Aminiya:
2025-10-24@20:40:53 GMT

Ƙungiya ta tallafa wa ɗaliban makarantar masu buƙata ta musamman a Gombe

Published: 24th, October 2025 GMT

Ƙungiyar Arewa Unity Women in Media, ta kai tallafi Makarantar Masu Buƙata ta Musamman da ke Gombe, domin taimaka wa gwamnati wajen kula da rayuwar ɗaliban da ke da buƙata ta musamman.

Tallafin ya ƙunshi gidajen sauro, bargo da tabarmi, wanda aka raba wa ɗaliban a lokacin bikin miƙa kayan tallafin.

’Yan sanda sun kama ɗalibi da ya soki Gwamnan Neja ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa

Shugabar ƙungiyar, Lois Hassan daga GMTV Gombe, tallafin na da nuna kulawa da ƙauna ga ɗaliban, tare da tabbatar musu cewa al’umma ba ta manta da su ba.

Ta ƙara da cewa ƙungiyar Arewa Unity Women in Media ƙungiya ce mai zaman kanta da ke gudanar da ayyukan jin-ƙai domin tallafa wa marasa galihu da ƙarfafa zumunci a tsakanin al’umma.

Malaman makarantar, Joy Samuel da Maimuna Manager, sun yaba da wannan tallafi, inda suka roƙi gwamnati ta samar da magunguna a cibiyar lafiya ta makarantar.

Haka kuma, sun buƙaci ƙungiyoyi da masu hannu da shuni su yi koyi da irin wannan aiki na alheri.

Wasu daga cikin ɗaliban da suka amfana da tallafin, Comfort Ephraim da Barisasa David, sun bayyana farin cikinsu, inda suka bayyana cewa tallafin ya zo a lokacin da suke buƙata sosai.

Sun kuma roƙi gwamnati da ta gyara wutar lantarki a makarantar domin inganta tsaro da yanayin karatu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Ƙungiya

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Piwuna, ya ce gwamnati ta gaza cika alƙawurran da ta ɗauka duk da sanarwar kwanaki 14 da ASUU ta bayar tun a ranar 28 ga Satumba, 2025.

Ya ce babu wani abin da aka cimma wanda zai hana ƙungiyar aiwatar da shawarar majalisar zartarwarta na fara yajin aikin.

“Dukkanin rassan ASUU a faɗin ƙasar nan an umarce su da su janye ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na dare ranar Litinin,” in ji Piwuna

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin wannan lokaci, za ta ɗauki mataki mafi tsanani bayan kammala yajin aikin gargaɗin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe October 22, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas October 22, 2025 Manyan Labarai Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja October 22, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
  • Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudurin Gwamnatinsa Na Ƙara Zuba Jari A Ilimi
  • Rasha ta miƙa wa Ukraine sojoji 1,000 da suka mutu a fagen daga
  • Cutar karnuka: An ƙaddamar da riga-kafin karnuka 2,500 a Gombe
  • Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 
  • Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
  • Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja