai armashi.

Kashim Shettima ya kara taya Sarkin Gumel, Alhaji Muhammadu Sani, murnar cika shekaru 45 a matsayin Sarkin Gumel, tare da yi masa fatan alkhairi.

Ya tabbatar da ci gaba da jajircewar Gidauniyar Kashim Shettima wajen inganta rayuwar ‘yan Najeriya.

A jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya yaba wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa kaddamar dadMasallacin.

Ya kuma taya Sarkin Gumel murnar cika shekaru 45 a kan karaga, tare da yi masa fatan alheri.

Shi ma a nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jinjina wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa gina Masallacin Juma’ar.

Namadi ya kuma yaba da jinjinar da VP ya yi kan sauyin da aka samu a harkar noma ta Jigawa, yana mai alkawarin cewa za a cigaba da kara himma a bangaren noma da ma dukkan ababen da za su ciyar da jihar gaba.

Gwamnan ya kara jinjina wa Mai Alfarma Sarkin Musulmi  da sauran manyan baki bisa halartar taro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi