A cewar sanarwar, “A ranar 15 ga Oktoba, 2025, da misalin karfe 11:00 na rana, wata mata da ke zaune a unguwar Federal Low-Cost, Gombe, ta bayyana cewa a daidai wannan ranar da misalin karfe 2:30 na dare, wani wanda ba ta san ko wanene ba, dauke da wuka ya kai mata hari, inda ya sace mata kayanta.

 

“Abubuwan da aka sace, sun haɗa da iphone 13 Pro Max, an kimanta kudinta akan ₦800,000, kwamfutar ‘Apple MacBook’ da darajarta ta kai ₦250,000, da agogon ‘Apple’ da darajarsa ta kai ₦35,000, ‘power bank’ na Oraimo wanda darajarsa ta kai ₦30,000, da jakar makaranta akan darajar ₦25,000.

 

Abdullahi ya ce, nan take jami’an ‘yansanda na shiyyar suka dauki matakin kama wanda ake zargin tare da kwato dukkan kayayyakin da aka sace.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina October 22, 2025 Labarai Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja October 22, 2025 Manyan Labarai Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki  October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

UNICEF Ya Tabbatar Da Anniyar Na Karfafa Jagorancin Mata A Fannin Ilimi

Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya tabbatar da aniyarsa ta inganta daidaito tsakanin maza da mata da kuma karfafa jagorancin mata a fannin ilimi a Jihar Jigawa.

Shugabar Ofishin UNICEF na Kano, Rahama Rihood Mohammed, ya bayyana hakan a wani taron da HiLWA ta shirya tare da tallafin Kungiyar Tarayyar Turai (EU) a Dakin Taro na Manpower Development Institute.

Ya ce bincike ya nuna cewa ko da yake mata su ne mafi rinjaye a aikin koyarwa a Jigawa, suna da kaso 14 bisa 100 ne kacal a mukaman shugabanci, kamar shugabar makaranta ko mataimakiya. Wannan, a cewarsa, yana takaita gudunmawar mata wajen tsara manufofi da ci gaban ilimi.

Rahama Ya bayyana cewa matsalolin al’adu, tsarin aiki, da rashin damar samun jagoranci na hana mata ci gaba, yana mai cewa idan mata suka jagoranci makarantu, ana samun kyakkyawar gudanarwa da karin nasara ga dalibai, musamman ‘yaya mata.

Ya ce a karkashin Shirin Jinsi na UNICEF (2022–2025), za a ci gaba da dakile matsalolin da ke hana mata cigaba, samar da tsarin daukar aiki da karin girma bisa adalci, da kuma gina hanyoyin koyarwa ga mata masu neman mukaman shugabanci.

UNICEF ya jaddada cewa zai ci gaba da aiki tare da HiLWA, da  EU, da Gwamnatin Jigawa domin samar da manufofi da za su karfafa mata a harkar ilimi.

Ya ce karfafa jagorancin mata ba  batun adalci ba ne kadai, muhimmin mataki ne na gina kyakkyawar makomar yara.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Tabbatar Da Anniyar Na Karfafa Jagorancin Mata A Fannin Ilimi
  • Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya
  • An Yi Fashi Da Makami A Gidan Adana Kayan Tarihin  ” Louvre” Na Kasar Faransa
  • Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa
  • An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba
  • ’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu
  • Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
  • APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno
  • Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba