Idan Tinubu ya gaza zai yi wuya a samu shugaban da zai yi nasara — Shehu Sani
Published: 22nd, October 2025 GMT
Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya ce zai yi matuƙar wuya a samu shugaban da zai saita Najeriya, idan har Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya gaza cika alƙawuran da ya ɗauka.
Shehu Sani, ya bayyana haka ne yayin hira a gidan talabijin na TVC, inda ya bayyana cewa Tinubu na da damar daidaita makomar Najeriya.
Har ila yau, ya ce nasarar Tinubu ko gazawarsa, za ta taka muhimmiyar rawa wajen tsara makomar siyasar ƙasar nan.
“Idan Shugaba Bola Tinubu ya gaza, bana ganin abubuwa za su zo wa shugaban ƙasan da zai zo da sauƙi,” in ji shi.
Tsohon ɗan majalisar ya shawarci shugaban ƙasar da ya zaɓi mutane ƙwararru da za su taimaka masa wajen cika muradun ’yan Najeriya maimakon bai wa masu yi masa biyayya muƙamai.
Ya ce Tinubu ya kamata ya maimaita ire-iren tsarin da ya aiwatar a Jihar Legas, inda ya naɗa ƙwararru da suka taimaka masa wajen samar wa jihar ci gaba.
Shehu Sani, ya kuma soki yadda siyasar Najeriya ta koma mai cike da rashin jituwa.
Ya ce abun baƙin ciki ne yadda masu mulki da ’yan adawa ke yi wa juna kallon abokan gaba maimakon abokan samar da ci gaba.
Ya buƙaci Shugaba Tinubu da ya ɗauki matakai da suka ƙunshi sauye-sauye, ko da kuwa wasu ba za su ji daɗin hakan ba, inda ya jaddada cewa kowace ƙasa da ta ci gaba ne ta hanyar sadaukarwa.
“Babu wata ƙasa da ta zama babba cikin sauƙi. Ƙasashe kamar China, Singapore, da Indonesia sun yi sadaukarwa kafin su cimma muradunsu,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026
Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), ta kammala fitar da jadawalin Rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026.
Za a gudanar da gasar ne a Amurka, Kanada da Mexico daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026.
Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan KwaraRabon jadawalin ya gudana ne a birnin Washington na ƙasar Amurka a ranar Juma’a, inda Ingila ta samu kanta a rukuni ɗaya Croatia.
Brazil za ta kara da Maroko, yayin da Amurka za ta kara da Australia.
Faransa za ta ɓarje gumi da Senegal, sannan Argentina za ta fafata da Austria.
Ga jerin yadda kowane rukuni na gasar Kofin Duniya na 2026 ya kasance:
Rukuni A: Mexico, Afirka ta Kudu, Koriya ta Kudu, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar.
Rukuni B: Kanada, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Qatar, Switzerland
Rukuni C: Brazil, Maroko, Haiti, Scotland
Rukuni D: Amurka, Paraguay, Australia, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar.
Rukuni E: Jamus, Curaçao, Ivory Coast, Ecuador.
Rukuni F: Netherlands, Japan, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Tunisia.
Rukuni G: Belgium, Masar, Iran, New Zealand.
Rukuni H: Spain, Cape Verde, Saudi Arabia, Uruguay
Rukuni I: Faransa, Senegal, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Norway
Rukuni J: Argentina, Aljeriya, Austria, Jordan.
Rukuni K: Portugal, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Uzbekistan, Colombia
Rukuni L: Ingila, Croatia, Ghana, Panama