NLC ta kuma buƙaci gwamnati ta bi shawarar UNESCO wacce ta ke cewa ya kamata a ware aƙalla kashi 25 cikin 100 na kasafin kuɗi na kowace shekara ga ilimi.

Ajaero, ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa magance matsalolin cikin makonni huɗu, NLC za ta haɗa dukkanin ma’aikata na ƙasa don gudanar da yajin aiki na ƙasa baki ɗaya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu October 21, 2025 Manyan Labarai Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara October 20, 2025 Manyan Labarai Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a October 20, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu

Bayanai daga rundunar sojin Najeriya na cewa an kafa wani kwamiti da ke binciken wasu jami’ai 20 da aka tsare bisa zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Jaridar Premium Times ta ruwaito wata majiyar soji da ke da masaniya kan lamarin tana cewa al’amarin ya faru ne a ƙarshen watan Satumba.

An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano An tsinci gawar wata mata da aka yi wa kisan gilla a Yobe

Majiyar ta ce ana zargin jami’an da shirya zubar da jini a juyin mulkin, kasancewar akwai sunayen wasu manyan jami’an gwamnati da aka shirya yi wa kisan gilla.

A cewar majiyar kamar yadda Premium Times ta ruwaito, daga cikin manyan jami’an gwamnatin waɗanda masu kitsa juyin mulkin suka shirya yi wa kisan gilla akwai shugaba Bola Tinubu da matamaikinsa, Kashim Shettima da kuma shugabannin Majalisun Tarayya, Sanata Godswill Akpabio da Abbas Tajudeen da sauransu.

Waɗanda ake zargin dai, bayanai sun tabbatar da cewa sun tsayar da ranar da za su kifar da gwamnatin farar hula, yayin da suke tuntuɓar juna a kai a kai.

Wannan yunƙuri na juyin mulkin ya haifar da firgici a tsakanin manyan jami’an gwamnati bayan da aka fallasa shi, duk da cewa babban hafsan sojin ƙasar ya sha ba wa gwamnatin Najeriyar tabbacin goyon bayan sojoji ga gwamnati.

An kuma ruwaito cewa saboda kaɗuwar wannan labari ne, gwamnati ta soke faretin cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai na ranar 1 ga Oktoba, kasancewar bikin sojoji ne ke jan ragamarsa.

Majiyar ta ƙara da cewa, rundunar ta kafa wani kwamitin bincike da zai bibiyi abin da hukumomi suka bayyana a matsayin rashin ɗa’a da kuma saba ƙa’idojin aiki.

Wata majiya ta ce kwamitin ya shafe makon da ya gabata yana zaman bibiyar al’amarin, amma har yanzu ba a san inda aka kwana ba.

Duk da cewa hedikwatar tsaron ba ta tabbatar da yunƙurin juyin mulkin kai tsaye ba, amma kakakinta, Birgediya Janar Tukur Gusau, a ranar 4 ga watan Oktoba, ya ce ana binciken wasu sojoji 16 kan rashin ɗa’a da kuma saɓa ƙa’idojin aiki.

Sai dai sanarwar da Birgediya Janar Gusau ya fitar a ranar Asabar, ta ce raɗe-raɗin juyin mulki da ake ta yamaɗiɗi ba gaskiya ba ne.

“Rundunar sojin Najeriya na tabbatar da cewa rahoton na ƙarya ne baki ɗayansa,” a cewarsa.

“An dakatar da faretin Ranar ’Yanci ne saboda a bai wa shugaban ƙasa damar halartar wani taro a wajen Najeriya, da kuma mayar da hankali wajen yaƙi da ta’addanci da ’yan fashin daji.

“Binciken da ake yi wa jami’ai 16 kuma na yau da kullum ne da aka saba domin tabbatar da ɗa’a da ƙwarewar aiki. An kafa kwamatin bincike kuma za a sanar da sakamakon bincikensa.”

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
  • Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
  • NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU
  • Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
  • Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
  • Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a
  • Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
  • An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu
  • Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU