Idan Tinubu ya gaza zai yi wuya a samu shugaban da zai yi nasara — Shehu Sani
Published: 22nd, October 2025 GMT
Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya ce zai yi matuƙar wuya a samu shugaban da zai saita Najeriya, idan har Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya gaza cika alƙawuran da ya ɗauka.
Shehu Sani, ya bayyana haka ne yayin hira a gidan talabijin na TVC, inda ya bayyana cewa Tinubu na da damar daidaita makomar Najeriya.
Har ila yau, ya ce nasarar Tinubu ko gazawarsa, za ta taka muhimmiyar rawa wajen tsara makomar siyasar ƙasar nan.
“Idan Shugaba Bola Tinubu ya gaza, bana ganin abubuwa za su zo wa shugaban ƙasan da zai zo da sauƙi,” in ji shi.
Tsohon ɗan majalisar ya shawarci shugaban ƙasar da ya zaɓi mutane ƙwararru da za su taimaka masa wajen cika muradun ’yan Najeriya maimakon bai wa masu yi masa biyayya muƙamai.
Ya ce Tinubu ya kamata ya maimaita ire-iren tsarin da ya aiwatar a Jihar Legas, inda ya naɗa ƙwararru da suka taimaka masa wajen samar wa jihar ci gaba.
Shehu Sani, ya kuma soki yadda siyasar Najeriya ta koma mai cike da rashin jituwa.
Ya ce abun baƙin ciki ne yadda masu mulki da ’yan adawa ke yi wa juna kallon abokan gaba maimakon abokan samar da ci gaba.
Ya buƙaci Shugaba Tinubu da ya ɗauki matakai da suka ƙunshi sauye-sauye, ko da kuwa wasu ba za su ji daɗin hakan ba, inda ya jaddada cewa kowace ƙasa da ta ci gaba ne ta hanyar sadaukarwa.
“Babu wata ƙasa da ta zama babba cikin sauƙi. Ƙasashe kamar China, Singapore, da Indonesia sun yi sadaukarwa kafin su cimma muradunsu,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi
Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya karyata zargin kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya, yana mai cewa wannan ikirari ƙarya ne kuma bai kamata a ci gaba da yada shi ba.
Sarkin ya bayyana hakan ne a taron Babban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewa na shekarar 2025, wanda aka gudanar a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, a ranar Talata, da taken: “Ƙarfafa Haɗin Gwiwar Al’umma Domin Samun Zaman Lafiya da Tsaro Mai Dorewa a Arewa.”
Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiyaYa ce: “Sun dade suna cewa ana kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya daga ƙasashen Yamma kamar Amurka, Kanada da sauransu. A ina? Yaushe? Wannan labari ne na ƙarya.”
Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewacin Najeriya ya ce ba zai yiwu a ce ana irin wannan kisa a wani yanki na Najeriya ba, kuma sarakunan gargajiya ba su sani ba.
Ya roƙi shugabannin ƙasa da su sanya dokoki kan amfani da kafafen sada zumunta saboda illar da suke haifarwa da kuma abubuwan batanci da ake wallafawa game da ƙasa da mutane a cikinsu.
Sarkin ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya da su daina zagin sojoji, yana mai jaddada cewa da babu sadaukarwarsu, da ƙasa ba za ta ci gaba da kasancewa ƙasa ɗaya mai zaman lafiya ba.
Sai dai ya amince cewa sojoji na fama da ƙalubale da gazawa, amma ya soki maganganun da ake yi a kafafen sada zumunta da ke zargin jami’an tsaro da haɗin gwiwa da ‘yan ta’adda, yana mai cewa hakan rashin tausayi ne kuma bai dace ba.
Sarkin ya sake jaddada goyon bayan sarakunan gargajiya ga ci gaban dimokuraɗiyya da biyayya ga dukkan shugabannin da aka zaɓa, ciki har da Shugaban Ƙasa, Majalisun Tarayya da na Jihohi, da Gwamnoni.
Ya kuma buƙaci sarakunan da suka halarci taron da su haɗa kai domin fuskantar ƙalubalen da ƙasa ke ciki, yana mai cewa za a mika shawarwarin da suka bayar ga Gwamnonin Arewa domin ɗaukar matakin da ya dace.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a taron ya ce sarakunan gargajiya na da muhimmiyar rawa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya ce suna da ƙwarewa wajen rage tashin hankali, warware rikice-rikice, da kawo zaman lafiya a lokacin ƙalubale.