An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya
Published: 24th, October 2025 GMT
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu October 24, 2025
Manyan Labarai Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji October 24, 2025
Manyan Labarai Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa October 24, 2025
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, Ta Kaddamar da Dakin Karatu Na Zamani a Zamfara
Uwargidan Shugaban Ƙasa ta Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta kaddamar da Dijital E-Learning Library a Gusau, Jihar Zamfara — ɗaya daga cikin jihohi goma da aka zaɓa a faɗin ƙasar domin aiwatar da wannan muhimmin aiki ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) tare da haɗin gwiwar Hukumar bunkasa ayukkan fasaha ta kasa (NITDA).
A yayin bikin kaddamarwar, Sanata Tinubu ta bayyana cewa wannan aiki ba wai game da fasaha da kwamfuta kawai ba ne, amma yana nufin ƙarfafa matasa, rage gibin fasaha (digital divide), da kuma buɗe sabbin ƙofofin ilimi da ƙirƙira ga al’ummar Zamfara da ma Najeriya baki ɗaya.
Uwargidan Shugaban Ƙasa, wacce Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta wakilta, ta bayyana cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaba a kowace al’umma.
Ta ce, a wannan zamani na dijital, samun kayan koyon zamani ba wata alfarma ba ce, amma wajibi ne domin ci gaban ilimi.
A cewarta, ta hanyar wannan dijital library, dalibai, malamai, masu bincike da ma jama’a gaba ɗaya za su sami damar shiga manyan bayanai, albarkatu da dama na ilmantarwa a sauƙaƙe.
Sanata Tinubu ta bayyana cewa Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) yana da burin tallafa wa ilimi, ƙirƙira da ci gaban zamantakewa, kuma wannan E-Learning Library na ɗaya daga cikin manyan alamu na hangen nesa na shirin.
Ta kuma yaba wa Ma’aikatar Sadarwa, Ƙirƙira da Tattalin Arzikin Dijital da kuma NITDA bisa ƙwarewar su wajen aiwatar da aikin.
A nata jawabin, Uwargidan Gwamnan Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta nuna godiya mai zurfi ga mijinta, Gwamna Dauda Lawal, bisa jajircewarsa wajen inganta harkar ilimi a jihar.
Ta shawarci dalibai, malamai da masu bincike da su amfani da wannan cibiyar ta dijital yadda ya kamata, domin bunƙasa ilimi da gina kyakkyawar makoma ga matasa da ƙarni masu zuwa.
Tun da fari, Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Zamfara, Malam Wadatau Madawaki, wanda Maryam Yahaya, Babban Sakataren Ma’aikatar, ta wakilta, ya yaba wa Sanata Oluremi Tinubu bisa ƙoƙarinta wajen bunƙasa ilimin dijital ta hanyar kafa wannan E-Learning Library ƙarƙashin shirin Renewed Hope Initiative.
Kwamishinan ya bayyana aikin a matsayin babbar nasara wajen bunƙasa ƙirƙira, haɗa kai ta hanyar fasaha da kuma tabbatar da ingantaccen ilimi ga ’yan Zamfara.
Haka kuma, ya yaba wa Uwargidan Gwamna Hajiya Huriyya Dauda Lawal bisa wakiltar Uwargidan Shugaban Ƙasa da kuma irin goyon bayanta da jajircewa wajen cigaban ilimi a jihar.
Madawaki ya ƙara da cewa wannan E-Learning Library na tafiya da hangen nesa na Gwamna Dauda Lawal, wanda tun bayan hawa mulki ya ayyana dokar ta-baci kan ilimi, matakin da ya haifar da gagarumin ci gaba a fannin ilimi a jihar.
Aminu Dalhatu