A wurin taron, kwamitin tsakiya na JKS ya kafa wasu tsare-tsare da za su zama jagora kan bunkasa harkokin tattalin arziki da walwalar al’umma a cikin shirin na shekaru biyar-biyar na 15 wadanda suka hada da sake tabbatar da shugabancin jam’iyyar baki daya, da sanya kula da mutane a gaba da komai, da neman samun ingantaccen ci gaba, da cikakkiyar zurfafa gyare-gyare a gida, da karfafa cudanya tsakanin kasuwa mai albarka da gwamnati mai kwazon aiki, da kuma tabbatar da samun ci gaba da inganta tsaro.

Har ila yau, kwamitin tsakiya na JKS ya shata wasu manyan manufofi game da shirin shekaru biyar-biyar na 15 da suka hada da gagarumar zurfafawa wajen samun ci gaba mai inganci, da ingantacciyar habaka dogaro da kai da karfin ci gaban kimiyya da fasaha, da cimma sabbin nasarori a cikin kara zurfafa gyare-gyare a gida gaba daya, da samun ci gaban al’adu da dabi’a a cikin al’umma a zahirance, da kara inganta jin dadin rayuwa, da samun manyan sabbin ci gaba wajen zurfafa Shirin samar da kyakkyawar kasar Sin, da kuma kara samun ci gaba wajen karfafa garkuwar tsaron kasa.

A gobe Jumma’a ne kwamitin tsakiya na JKS zai gudanar da taron manema labarai kan ka’idoji da kudurorin da aka cimma a cikakken zaman taro na hudu na kwamitin kolin JKS na 20. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka October 22, 2025 Daga Birnin Sin Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11 October 22, 2025 Daga Birnin Sin Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera October 22, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

UNICEF Ya Tabbatar Da Anniyar Na Karfafa Jagorancin Mata A Fannin Ilimi

Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya tabbatar da aniyarsa ta inganta daidaito tsakanin maza da mata da kuma karfafa jagorancin mata a fannin ilimi a Jihar Jigawa.

Shugabar Ofishin UNICEF na Kano, Rahama Rihood Mohammed, ya bayyana hakan a wani taron da HiLWA ta shirya tare da tallafin Kungiyar Tarayyar Turai (EU) a Dakin Taro na Manpower Development Institute.

Ya ce bincike ya nuna cewa ko da yake mata su ne mafi rinjaye a aikin koyarwa a Jigawa, suna da kaso 14 bisa 100 ne kacal a mukaman shugabanci, kamar shugabar makaranta ko mataimakiya. Wannan, a cewarsa, yana takaita gudunmawar mata wajen tsara manufofi da ci gaban ilimi.

Rahama Ya bayyana cewa matsalolin al’adu, tsarin aiki, da rashin damar samun jagoranci na hana mata ci gaba, yana mai cewa idan mata suka jagoranci makarantu, ana samun kyakkyawar gudanarwa da karin nasara ga dalibai, musamman ‘yaya mata.

Ya ce a karkashin Shirin Jinsi na UNICEF (2022–2025), za a ci gaba da dakile matsalolin da ke hana mata cigaba, samar da tsarin daukar aiki da karin girma bisa adalci, da kuma gina hanyoyin koyarwa ga mata masu neman mukaman shugabanci.

UNICEF ya jaddada cewa zai ci gaba da aiki tare da HiLWA, da  EU, da Gwamnatin Jigawa domin samar da manufofi da za su karfafa mata a harkar ilimi.

Ya ce karfafa jagorancin mata ba  batun adalci ba ne kadai, muhimmin mataki ne na gina kyakkyawar makomar yara.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
  • Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
  • Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
  • UNICEF Ya Tabbatar Da Anniyar Na Karfafa Jagorancin Mata A Fannin Ilimi
  • Iran Ta Godewa Rasha Game Da Goyon Bayan Da Ta Bata A Kwamitin Sulhu Na M D D
  • Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
  • Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
  • Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi