Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal
Published: 22nd, October 2025 GMT
Wannan tsarin na taimaka wa yara su samu ilimi mai zurfi da zai ba su damar daidaita da tsarin rayuwarsu na yau da kullum.
Makarantun suna da ɗakunan kwana, gidajen malamai, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru, kayan karatu, da cibiyar koyon sana’o’i kamar ɗinki, sassaƙa, kwamfuta, da sauransu.
Haka kuma, gwamnan ya gyara Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Zamfara da kuma Kwalejin Fasaha da Kimiyya ta Zamfara (ZACAS).
A ɓangaren lafiya kuwa, gwamnatinsa ta gyara asibitoci da cibiyoyin lafiya da dama a faɗin jihar.
Don rage mace-macen mata da jarirai a yayin haihuwa, ya ɗauki ƙarin ma’aikatan lafiya, tare da samar da magunguna da kayan aiki, tare d harkar kyautata kiwon lafiya ga mata masu juna biyu da yara kyauta.
Asibitin Ƙwararru na Yeriman Bakura an gyara shi gaba ɗaya tare da samar da kayan aiki na zamani.
Asibitin Gwamnati na Kauran Namoda ma an sabunta shi da kayan gwaje-gwaje, kujerun haihuwa, injinan ECG, da sauran kayan asibiti na zamani.
A Nasarawa Burkullu, an gina sabbin sassa a Asibitin Gwamnati, ciki har da ɗakin agajin gaggawa, ɗakin tiyata, ɗakin haihuwa, ɗakunan jinya na maza da mata, ɗakin gwaje-gwaje, da ɗakin magani.
Haka kuma an samar da masallatai, gidajen ma’aikata, da rijiyoyin burtsatse.
A ƙaramar hukumar Maru, Asibitin Gwamnati ma an gyara shi tare da sanya kayan aiki na zamani.
Gwamnan, ya kuma ƙaddamar da shirin sabunta birane wanda ya haɗa da gyaran manyan hanyoyi da gine-gine a biranen jihar.
A ɓangaren tsaro, Jihar Zamfara ta samu sauƙin yawaitar hare-hare a ’yan shekarun nan.
An rage kashe-kashe da satar mutane sosai.
Wannan ya faru ne saboda ƙirƙirar rundunar ‘Community Protection Guards’ a kowace ƙaramar hukuma 14 da ke jihar.
An zaɓi mutanen ne bayan cikakken bincike da DSS ta jagoranta, sannan aka horar da su don taimaka wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan ta’adda.
Gwamnan ya kuma raba motoci 140 ga hukumomin tsaro daban-daban a jihar.
Tarihin Gwamna Dauda LawalAn haifi Dauda Lawal a ranar 2 ga watan Satumba, 1965 a Jihar Zamfara.
Ya kammala karatunsa na digiri da digiri na biyu a Fannin Siyasa a Jami’ar Ahmadu Bello, da ke Zariya, sannan ya yi digirin digirgir a Fannin Kasuwanci a Jami’ar Usmanu Danfodiyo, da ke Sakkwato.
Hakazalika, ya yi kwasai-kwasai na horo a Harvard Business School, Oxford University, London School of Economics, da Lagos Business School.
Kafin ya shiga siyasa, ya yi aiki a MAMSER, sannan ya yi aiki a Ofishin Jakadancin Nijeriya a Washington DC a matsayin jami’in shige da fice.
Daga baya ya koma aiki a bankin First Bank of Nigeria, inda ya zama Daraktan Ayyukan Jama’a na Arewa.
Ya shiga siyasa a shekarar 2018, inda ya tsaya takarar gwamna a jam’iyyar APC, amma bai yi nasara ba.
A zaɓen 2023, ya tsaya takarar gwamna a jam’iyyar PDP kuma ya lashe zaɓen, tare da Gwamnan Jihar Zamfara.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya
Hukumar Leƙen Asirin Soji ta Najeriya (DIA) tana gudanar da bincike kan wani tsohon gwamna bisa zargin sa da ɗaukar nauyin sojoji da nufin yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu juyin mulki.
Majiyoyin Aminiya sun bayyana cewa akwai zargi mai karfi cewa tsohon gwamnan, wanda ɗan asalin yankin Kudu ne kuma tsohon babban jami’in gwamnati a ɓangaren albarkatun mai da iskar gas ne, ya ɗauki nauyin yunƙurin juyin mulkin, wanda da aka shirya aiwatarwa a ranar 25 ga watan Oktoban nan da muke ciki.
A ƙarshen mako ne kafofin watsa labarai na Shahara Reporters da Premium Times suka ruwaito cewa wasu hafsoshin soji 16, —waɗanda Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta ce sun shiga hannu saboda aikata abubuwan da saɓa ƙa’idar aiki— an tsare su ne saboda zargin su da yunƙurin kifar da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Daga cikin sojojin da aka kama akwai wani mai muƙamin Birgediya-Janar da wani Kanar da wasu na ƙasa da su da ke Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Sha’anin Tsaro (ONSA).
NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu? Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a KanoMajiyar Aminiya ta tabbatar da cewa akwai ƙamshin gaskiya a rahoton zargin yunƙurin juyin mulkin.
Majiyar ta ce, “Gaskiya ne. Akwai hannun fararen hula, ciki har da wani tsohon gwamna, kuma ana bincike domin gano irin rawar da suka taka a ciki. A halin yanzu, sojoji 16 da ake zargi suna tsare.
“Tsohon gwamnan da ke ake zargin tsohon mai babban muƙami ne a ɓangaren albarkatun mai da iskar gas, amma ba a riga an kai ga tabbatar da sa hannunsa a ciki ba.”
Wata majiyar kuma ta shaida mana cewa binciken na ƙoƙarin gano irin alaƙar da kuma tattunawar da ke tsakanin tsohon gwamnan da sojojin da aka kama.
Ta ƙara da cewa akwai yiwuwar za a gayyaci tsohon gwamnan domin amsa tambayoyi idan har aka samu ƙwararan dalilai game da alaƙarsa da sojojin da ake zargi da neman kifar da gwamnati.
Rahotanni sun bayyana cewa Hukumar Leƙen Asirin Soji ce take gudanar da binciken, tare da wakilai daga rundunonin sojin ƙasa da sojin sama da kuma Sojin Ruwa ta Najeriya.
“Mambobin kwamitin binciken sun haɗa da manya-manyan hafsoshin soji, bisa jagorancin wani mai muƙamin Manjo-Janar. An tsananta sirranta jerin sunayen waɗanda ake binciken.”
Manyan waɗanda ake zargiMajiyoyinmu sun bayyana cewa Manjo-Janar ɗin da ke jagorantar binciken ɗan asalin Jihar Neja ne.
“Akwai wani Kanar ɗan asalin wani babban gida daga Jihar Nasarawa. Mahaifinsa basarake ne kuma ɗan uwan tsohon Gwamnan Jihar, Umar Al-Makura,” in ji majiyar.
Binciken da muka gudanar a garin Lafia, hedikwatar Jihar Nasarawa, ya gano cewa zuri’ar Al-Makura suna cikin damuwa.
Ɗaya daga cikinsu da ya shaida wa wakilinmu a ranar Lahadi da dare, ya ce, wanda ake zargin “Kawuna ne. Gaba ɗaya danginmu sun shiga damuwa. Ni kaina ina cikin tashin hankali, … Haka ma matar hafsan sojin. Addu’armu dai ita ce, Allah Ya sa kada a kama su da laifin abin da ake zargi.”
Ƙarin sojoji sun shiga SojojiBinciken da muka gudanar ya gano cewa an ƙara jama wasu sojojin domin amsa tambayoyi kan alaƙarsu da zargin yunƙurin juyin mulkin.
“Baya ga tsohon gwamnan akwai wasu manyan ’yan siyasa daga yankin Kudu da kuma Arewa da bibiyar duk wani motsinsu,” in ji majiyarmu.
Ba mu ambaci juyin ba — SojojiA ranar Asabar Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta fitar da wata sanarwa ta hannun Daraktan Yaɗa Labaranta, Birgediya-Janar Tukur Gusau, da ke ƙaryata rahotanni da ke cewa zargin yunkurin kifar da gwamnati ne ya sa aka dakatar da bikin zagayowar ranar samun ’yancin cikar Najeriya karo na 65 a ranar 1 ga watan nan na Oktoba.
Manjo-Janar Tukur Gusau ya buƙaci jama’a da su yi watsi da labarin, yana mai bayyana masu yaɗa shi a matsayin maƙarya kuma marasa kishin ƙasa.
Sanarwar mai taken ‘DHQ ba ta ambaci juyin mulki ba, ta ce, “DHQ ta lura da wani labarin ƙarya da wasu kafofin watsa labarai na intanet suka wallafa da ke riya cewa an soke bukukuwan zagayowar ranar cikar Najeriya shekara 65 da samun ’yanci ne saboda zargin yunƙurin juyin mulki.
“Labaran suna nuni ga wata sanarwar DHQ na baya-bayan nan game da tsare wasu hafsoshin soji 16 da ake bincikar su kan saɓa kai’idar.
“Rundunar Tsaron Najeriya na sanar da al’umma cewa abin da kafofin watsa labaran suka wallafa ƙarya ce tsagwaronta, kuma an ƙirƙira ta ce domin sanya mutane cikin fargaba da rashin yarda da juna.
“An yanke shawarar dakatar da bikin ne domin ba wa Shugaban Ƙasa damar halartar wani muhimmin babban taro a ƙasar waje da kuma ba wa sojijojinmu damar ci gaba da ragargazar a ayyukan ’yan ta’adda da ’yan bindiga da ke addabar ƙasar .
“Hedikwatar Tsaro tana kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa binciken da ake yi kan hafsoshin sojan guda 16, abu ne na yau da kullum a gidan soja, domin tabbatar da ɗa’a da kuma ƙwarewa a kowane mataki.
“An riga an kafa kwamitin bincike yadda ya kamata kuma nan gaba za a sanar da al’umma sakamakon binciken
“DHQ na kira ga ’yan ƙasa masu kishin zaman lafiya da su taimaka wa jami’an da duk wata gudunmawa d ta dace. Gwamnatin Tarayya da ɓangaren Majalisa da ɓangaren Shari’a suna aiki kafaɗa-da-kafaɗa domin tabbatar da tsaro da ci-gaba da kuma walwalar al’ummar Najeriya da kuma ɗorawar tsarin dimokuraɗiyya.
“Hedikwatar tana kuma kira ga jama’a da su yi watsi da labaran ƙarya da maƙiyan wannan ƙasa suke yaɗawa. Rundunar Tsaro ta Najeriya ta tsaya kai da fata wajen tabbatar da biyayyarta da kuma kare kundin tsarin mulkin Najeriya a ƙarƙashin jagorancin Babban Hafsan Hafsoshin Tsaro, Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR.”
Neman a bayyana su da ainihin zarginTun bayan ɓullar labarin zargin yunƙurin kifar da gwamnati ’yan Najeriya ke ta kira ga rundunar sojin ƙasar ta bayyana sunayen waɗanda ake zargin da ake tsare.
’Yan Najeriya a kafofin sada zumunta sun buƙaci hukumomin soji su bayyana haƙiƙanin laifin da ake zargin hafsoshinta 16 da ta ce tana tsare da su.
Adelabi Gbenga, ya wallafa a Facebook cewa: “Zuwa ga rundunar soji, muna buƙatar ku sanar da ’yan Najeriya haƙiƙanin laifin hafsoshi 16 kafin kunga,a da su. Ruwa ba ya tsami banza.”
“Saɓa wa ƙa’idar aiki? Ku gaya mana ne suka yi takamaimai. Kar ku da mu a cikin duhu. Kuma da kuɗaɗen harajinmu ake biyan ku albashi,” i. Ji Edidiong Jackson a kafar X.
Zakaria Olambeloye ya wallafa a Facebook cewa, “Su sojojin nan ko… Shi ya sa ba na son shiga aikin. Tun da mutane sun aikata laifi, ku fito ku faɗi irin laifin kuma shi ne wahala? Ku gaya mana su waye su, kuma wane laifi suka aikata.”