Hukumar gudanarwa ta ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sanar da dakatar da Mai Ba da Shawara a harkokin koyarwa na ƙungiyar, Ogenyi Evans, da Babban Koci, Ahmed Garba (Yaro Yaro), saboda rashin gamsasshen sakamako da ƙungiyar ke samu a farkon kakar wasa ta 2025/2026 Nigeria Premier Football League (NPFL).

 

A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne sakamakon jerin sakamakon wasanni marasa kyau da suka gaza cika tsammanin masoya da masu ruwa da tsaki a ƙungiyar.

 

Ya yanzu dai, kungiyar ta Sai Masu Gida ta buga wasanni takwas, inda ta samu nasara a biyu kacal, ta kuma tashi kunnen doki a wasanni 2, sannan suka sha kaye a wasanni huɗu — sakamakon da ƙungiyar ta bayyana a matsayin abin da bai dace da ƙungiya mai irin wannan matsayi ba.

 

A halin da ake, tsohon kyaftin ɗin ƙungiyar kuma mataimakin koci, Gambo Muhammad, zai jagoranci harkokin koyarwa tare da kocin masu tsaron raga, Suleiman Shuaibu, yayin da Coach Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai shiga cikin tawagar masu koyarwa ta wucin gadi har sai an bayar da umarni na gaba.

 

Hukumar ta kuma jaddada aniyarta ta sake gina ƙungiyar domin samun sakamako mafi kyau da kuma ci gaba da kare martabar ta a matsayin ɗaya daga cikin manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa a Najeriya.

 

Daga Khadijah Aliyu

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kano Pillars a ƙungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta

Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta

Ana binciken wani tsohon ma’aikacin jinya a qasar Italiya bisa zargin ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu kuma ya je ma’aikatar fansho a matsayin mahaifiyarsa don neman fanshonta. Haka kuma an gano ya voye gawarta a cikin gidansa har tsawon shekaru uku bayan mutuwarta.

Mutumin xan Italiya ya saka tufafin mahaifiyarsa da ta mutu sannan ya yi kwalliya da gazar da jan-baki kamar yada take yi, ya je bankin da take ajiya yana neman a biya shi kuxi fanshonta, bayan ya voye gawarta a gida.

Mutumin mai shekaru 56, ma’aikacin jinya da ya rasa aikinsa a garin Mantua, ya sami damar karvar dubban kuxi na Yuro kafin asirinsa ya tonu, kamar yadda Jaridar Corriere della Sera ta Italiya ta ruwaito.

An kuma yi zargin cewa, ya naxe gawar mahaifiyarsa, Graziella Dall’Oglio, sannan ya voye ta a cikin firji a gidansu har tsawon shekara uku ba tare da ya sanar da ma’aikatar fansho ba, inda ya riqa zuwa yana cire kuxin fanshon da ake tura mata yana bidirin gabansa.

Mis Dall’Oglio ta rasu kimanin shekara uku da suka gabata, tana da shekara 82. Amma xanta bai bayar da rahoton mutuwarta a hukumance ba, maimakon haka ya naxe gawarta a cikin zane, ya saka ta a cikin wata jakar ajiye kaya sannan ya voye ta a gidan.

Rahotanni sun ce, ya yi shigar mahaifiyarsa, sanye da jan-baki da hoda da gazar da kuma sarqa, sannan ya tafi sabunta katin shaidarta da ya qare a ofishin gwamnati da ke wajen Borgo Virgilio.

Bayanai sun nuna cewa, ya yi wa kansa aski sannan ya sanya gashin mata a kansa kamar irin na mahaifiyarsa da ta rasu, kuma ya sanya kayan ado kamar yadda ta saba.

Jaridar ta bayyana cewa, wannan wani sabon salon damfara ce kamar irin na fim xin ‘Mrs Doubtfire’, wanda aka yi a shekarar 1993 da Robin WilliaMis da ya fito a ciki. Mutumin ya bayyana a ofishin gwamnati da ke wajen Mantua a farkon wannan watan, inda aka yi zargin ya bayyana kansa a matsayin Mis Dall’Oglio.

Wani ma’aikacin ma’aikatar fansho ne ya harvo jirginsa, inda ya lura da cewa, akwai alamar tambaya game da ‘matar’ da take neman a canza mata katin. Musamman da yake ya san wacce take da ainihin katin ba ta da kaurin wuya, sannan kuma muryarta ba ta maza ba ce. Wannan ce ta sanya ma’aikacin bai wata-wata ba cikin sauri ya kai rahoto ga ‘yan sanda nan da nan kuma ya sanar da magajin garin Mantua.

’Yan sanda sun ce, da isarsu sai suka kwatanta hotunan Mis Dall’Oglio na gaske da na xanta da ya yi shigar burtu kuma sun fahimci cewa, akwai lauje a cikin naxi.

Bincike ya nuna xan ya karvi kuxin fanshonta na shekaru uku da suka kai kusan Fam 47,000 kuma da mallakar gidaje uku, a cewar rahotanni.

Bayan an kama shi, ‘yan sanda sun je gidansa, inda suka gano gawar Mis Dall’Oglio da aka voye a xakin wanki.

“Ya shigo ofishin ma’aikatar fansho yana sanye da dogon siket, ya yi ado da jan baki da jan-farce da sarqa da ‘yan kunne irin na tsofaffi,” Francesco Aporti, magajin garin Borgo Virgilio ya shaida wa Jaridar Corriere della Sera.

“Amma sai dai yana da kaurin wuya, sannan kuma fatar hannunsa ba ta yi kama da na tsohuwa ‘yar shekara 85 ba.

“Muryarsa kuma ta maza ce duk da yake ya yi shigar mata. Amma da a ce ba a lura da waxannan abubuwa ba da ya ci lalai.”

Da yake magana game da mahaifiyar wanda ake zargin, magajin garin ya ce, “Wataqila ta mutu ne saboda dalilai na rashin lafiya, amma za a tabbatar da hakan ne kawai ta hanyar binciken gawar.” Wannan labari ne mai ban mamaki kuma abin baqin ciki ne qwarai.”

‘Yan sandan Italiya sun ce, gawar mahaifiyar an naxe ta da zanin gado sannan aka saka ta a wata jakar kaya, aka sanya ta cikin firji.

Daga baya ’yan sanda sun xauki gawar zuwa wajen ajiye gawarwaki a asibitin da ke yankin don yin gwajin qwaqwaf da nufin gano musabbabin rasuwarta. Yanzu haka ana binciken mutumin a kan laifukan zamba da voye gawar da ya yi ba bisa qa’ida ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna